Showing 1 words to 3000 words out of 82431 words
*KNKB2001*
*Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 05521790550,ban da tsarin kati wannan karo a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488*
Duka na tattara yaran muka bi Jamal zuwa gidan Mama hankali tashe,Har da Hafsah muka iske gidan cike da mutane,Kawayen mama da su Anty Binta,Anty mahma da sauran makotan abokan arzuka.
Yadda naga Mama na kuka sai da ta karyamin zuciya ni kaina na shiga tashin hankali mai tsanani. na kasa dora wannan sabuwar kaddarar data bullo mana lokaci d'aya a kan mizani. abu d'aya na sani ina da yakana da yakinin na yarda da Allah sannan na aminta garesa kowani tsanani yake,kuma dukkan sauki daga garesa ne.
Sai ban bi ayarin yan kuka ba. Na koma gefe ina hailala da yi ma Allah kirari da istigifari,domin nema ma Yaya ishaq mafita da salama acikin sabon halin da ya wayi gari acikinsa.
Ganin ba wanda ya tuna da kiran mutanen karofi sai na Dauki wayata na fita daga falon Mama nayi nisa da Hayaniyar mutane,na kira Goggo na shaida mata abunda ke faruwa Allah Sarki dan'uwa rabin jiki sai Goggo ta Rud'e hankalinta ya tashi ta dinga Daukan Salati tana Direwa,mun rabu tace gatanan zuwa bari ta shaida ma su Yaya Isa halin da ake ciki.
Ni da kaina na kira Yaya Asiya na gayamata Halin da ake ciki. itama tana ta salati tana Direwa,kowa in yaji abunda ya faru sai ya tambayi garin yaya..?mu kuma bamu da masaniyar yadda abun ya faru,abu d'aya muka sani ana Tuhumarsa da Batar wasu makudaden kudad'en gwamnati, lamarin akwai d'aga Hankali aciki.
Zuwa yammah gidan Mama ya cika da jama'a yan jaje da masu zuwa kallon abunda ke faruwa suna komawa gefe suna dariya. Da yammah hatta Dangin Mama na yamai sun iso mazan su da matansu har da Hure,itama sai uban kuka take yi ba kiran sunan Allah ballatana Salati.
Goggo ta iso tare da Yaya Isa da Yaya Salisu,basu jima da zuwa ba sai ga Hajiyar Dala ita da megidanta ashe yana gari duka an taru a falon Mama ana faman maida zencen,ni dai ina gefe sanye da Hijabi bazan ce ban yi kuka ba sai dai ban yi kuka na fitar Hayyaci da su mama suka dinga yi ba. ni nafi muka duka lamurana ga ubangijina, yara ma haka suke kuka tun ballatana ganin manya nayi Amir kad'ai ne bai yi kuka ba,sai Hawaye domin shi yazo wajena yana fadin"Umma da gaske yan sanda sun kama Daada.?shikenan bazai Dawo ba..?
Sai na jawosa jikina na share masa hawaye Lokaci d'aya ina fadin"Basu kamasa ba sun dai rikesa suna masa tambayoyi,ka yi ma Daada addu'a da ikon Allah zai jibanci lamarinsa, Sannan ya warware al'umaransa ya Dawo gida lafiya"
Sai ya dagamin kai Daganan bai kara kuka ba. na riga na cusamai yakinin Da sanin Allah komai ya faru sannan garesa ne dukkan wata mafita take.
Mijin Hajiyar Dala babba ne a matakin gidan Soja yasan manyan mutane sosai sai bige bigen waya yake domin nemam makaman zencen,Ammh shuru kake ji har Dare sallah kawai ya fitar da mazan matan mu kuma muka gabatar da tamu acikin gida,
A d'akin Badariya nake yada Saukata in nazo tana kwance sai kuka take yi, su Anty Mahma na bata baki da na idar da sallah ina azkar Lokaci d'aya bakina na motsi ban jirka daga inda nake ba sai da na Daga Hannunwana na rokar ma Yaya Ishaq sauki da salama acikin kaddaransa,na Roki Allah ya kubutar da shi cikin Aminci.
