Showing 63001 words to 66000 words out of 82431 words
Nafila bayan na idar na Daga Hannuna ina addu'ar Allah ya bani juriya da kwarin gwiwa sannan kada yasa ya'yana su zama raunin da zai sa su shiga Tsakanina da Burina.
Washegari Fuskata a Had'e na tashi shi kanshi ya ganni ko gaishe shi ban yi ba shine yace"Ina kwana Anty Fa'iza"
Kallonsa nayi na basar na cigaba da aikin gabana sai ya kwashe da Dariya yana fadin"Wai fushi kika yi..?zaki yi ma mai Dalili yarinya"
Ina jinsa nayi masa banza Da rana Zainab nata kirana sai na rasa ya zan yi da ita.?Sai kawai na dauki wayar na tafi Dakin Mama yana ko kwance kan kujera Mama na zaune a kasa suna Hira yanayin yadda na shigo yasa Mama ta kalleni tana fadin"Fa'iza lafiya..?
Shima sai ya sakamin ido yana nazarina Gabanta na duka na ijiyemata wayar ina fadin"Mama ki masa mgana kila ke yaji mganarki"
Matarsa ke damuna da kira shi kuma in na kai masa sai yak'i mgana da ita. Har ga Allah mama bana so Zainab taga laifina,sai taga kamar ina mata Tsakani da mijinta ne"
Mama sai ta kallesa tana fadin"Shi ina wayarsa ne..?
Kai tsaye nace"Bai gyara ba kuma yaki siyan wata. saboda yasa matarsa ta rika jin Haushi na"
Sai Mama ta Rausayar dakai kafin tace"ka kyauta. Tashi kije Fa'iza zan yi mai mgana"
Na ko mike na ficewata ban ko kallesa ba,inaga Mama tayi mai fad'a yasa ya dauki wayar suka yi mgana,washegari kuma da Safe wajen sha daya sai gata Direba ya kawosu ita da yara,Na karbeta hannu biyu kamar yadda na saba kai Tsaye wannan karon Dakin mijinta ta sauka yana dakin tana zuwa ya shuru Takalminsa ya fice ya'yansa kawai ya Kula ga cikinta har ya fitio ta kara kiba kamar ba ita ba.
Bayan na gama abincin rana munci muka zauna zaman Hira a manganunta na fahimci ita kaddaranta Soyayyan Yaya Ishaq ne shine Rauninta Kuma mahaifinta na kaunarta bazai so abunda zai sosa mata rai ba.
Kai Tsaye ta kalleni tana fadin"Maman Amir Honey yaki ya yafemin laifin da ban ma aikata ba. Daddy mu kad'ai ya Haifa Dagani sai zuzu komai muke so a duniyan nan yana bamu shi baya so yaga muna wahala ganin yadda kwanakin chan nayi ta fama da Laulayi ne yasa yace a cire ciki ammh da nuna bana so ai bai kara mganar ba. meyasa shi Honey bazai sauko ba Har Daddy fa ya so yaje chan su yi mgana yaki ya Saurareni,yanzu haka Daddy na chan ya kafa kwamitin Bincike a ma'aikatarsu kan Case dinsa ammh duk bai gani ba yanzu nazo ko kulani bai yi ba"
Sai Hawaye sharr sai ta bani Tausayi,Ashe an fara binciken ni bama mu yi mganar da Abba ba. Tunda yace min bai samu sun yi mgana da Engr din ba har yanzu saboda baya kasar bai dawo ba,Ina kallonta tana kuka,sai a raina nace ita kuma nata kaddaran kenan..?tana son shi Kuma Dole Mahaifinta ya barta ta biyo abunta take so in har shima yana son abunda yarsa ke so.
Lallashinta na dinga yi ina bata baki ta kara kallona tana fadin"Wlh maman Amir ina cikin wani Hali Cikin nan sani Son kasance da shi yake yi. ammh yaki Saurarena a kwanakin baya kamar zan yi hauka haka nakeji,saboda yanayin jikina yasa sai da na samu sauki na taho"
Na Tausaya mata saboda haka nayi fama da wannan sha'awan Lokacin cikin Ahmad ammh ban samu ba,Domin Yaya ishaq bai saurareni ba akwai ranar da har kuka nayi masa yace shi baya cikin mood din ya gajiye ya Dawo bazai iya min wani amfani ba, ranar kamar zan yi hauka naji kamar na Mutu da addu'a da Taimakon Allah sai da cikin yayi kwari komai ya lafa tsakani ga Allah na Tausaya mata matuka shiyasa na Rike mata Hannu ina fadin"kada ki damu zai sauko in sha Allahu"
Tana sharan kwallah tace"Yaushe zai sauko..?ko fa kallona bai yi ba..?
