Showing 39001 words to 42000 words out of 82431 words

Chapter 14 - Kana Naka Book 2 Hausa Novel Complete

Janafty   

07 Dec 2024

198

ina fuskartarsa Saboda yadda yaji ina zufa ne,ga haki Lokaci da'ya Fuskata ya tallabo da Hannayensa duka Biyu Lokaci d'aya yana fadin"Fa'iza..Fa'iza ni ne fa"
Sai da naji muryansa naji Numfashina na daidaita,Abun ka ga mai hawan jini abu kadan ke haye mana sai na sauke ajiyar zuciya ina kallonsa cikin mamaki shima kallona yake yi na bude baki nayi masa mgana cikin mamakin ganinsa kawai Dif!
Kamar an kawo wutar lantarki an Dauke haka naji Jikina ya amsa ya koma kuma ya saki Lokaci da'ya, sakamakon bakin Yaya ishaq da na tsinta dumu dumu acikin nawa bakin yanayin da ban san yadda zan kwantata muku ba.ni dai da Hankalina Yaya Ishaq bai taba sumbatata baki da baki ba,ban ki in muna cikin auratayya yana bukatar natsuwa yana yi shima ba cikin soyayya ba ko natsuwa ba. cikin Tilastawa da neman biyan bukatar sa.
Shiyasa sai na rude na gigice na fita daga Hayyacina ban kara Dimaucewa ba sai da naji Hannayensa na kara kaina ajikina da zafi zafi duk inda Hannunsa yakai a jikina sai ya taba,tsayuwa ce ta nemi gagaranmu sai kawai ya bini muka zube bisa Katifar da na gama gyara masa ya kasance ina kasansa shi kuma yana sama na,bazan iya fassara yanayin ba abu d'aya na sani yayi nasara motsa sha'awata da nayi shekaru da Binneta yayi nasaran yayyafa mata ruwa data Farfad'o batare da sanina ba,Doguwar rigar yadi ne ya jikina daga sama ya zage zif din yayi kasa da ita,ba san da wani lokaci hakan ya faru ba na dai san naji hannayensa suna kai da kawo saman kirjina sannan hancinsa na shinshino duka fatar jikina tare da Game numfashinsa da karamin Nishin dake fita da kofofin Hancina.
Na fita daga duniyar da muke ciko ko nace ya taimaka wajen fitar dani daga Hayycina har yayi nasaran raba ni da Rigar jikina hannayensa dumu dumu acikin maraata,Fatar jikinsa tana gogar fatar jikina numfashi na ya sarke sai wani Uhmm...!
Kawai nake saki,wani irin tafiya ya dinga yi dani tafiyar da tunda nake bantaba sanin ana iya kai macen wannan bangaran ba,Ban kawo ma kaina abunda yake shirin faruwa dani ba sai da naji bakon al'amarin da bayan shudewar mintina Arba'in yana kokarin kwace natsuwata kamar almara naji wani bakon al'amari na kokarin Ratsani Ratsawar da na manta ya yanayinta,kansa na tsakanin wuyana cikin Shakar Nunfashi naji yana karanto addu'ar da sai in zaka kadaice da matarka kake karantata kamar irin an buga kaina Gaf!yayi gaba sai yayi baya sai naji ni Tsamo Tsamo na dawo duniyar da ya tafi ni ina Dago idanuwana da suka yi min nauyi na kallesa a saman kaina daga ni har shi mun rasa suturun jikinmu,shi kokarinsa ya kai ga inda yayi alkawarin jinginewa na har abada ai kamar an sako min wani karfi bansan Lokacin da nayi wani yunkuri d'aya ba sai ga shi na barar da shi a gefena har keyarsa na bugun bangon Dakin na tabbata ba karfina ba ne Ya riga yayi laushin da bazai iya moran ma kansa wani abu ba.
Kafin ya dawo hayyacinsa nayi gefe ina Raruman kayan na,daga inda na turesa ya Dafe keyarsa dishi dishi yake ganina Tsabar Halin da yake ciki cikin muryan da ta shige ba'a ko jinta ya kira sunana"Faaaa...izaaaa"
Naji dai jan sunan nawa ammh ban tsaya bin ta kansa ba,na rarumi zanin Gadon da na cire zan wanke na nade jikina da shi ba inda jikina baya rawa,kuka kawai naji ya Sarkeni kawai sai na fashe da kuka har da Shessheka.
Da rarrafe da jan jiki ya kariso gabana sai ji nayi ya rikoni nayi saurin kwace kaina cikin ihu nace"kada ka sake ka tab'ani..'
Kada ka sake..".
Na fad'a cikin ihu lokaci d'aya da kuka sai ya kasa kara tabanin ya koma gefe yana kallona,da kafarsa ya ja gajerun wandonsa ya saka kaina na maida kasa ina kuka,kamar ana dawomin da komai haka abubuwan da suka wuce suka rika dawomin na Dade bana fama da Kuncin zuciya tunda Allah ya samamin mafita ammh yau sai naji kamar komai anan yake faruwa kirjina yayi nauyi bakinciki ya cikani da na kasa sarrafa kaina agabana ya Durkusa kamar jaririn dake neman nono wajen uwarsa,yana shirin kara tabani nayi gefe da sauri ina kara rike zanin gadon dake hannuna gudun kada ya rabu da jikina,Sai ya Daga hannu cikin kasala da sanyin jiki,idanuwansa sun sauya Launi Jijiyoyin kansa sun mike gabad'aya cikin alamun Sararawa yace"Na bari naji bazan taba ki ba,ammh kiyi ma girman Allah ki bar kukan nan ki tsaya muyi mgana Fa'iza"