Tare muka shafa addu'an da su Anty mahma ta kalleni tana fadin"Sannu Fa'iza kin fi mu karfin gwiwa,muma bari mu tashi mu yi sallar mu roki Allah sauki kan al'amarin yafi wannan koken koken da muke ta yi"
Nayi yake ban ce komai ba,kamar bazan yi mgana ba ammh kukan Badariya ya Dameni sai na karisa kusa da ita na zauna na Dagota zaune ina Share mata Hawaye ta kalleni nima na kalleni, kafin ta kara saka kuka tana fadin"Anty Fa'iza Yaya ishaq bamu san wani Hali yake ciki ba..Mama nata kuka"
Sai ta fada jikina ni kuma sai na riketa ina Lallashinta har sai da ta samu natsuwa sannan na kalleta ina Fadin"Kuka ba mafita ba ce Badariya.in mun yarda Allah ke da Kaddara sannan shike da sa'a da Aminci to mu mika masa duka Kukan mu, sai ya Dudemu ya share mana Hawaye.Tashi ki yi sallah ki rokar ma yayanki sassauci da warwarewar al'amarinsa,sai kiga da ikonsa komai ya Daidaita"
Da ga alamu mganganuna sun shigeta nan take ko ta mike ta shige Tiolet Halisa na gefe tayi tagumi sai itama ta mike tana fadin"Madallah da wannan Tunatarwa taki Anty Fa'iza.Da su mama ma za'a samu mai Tunasar da su da sun bar wannan kukan sun koma ga Allah"
Anty Mahma tace"Mai dakatar da kukan Mama abu d'aya ne sai in Ishaq din tagani a gabanta kila sai kukanta ya tsaya"
Ni dai ina jin su ban ce komai ba,Dakin na bar musu na fita falo neman su Ahmad,Saboda Halin da gidan ya yini ko abinci ba wanda ya nema ni kuma naga in mu manya ne yaran fa..?sai na shiga kitchen na Dafa musu jallop din taliya na zubo musu ina bin yaran daya bayan D'aya ina ba su suci abinci,ashe Anty Binta na takaice dani,D'an wajen Anty mahma ke kusa da ita na nufesa da karamin Filet din na zubamai ina fadin''Anwar taho kaci abinci..".
Ba zato kawai naji an yi sama da Filet din ya koma ya kife a kasa sai hankalin kowa ya koma kanmu Anty Binta na gani tsaye a kaina Tana faman Huci Idanuwanta sun kala sun yi jajir ta nuna ni da yatsa tana fadin"Acikin wannan halin da muke ciki ke har ta abinci kike..?ina lura dake tun dazu abunda ya faru bai Dameki ba, kamar ma murna kike da Faruwar haka me ake da auran mace irin ki Fa'iza macen kaddara macen da bata san mijinta ba"
Sai na kame a tsaye na kasa mgana sai dai na Sadda kaina kasa Mama ta Dakata da kukanta tana kallona, sai kuma aka rasa me mganar mazan duk suna waje ana ta buge bugen waya domin samun mafita.
Anwar ne yabi taliyar kasa yana ci,Alamun yana jin yunwa wata kawar Mama tace"yara fa najin yunwa, tayi Dubara da ta dafa musu in mu mun hakura saboda tashin hankali,su yara ne basu san komai ba"
Goggo tace"To shi yaro ma me ya sani.?shi dai yaci ya koshi"
Ganin ba'a bata gaskiya ba sai ta fara Borin kunya tana fadin"ku fa ganta wlh ko Damuwa ma batayi ba.kamar cewa ma take gwara da akayi hakan"
Goggo ce ta shigar min cikin bacin rai tace"Assha.Haba Binta ta ya ya mijin ta uban ya'yanta na cikin wannan Halin kice bata damu ba..?ai ba kowacce damuwace ke nuna kanta ba, in mu muna nuna Damuwar da kuka ita sai ta fimu hankali ta nuna Damuwarta wajen Ubangijin komai da komai, kinga kenan tafi mu Dubara mai kyau"
Sai aka fara fadin haka ne kuwa a wajen,ba'a bata gaskiya ba. ganin bata samu nasaran tozartani ba sai ta kalleni a wulakance ta juya ta tafi ni kuma sai na Dauki Anwar na tafi da shi domin na zuba mai wani abincin na basa yaci kada a Dauki alhakin karamin yaro da yunwa.