Don Allah ki yi masa mgana ki tayani basa Hakuri"Sai na kasa mgana kawai ina kallonta ina zan kara mgana nima ta kwabemin Saboda na lura da yadda nake masa mganarta alokacin yake kokarin nuna min nima ai matarsa ce.
Ni dai ina ta bata baki ina fad'amata zai sauko cikin hakane yasa nace"To kiyi masa abunda yake so ki bar aikin nan Maman Fadil sai ya sama miki anan ki dai dawo kusa da shi hakan zai fi"Sai tayi shuru kafin tace"Daddy ne ya hana fa. Ammh wlh naso haka tun da na Fahimci bazan iya zama nesa da shi ba"
Ni ko sai naga na samu damar da zan gayamata gaskiya sai na gyara zama ina fadin"Mahaifa suna da iko a kanmu ne idan muna gabansu. ammh da zarar sun aurar damu mun bar karkashin ikon su mun koma karkashin ikon Mazajen mu,Ki gane wani abu shifa miji ba abun wasa ba ne yana da cikakken iko akan ki Zainab. Yafi mahaifinki iko akan ki, in yace kada kiyi abu kika yi Allah zai yi Fushi dake in ransa ya baci,ko da mahaifinki kika sabamawa dalilin Umarnin mijinki Allah bazai kamaki da laifi ba,a ko'ina Umarninsa na saman na kowa in dai a kanki ne"
Sai tayi shuru tana kallona alamin bata san haka ba ni ko sai na cigaba da Fadin"Annabi muhammad Salallahu alaihi wasallam ya fad'amana in da Allah zai wajabta Sujudda Tsakanin mutane da ya wajabta Sujuda ga mata zuwa ga mijinta.Saboda a nuna Daraja da girman miji ga matarsa"Sai ta waro ido tana fadin"Yanzu duk ina cikin Fushin Allah ne Maman Amir..?
Sai na girgiza mata kai ina fadin"Cikin Rashin sani ne. Shi kuma Allah bai kama mutum da laifin da bai sani ba,Ni dai shawaran da zan baki ki yi kokari ki gyara zamantakewar dake Tsakanin ku,Sannan ki daina Fifita mganar Mahaifinki saman tasa baki kyauta ba ki bashi hakuri ki nuna masa zaki bi Umarninsa sannan zaki Girmama duka muradansa akanki sai a zauna Lafiya"Sai ta damke hannuwana Tana fadin"Nagode sosai Maman Amir.Ban taba ganin kishiya mai kyakyawan zuciya kamarki ba"
Sai kawai nayi mata mirmishi sai gashi na zake ina gayamata yadda zatayi ya sauko,ni nace ta sake wanka ta d'au gayu yau a sha soyayya. Sai Dariyan jin dadi take yi,Mama na Dakinta tana jin mu bata ko leko ba naga yanzu ta daina ma Zainab din Rawan jiki,yara suna dawowa makaranta suka fara Murnan ga Anty ga su Farhan,ko Dakin nasa ma ni na shiga na gyara shi Saboda bata iya ba. Da Daddare tuwon shinkafa nayi mana miyar ganye,da gyad'a sai Dare ya Dawo ina ta mamakin shi ko ina yaje haka?
Ruwan wanka ma da yace na sakamai yana zafi na juye na bama Zainab nace ta bisa Dakin dashi ta karba ta wuce to bansan ya suka kare ba,Saboda afalo muka hadu muka ci abinci gabad'aya. ina kallo sai kallonsa take yi shi kuma yana basarwa kamar an matsi bakina nace"Wai ina kaje yau tun Safe ne.?
Kamar yana Jirana kawai sai ya harareni kafin yace"masallaci naje na zauna ina kai kararki wajen Allah. Ki nemi yafiya ta.
wlh in ban yafe miki ba, bazaki yi albarka ba Fa'iza"
Sai na saki baki ina kallonsa kuma agaban yara ga Hafsah. zaraf Anum tace"Umma me kika yi ma Daada..?
Kafin nayi mgana yace"Tambayeta dai Anum.."
Zainab na gefe tace"Kema fushi yake yi dake Maman Amir..?
Kawai sai ya kai mata Harara yana Fadin"Ina ruwanki..?
Sai ta kalleni nima na kalleta nayi mata signa da ido sai ta mike nima na mike ina fadin"Amir ka kwashe kwanukan nan ka kai kitchen.
Anum ki share falo Hafsah ki yi ma yaran shirin kwanciya Fadil dina taho muje mu kwanta"Yaro ko ya taso daga wajen Uban ya nufoni na Daukesa na kalli Zainab ina fadin"Ki shiga ki gyara masa shimfid'a. Sai da Safe"
Sai ta amsamin da Toh,ta wuce nima na wuce da kallon mamaki ya bimu da shi kuma muka ki basa damar mun Fahimcesa yaran kuma suka rika fad'in"Umma sai da Safe,Anty Sai da Safe"
ni dai tunda na shige Daki kamar Allah ya aikomin da barci ina Kwantar da Fadil nima nabi gefensa na kwanta sai barci sai asuba na tashi,Da Safe basu ma fito da wuri ba. Sai chan rana tunda naga ta fito tana Annushuwa na kalleta ina fadin"Ya ya.?
Sai ta bani Hannu muka tafa Lokaci daya tana fadin"Komai ya daidaita.
Ammh fa yace sai na ijiye aikina na Dawo nan sannan zai san ina son sa"
Kai Tsaye nace"Sai ki nema wani anan ba Shikenan ba"
Kai ta gyada min kafin tace"Haka za'ayi. Nasan zamu sha rigima da Daddy ne"
Ina shirin mgana kawai daga bayanmu mukaji muryansa yana Fadin"Fa'iza wlh kiji Tsoron Allah. Ki kuma Tubar masa saboda abunda kike yi sam bai dace ba."
Kafin nayi mgana tayi zaraf tace"Honey laifin me Maman Amir tayi ita kuma..?
Sai ya harareni yana fadin"Tambayeta ita ai tasan komai"
Sai ta juya tana kallona kafin tayi mgana na tare ta da fadin"Kada ki biye masa bansan abunda yake mgana ba"Saboda kada ya kara mgana na yi wuf na fice ina sauke Numfashi,shikenan ma'auratan suka Daidaita kansu,Sati daya tayi mana sannan ta koma ta kuma ta tabbatar min zata yi kokarin ta ijiye aiki sannan ta Lallabi Daddy ko gida ya siya mata a nan ni ko araina nasan Yaya Ishaq bazai yarda ba. kuma Tsakani ga Allah wannan gidan yayi mana kad'an ace mata Biyu da yara ga Mama shima ai sai ya Duba ammh yadda bai sakoni aciki ba nima ban Tusa kaina ba..
Maganar auran Halisa ya taso Anty Binta ana ta shirye shirye ni dai nace zan gyara amarya ta bangaran jiki da kamshi,kuma Anty binta na fad'amawa sai gashi tana min godiya sannan tamin mganar zatayi Zobo da kunin aya ranar walima tana so nayi mata,girki ma in ba damuwa na shige gaba ban nuna mata komai nace duk zan yi,mun yi waya da Badariya tace bazata dawo ba,ni na bata baki tace zata dawo ana gobe Daurin aure tunda kano za'a kawo amarya sai ta biyo su ta dawo abunta nace shikenan kuwa.
Da kudina na siyo kayan hadin Turaruka na had'ama Halisa da na Rushi da Humra da kwallacha sun kai na Dubu ashirin,sannan ga na gyaran jiki tun ana saura sati daya biki take zuwa kullum da yammah ina mata Gyaran jikin.
Ranar da muka kwana uku muna yi sai dare na gama mata,ita da wata kawarta suka zo,kuma tare suka tafi a dakin Mama nake yi mata ita tunda ta gidace,Mama sai mamaki take yi tana fadin"Ikon Allah.."
Ranar na gaji,ko zobon yammah ban Dafa ba Hafsah na makaranta,bata dawo da wuri ba,Ban iya ko yin abincin Dare ba saboda bayana ya rike sai nayi wanka na gasa jikina da Ruwan zafi nayi sallar mangariba ina zaune ina lazumi Hafsah ta shigo ina ta mata fadan ina ta Tsaya sai tace min bata samu abun hawa ba ne da wuri, sai na Sassauta nace in ta huta ta Dafamana ko Cousscouss ne.
Tace to bari tayi sallah Yaran kuma suna Falo Yaya Amir na biya musu karatu ina jin tashin muryoyin su daga Falo,Chan sai ga Hafsah da wayarta ta kawo min Abba ke son mgana dani bayan na dauka mun gaisa yacee"Kuna lafiya ina matata da megidan naki..?