Har dare ba wata mgana mai Dadi,Domin har alokacin mahaifin zainab yace basu bari an ga Yaya Ishaq ba, duk mazan nan suka kwana da Safe kuma suka hadu suka Dauki Hanyar Abuja har da mijin Hajiyar Dala da shi a Hotel ya kwana da Safe da shi da Tawagansa suka Dauki Hanyar Abuja.
Nan kuma Yaya isa da su Jamal da Kawun Mama dake yamai da suka iso jiya,suka tafi tun a hanya ake ta kiransu sukace basu isa ba,bayan kuma sun isa sai suka daina Daukan wayoyin mutane hankula suka kara tashi Sai Dare sannan Hajiyar Dala tayi waya da megidanta yace shi ya wuce kano ma ammh yana ta kokarinsa abu ne da ya had'a da Gwammati, sunce zasu Tuhumesa ne kuma har Lokacin basu bari an gansa ba.
Wannan labarin ya kara Tada Hankula cikin kwana Biyu ba'ayi barci cikin salama ba,Yaya Asiya tazo jaje ita da ya'yan Goggo na Karofi har da Yaya mariya nima makotana duk sun zo,yimin jaje abun duniya baya boyuwa Tuni mgana ta bazu a gari,Mutane na maau saran Zobo da kunin aya a wajena suna ta kirana bani da sukuni ga masu son Turaren kamshi har da masu biki na abinci, bani da sukuni hakuri nayi ta bama Mutane ina gaya musu halin da nake ciki na Mijina na Hannun masu Binciken Gwamnati a abuja.
Goggo tunda tazo bata koma ba tana tare da Mama tana bata baki Hajiyar Dala data kwana biyu sai ta koma cikin kwana Biyar mama ta fita Hayyacinta su Anty Binta sun gaji da kukan sun hakura, Tuni wadanda sukaje Abuja sun dawo labarin bai Sauya ba, sai dai sun tabbatar da cewa Mahaifin zainab na iya bakin kokarinsa haka ma Mijin Hajiyar Dala ana ta shiga da fita.
Ganin sai zama haka kawai muke yi,Sai nayi tunanin gwara na tattara yara mu koma gida mu cigaba da gayama Allah,tunda ko mun zauna anan gidan abunda Allah ya tsara shi zai faru kuma bamu isa mu sauya masa kaddara ba, sai dai in muna addu'a sai kaddarar tazo masa saukakkiya.
Kwanan mu shida da Safe na samu Mama a dakinta ita da yan'uwanta na yamai bayan na duka na gaisheta ta amsa muryanta a shake kaina na kasa nace mata zan kwashe yara zamu koma gida, sai kawai tayi shuru batayi mgana ba,Hure na gefe sai ta tabe baki kafin tace"Ai ba sai kin gayamata ba ki yi gaban kanki kawai.Ai Anty ita ke da rashi saboda ita ke da D'a"
Baki da asara ko da an rasa Ishaq"
Sai mganganu ya fara tashi a tsakaninsu Mama ce ta katse da fadin"ku kyaleta ta tafi.."
Muryanta a shake ni kuma ganin haka sai na sanyaya murya ina fadin"Mama naga zaman bai da amfani ne ga d'awainiya gwara mu koma gida sannan ga makarantarsu duk ya tsaya zamu cigaba da gayama Allah a duk inda muke da ikonsa komai zai warware"
Wani kallo Mama tayi min kafin tayi tari ana mata sannu sai ta kara kallo kafin tace"Na dad'e da sanin baki da asara a komai Fa'iza, ki yi tafiyarki Domin zamanki bai da amfani ammh ki bar masa ya'yansa anan su d'in Dolensa ne saboda Mahaifin su ne, in suka rasa sa bazasu taba samun madadinsa ba"
Daga haka sai ta koma ta juyar da kanta tana share hawaye, jin abunda ta fada yasa na tashi na fita ni ba haka ne nufi ba ganin ta min gurguwan fahimta sai na fasa gudurina.
Goggo na sama na gayama yadda muka yi da Mama sai ta Dafa kafadata kafin tace"Da kin nemi shawara ta da baki yi mata mgana ba,me neman kuka ne fa aka jefe shi da kashin awaki.Ki rabu da ita ki zauna din har muga abunda Allah zai yi"
Tun da Goggo ta fad'amin haka sai na bar mganar Tafiyar ashe na gudu ban tsira ba mgana ta ding yawo tsakanin Dangin Mama da kawayenta Anty Binta Kirkiri a gabana tace Daman ban damu ba so nake nakoma gida na cigaba da sana'ata tunda shine a gabana,naji haushin wannan mganarta kuma ban kyaleta ba sai da na kalleta ido cikin ido sannan nace"Ko ban damu saboda yana mijina kuma uban ya'yana ba.Zan nuna alhini na saboda yana matsayin Yayana wanda iyayenmu suke abu d'aya ballatana shi din Uban ya'ya na ne"
Daga haka na huce na barta,sai ta fashe da kukan nayi mata rashin kunya mgana taki ci taki cinyewa Goggo ta kashe mganar da Fadin"Haba Binta mu bar wannan ceceku cen tunda ba shi ba ne a gabanmu.Mu ji da abunda ke gabanmu don Allah"
Ammh Anty Binta batayi shuru ba sai da tace"Ai gani tayi tana kama kud'i sai ta dauka daidai muke da ita.Abunda bata sani ba komai lalacewar Daji bai kai in giwa ta mutu kiyasha ya jata ba, ko tana mace tana da Madaukakiyar Darajarta"
Dakyar mgana ta mutu sai da Wata kanwar uwa take ga Mama ta tsawarta ma Anty Binta sannan mganar ta Dakata ammh tana ta kananun mganganu a kaina niko bansan tanayi ba ina Dakin Badariya.
Washegari ya kama Sati daya kenan da labarin da iso mu,an yi an yi an shiga an fita duka labarin bai sauya ba,Hankula ko sun fara kwanciya sai su kara tashi jin ba wani labari mai Dadi.
Sai a ranar muka yi waya da Zainab da yake muna da lambar juna sai dai mukam jima bamu yi mgana ba. sai in wani abu ya taso ko rashin lafiya,Ita ta kirani ni na shafa da ita ballatana ma na kirata, mun gaisa cikin Alhini muka yi ma juna jaje,Sai dai ban wani ji ta cikin wani yanayi ba,Ita take fad'amin mganar Yaya Ishaq sai manyan Gwamnati sun shiga tunda Fitar da kudi ne na ma'aikata kuma ta Office dinsa da saka Hannun sa komai ya fita ba yadda za'ayi ya fita,Tace Babanta ya samu ganinsa sau daya ammh har yanzu ba wani mganar su bada Belinsa,Mun dade muna mgana da ita nace mata ina gidan Mama tayi ta mamakin tace ita da yara sun koma gida sai dai bata bar zuwa wajen aiki ba,Saboda sun ki bata Hutu a raina nace Mama taji kuwa..?sai ga shi tana fadamin Ko da yaushe suna Mgana da su Mama,kuma susan tana zuwa wajen aikinta nan take na Fahimci abun,inda ake raina an fi kai Hari chan bangaran.
Ranar da yammah sai ga Hajiyar su Raliya tazo,ni ina chan Dakin Badariya ban sani ba,Mama na ganinta da su Anty Binta suna ta Rawan jiki mama ta santa tunda kawancen Raliya da Badariya ba yau ba ne,Sai dai ita Hajiyar su Raliya ce bata zurfafa zumunci da Mama ba, sai kuma gashi ni jinina ya had'u da nata da zuru'arta.
Bayan gaisuwa da jajanta abunda ya faru sai Hajiyar su Raliya ta nemi ganina Mama ta tabe baki kafin tace"Kila ma bata gidan domin tun jiya take son ta koma gida dayake bata damu ba"
Hajiya batace komai ba,Da Badariya tazo gaisheta sai tace ta kira mata ni,Ina Dakinta tazo ta kirani ina jin tace Hajiyar su Raliya na mike na fita da Hijabi suna falo na duka na gaisheta cikin Fara'a ta amsa ni tana fadin"Haka ake yi Fa'iza abu ya faru haka bazaki kirani ki fadamin ba..?
Sai dai naji a bakin Raly.?