Nace"Duk suna lafiya Abba"
Sai yace"To madallah kan mganar Binciken da nace za'ayi kan Case din mijinki ne,Engr ya dawo nayi mgana da shi yace ba matsala sai dai zamu kara jira Tunda mahaifin nasa yana London Mahaifiyarsa ke chan za'ayi mata Dashen koda. hankalinsu duk ba'a kwance yake ba shiyasa har yanzu bai yi masa mgana ba"
Sai nace"Ayya Allah ya bata lafiya Abba"Sai ya amsamin mud'an taba Hira har ya bama Ammi muka gaisa tana min Tsiya"Hajiya Fa'i mai turaran kamshi"
Dariya nayi ina fad'in"Kai Ammi"
sai kawai tace"Abban ki ma yace y'ata ta iya had'a Turaren kamshi"
Kunya suka bani su ko ba ruwan su Abba da Ammi sai su,mun gama wayar kenan naga mutum tsaye a kaina ina dagowa cikin mamaki nace"Sannu da zuwa"
Sai kawai yace"ina son mgana dake. ki sameni a dakina"
Daga haka ya fice mamaki ya kamani na rike haba a fili nace"Topha..!
Ina shirin tashi aka fara kiran sallar Isha'i sai na mike nayi salla na idar kenan na mike ina ninke Darduma Anum ta leko tana fadin"Umma Daada na kira"
Sai na gyada mata kai ban ko cire Hijabin jikina na fita zuwa Dakinsa ina Shiga sai faman safa da marwa yake yi har sai da nace"Lafiya..?
Kai tsaye yace"Ina jin yunwa ina abincina.."
Kai Tsaye nace"Aiki nayi nagaji sai da Hafsah ta shgo nace ta dafa mana ko Taliya"
Sai kawai naga ya karisa ya rufo kofa da Sauri nace"Ya da rufe kofa..?
Yana juyowa yace"Yau zamu yi ta kare Fa'iza hakki na zaki bani nagaji"
Gabana ya fadi na kwalolo ido waje hakkina..? Na maimaita a raina.
na shige su ga shi in nayi wani ihu yara na falo suna jin mu.
bakina yayi nauyi ina ji ya ja har hannuna bakin katifarsa ya cire min Hijabin jikina cikin rawan murya nace"Abincin fa..?
Kai Tsaye yace"Zamu ci in mun gama. Fa'iza bazan iya jira ba"
Bakina naji yayi wani Dif. Jikina kuma Kamar mara Lakka, kamar rakuma da akala haka yafara bi da ni a gaggauce kamar daman ni yake jira.
*Janafty*
*KNKB2017*
*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*
Saboda yanayin da zuciyata take ciki yasa kwata kwata gangan jikina bai karb'i sakonnin dayake aika min da shi cikin zafin nama ba,Doguwar riga ce a jikina har ya samu nasaran Rabani da ita,ammh na kasa wani motsi na riga na Sadakar bani da wani Tsumi ballatana Dubara a lokacin.
Bakina ne yayi min wani irin nauyi, ina ji kamar ya kumbura saboda irin yadda Yaya Ishaq ya rika sumbatata a raina sai cewa nake yi daman haka Sumbarta take..?
Sharaf nayi masa ko hannuna ban yarda na motsa ba,kwance nayi masa kamar ruwa ya cinye ni,Ina jinsa yana gwama Numfashi,sama sama sannan Lokaci d'aya yana sauke ajiyar rai chan naji yana kiran sunana fad'i yake yi"Fa'iza ki rikeni. Ki rumgume ni don Allah"Ya fad'a cikin wani irin yanayin da ba kowa zai iya sanin yanayin ba.
Nayi masa banza kamar ban ji ba, kuka ne ya taho min daga karkashin Zuciyata sai hawaye sharr sannan na saki Shesshekan har yana jina.
Sai naji kamar an zare masa lakkar jiki ya koma ya kwanta a gefe yana maida numfashi. ni kuma ina ta kukana sai ya mike zaune cikin yanayin Sarkewar murya yace"Yanzu Saboda zan karbi Hakkina ne yasa kike wannan kukan Fa'iza.?
Shuru nayi masa ban yi mgana ba sai dai ina cigaba da kukana kamar karamar yarinya sai kawai ya mike Kaina na juya gefe har ya gama Suturtata jikinsa,ina daga kwance kawai naji ya yi wuf ya tadani zaune yana fadin"Tashi ki saka kayan ki"
Sai na bisa da kallo ina Tunanin ko ya fara samun matsala ne ganin yana komai a gaggauce.
Mikar dani Tsaye ya yi ya na kokarin sakamin rigar na rike hannunsa muryata a shake nace"Bari zan saka da kaina"Kamar wacce zan gudu ina gama sakawa ya jawo hijabi ya zuramin Saboda Sauri kamar zai ciremin kai, nayi baya ina kallonsa da Tarin mamakinsa Maikon hawaye sun cikamin ido ban samu damar mgana ba. kawai ya finciki hannuna ya isa ga kofa ya Bude yana jana muka fito Falo yaran duk suna falon suna ganinmu suka bimu da ido ganin yana kokarin Fita daga Dakin yasa na Turje ina fadin"ina zaka kai ni..?.
Bai ko Saurareni ba ya fincikeni zuwa waje sai kawai naga mun shiga Dakin Mama Lokaci d'aya yana fadin"Mama kin kwanta ne..?
Mama na zaune saman kujera da waya a hannunta kamar ta ma gama wayar ne muka fad'o dakin yadda ta ganmu ne yasa ta mike a firgice tana Fadin"Kai lafiyan ku kuwa..?
Gabanta ya zaunar dani yana Fadin"Mama gata nan ta fad'a miki meyasa take hanani Hakkina..?
Ki tambayeta meyasa take guduna bata kaunar na rabeta. Mama Fa'iza na gudu na a Shimfid'a"
Shi yake mganar nan ammh ni kunya da bakinciki sun rufemin ji na da ganina na wani Lokaci,Tsabar yadda na kad'u na girgiza da wannan wulakancin na Ishaq .ashe shi yana da bakin mgana ban sani ba..?ni shekarun da ya kwashe a jingine da aurene wajen wa na taba kai karansa.?sai shi ne yake da bakin mgana."
Kaina na dunkule a kasa ina kuka kamar na mutu haka nake ji Saboda kunya ita kanta da Mama sai da ta kasa zama kunya duk ya Rufeta ta kasa mgana tana mamakin d'an yau.
Kallonta yayi a rikice yana fadin"Baki ce komai ba Mama..?
Sai Mama ta juya baya tana fadin"Fa'iza ki yi hakuri don Allah.Kada ki kara gudun mijinki a shimfid'a. kai kuma ka bita a hankali kada ka matsa mata."
Wannan mganar ku ce Tsakaninku ne, don Allah kada ku kara sakani"
Daga haka ta shige uwar Dakin ta tabar mu nan zaune,shi yana Tsaye ne kamar wani Saraki.
Kafafuwana sun yi min zafin da na kasa tashi sai da na ganshi Durkushe a gabana yana fadin"Kin ji dai abunda Mama tace ko..?kada ki karamin Gaddama in dai na kira ki a Shimfid'ata"
Sai kawai na Dago Rinannun Idanuwana na sauke a kansa cikin wata irin murya mai cike da Takaici nace"Meyasa ka kawo k'ara na wajen Mama..?
Sai hawaye ganin kukana sai kuma ya Rud'eni ya fara kokarin son rikoni yana fadin"To ke ne Fa'iza duk yadda zan yi dake kin ki ganewa shiyasa na kawo kararki wajen Mama"
Ture hannunsa nayi dake kokarin rikeni na mike Dakyar ina fadin"n ban taba kawo kararka ba.
Ban taba fad'ama kowa halin da nake ciki ba,ko da yan'uwana ne. sai kai ne da bakin ka yafi nawa Tsini..?.
Na karishe fad'a a Fusace cikin kuka Sai shima ya mike yana kallon Dakin da Mama ta shige Lokaci daya yana Fadin"haba mana.."
Kuma wai yana kokarin rikoni Saboda bai da kunya a fusace na make Hannunsa ina fadin"Tunda kaso a fasa komai za'a fasa kowa yaji"
Ganin ina nufar dakin da Mama ta shige yasa ya rikoni da karfi yana Fadin"Don Allah a'a Fa'iza don Allah"
Daman ba fad'a zan yi ba sai na Turesa na kama Hanya na fita Daga Dakin mama,zan shiga Dakina ya Taremin Hanya yana faman marairaicemin sai kawai na juya da gudu nayi hanyar waje saboda naji hayaniyar yara har lokacin suna falo kamar abinci suke ci bana so su Fahimci abunda