Kaina na kasa ban ce komai ba sai ta Cigaba da fadin"ba'a haka Fa'iza irin wannan sai ki kirani ki fadamin ko ba a Uwar kika Daukeni ba..?Goggon karofi ta karbe d'iyarta kenan.?
Goggo na gefe tayi dariya kafin tace"Ba ruwana Hajiya ke da Diyar ki"
Kaina na kasa na shiga bata Hakuri sai tace bakomai su Mama haushi duk ya cikasu kallona tayi tana fadin"Ya abun ya faru ne ina so na sani saboda naji in zan iya taimaka wa"
Kafin nayi mgana Anty Binta ta karb'e da bayanin yadda ake ciki Hajiyar su Raliya,ta gyada kai kafin tace"Akwai Kanina yana aiki da Hukumar EFCC din achan Abuja, bari na nemesa naji ko zai iya taimaka mana"
Nan da nan bakin Mama ya washe a gaban mu ta kirasa suka gaisa ta rattamai bayanin komai sai ya nemi sunansa da inda yake aiki Anty Binta ta fadamata sai ta turamai yace ta bashi nan da zuwa Dare zai bincika mata halin da ake ciki.
Bata wani jima ba, tayi ma su Mama sallama,akan yadda akace in sha Allahu gobe zata dawo ita da sauran yaranta Mama godiya kamar zata kwanta mata Hajiya ta kalleta kafin tace"Bakomai kada ki damu babba ne a wajen zai binciko komai..Zan iya yin komai saboda Fa'iza kamar diya take a wajena Ahalina Ahalinta ne,zan iya bakin kokarina bazai gagara ba insha Allahu"
Basa kaunar su ji an ambaceni kuma basa kaunar alfarma ta barayina har waje na rakata ni da Badariya,Direba ya zo da ita ta shiga mota tana ce min sai zuwa gobe,Ta tambayeni su Amir nace suna cikin gida,na dawo cikin gida naji ana ta maimaita zencen nidai a raina ina fatan Allah ya kawo mafita.
Washegari da wajen yammah sai ga Hajiya ta dawo ita da Raliya da yayyin Raliyan suna zuwa ni suka nema daman suna zuwa gidana,Ita kuma Hajiya ta nemi su mama ta gayamusu halin da ake ciki,Hukumar ta na bincike ne,sannan akwai yuyuwar komai da ya fita da saka hannun Yaya Ishaq saboda haka in sun gama Bincikensu zasu yi mgana, sannan sun hana Belinsa saboda cases din na da girma Hankula sun kara tashi tace dai a Dage da addu'a komai zai daidaita.
Wasa wasa har an shud'e Sati Biyu shuru dai mgana d'aya sai sun gama Bincike,Gajiya nayi da zama na Tattara na koma gida na da yara Goggo ma ta koma Karofi mama an barta da Anty Hure ne mutum yamai suma sun koma kowa ya Saduda yasan Allah ke yi,Mama ta saka ana ta Sadaka da Saukan Qur'ani ni kuma agida banzauna ba ni da yara muna ta kai ma Allah kukan mu,Ban kara bi ta kan Zobo da kunin aya ba,Saboda Halin da nake ciki ko makaranta yaran basu koma ba Hafsa ce ta koma makarantar ta tana zuwa.
Wajen wata da'ya da Tsare Yaya Ishaq aka bama yan'uwansa Daman ganinsa Su Yaya Isa dai suka koma Abuja mgana ta tabbata ba yadda Yaya Ishaq zai fidda kansa saka hannunsa da yardansa aka fidda kudad'en,zai biya taran kudaden gabad'aya da tsabar kudi ko Kaddara.
Lokacin da labarin yazo mana Sai murnan kowa ta koma ciki kudi ba kadan ba wajen Million 70,ina Yaya ishaq yaga wannan kudin ko Kaddara..?su Yaya isa sun dawo suna mganar ya lissafa abunda ya mallaka, gida biyu nan katsina d'aya sai na Abuja sai mota sai gidan mahafinsa,Sai tsabar kudi miliyan d'aya da rabi asusun bankinsa sai fili a nan katsina,Hukumar tace zata zo ta Duba duka kaddarorin zata kwace zai zama karkashinta.
Sai naji na rude ina ta maimaita innalillahi acikin raina Hankali tashe na kalli Yaya isa ina fadin"Aikin sa fa Yaya