Sai a lokacin na dawo hayyacina na Fahinmci gadar zare ya hadamin Allah na sona da Rahma da na Rufta acikin shirinsa da na shiga uku.
Bani kuma da sauran mgana burina da na dad'e dashi acikin raina zai mutu batare da na cika sa ba.
Rokona ya cigaba da yi ganin naki daina kuka ganin yana magiya kamar zai yi kuka yasa na saurara da kuka na, sai dai ban daina jan Numfashi ina Jan majina ba,zaman dirshan yayi a gabana cikin wata irin muryan da bazaka taba cewa Ishaq kabir karofi gaye dan kwalisa ne ya mallaketa ba murya ce da zata iya kasaara jikin ko wacce d'iya mace mai lafiya in dai ta jisa da muryan ya fara mgana cikin karyayan sautin da ni kadai zan jisa yace"Haba Fa'iza haba fa'iza meyasa..?kin san halin da kika sani Tsawon wannan lokacin..?ki dubeni kiga yadda na koma a gabanki don Allah ki kara bani dama na gyara kuskurena na yarda na amince ni mai laifi ne ammh kada ki horani ta wannan bangaran na amince ki min duk abunda kika ga dama,ammh ba ta wannan bangaran ba ki bari na samu natsuwa daga gareki koma menene sai ya biyo baya.."
Sai da ya Dire mganarsa na Dago jajayen idanuwana na wurgasa masa wani harara da mamakin jin kalamansa na karshe,cikin karya wuya yace"Don Allah Fa'iza.."
Har da kokarin sake rikoni na ko kara matsawa baya shima yana kara matsaoni da karfi nace"Ka na matsowa wlh zan yi maka ihun kwarto wlh"
Cak ko ya tsaya yana kallona cikin mamaki yace"Kwarto fa,kwarto fa Fa'iza..?
Kai tsaye ina kuka nace"Eh Kwarto nace. kuma ka kara matsowa kusa da ni kasha mamakina"
Sai ya koma gefe na ya zauna yayi Tagumi kamar wani maraya Lokaci daya yana fadin"Ina cikin wani Hali don Allah Fa'iza ki bar ni na samu natsuwa daga wajen ki don Darajan don Allah Fa'iza ki ji tausayina"
Banza nayi da shi ina ta sharan hawaye ya kara kwaso magiya har ya gama ban ce masa komai ba, sai ya matso kusa dani na zaro mai ido sai ya koma da baya hannunsa a sama yana fadin"Wlh bazan taba ki ba..ammh in kika min haka kin min adalci kenan Fa'iza.?zina kike so naje nayi ko kuma kina so na fad'a wata Halakan ne..?
Idanuwana suna fitar da kwalla na Dago ina kallonsa cikin Muryata nace"Adalci ka ke mganar ban yi maka ba..?kai kasan menene adalci kuwa..?kuma  da kake mganar ka da ka fad'a zina ko halaka, au sai yanzu kasan Ana iya fad'awa wannan halakar.?ammh baka taba Tunanin matar daka jingine Shekaru Biyar baka taba waiwayanta da sunan bata hakkinta na aure ba.Ita baka taba Tunanin wata Halaka zata fad'a ba..?ko ita ba Mutum bace..?ko ita bazata iya fadawa zinar ba ne..?
Na fada cikin wani yanayi Lokaci kamar alokacin yake fadamin ya zabi Zainab sama dani sannan ya jingine aurena fiye da shekaru biyar ammh Saboda Namiji bai da kunya har zai iya nema na da wani abu..?
Wani irin kallo nake bin sa da shi kallon tarin takaicinsa da bakincikin da yayi shekaru yana kunsamin Hawaye suna kwarnya a saman fuskata.
Kansa ya dafe cikin wani yanayi lokaci d'aya yana fadin"Na sani..nasan ni me laifi ne Fa'iza kiyi hakuri ki yafemin nasan nayi miki tarin laifukan da bazasu yafu lokaci d'aya ba, ammh ki duba ki gani wlh nayi nadama nayi nadama ki bani dama na gyara kuskurena"
Cikin kuka nace"Ina nadaman da kayi..?yaushe ka fahimci Fa'iza mutum ce kuma macece kamar zainab..?
Sai ya kasa mgana ya fara mgana cikin kame kame yana fadin"Tun tuni Fa'iza,Wlh tuni na gane kuskurena.
nayi nadama kema kin sani"
Kai tsaye nace"Babu abunda na sani.Abu d'aya na sani cewa baka sona baka taba kaunata ba.ka zauna dani ne saboda Baba..ka ce bani da amfani kace ni ba matar kwarai bace, ni ba matar rufin asiri  ba ce kace ni  Fa'iza ban dace dakai ba,Alfarma kake yi min,ka manta ka sha fad'amin baka Daukeni a bakin komai ba..?ka manta da kanka ka kirani ka nemi alfarman na barka ka yi rayuwar aure da Zainab ni kuma ka jingine aurena ba.?ko ba kai ba ne ka zabi wata macen sama dani ba?meyasa sai yanzu kake tsammanin komai zai zo maka da sauki..?.
Na karishe fad'a ina tsiyayan hawaye,wani Turiri da hayaki na fitowa daga kasan raina,Hannuwana ya riko jikinsa na rawa yace"Na sani ki bar tuna baya wlh a wanchan Lokacin bansa me ya shiga kaina ba ne,Ammh wlh na dawo hayyacina na gane kuskurena na fahimci sakacina da laifina na fahimci sakacin da nayi Wlh na tuba na tuba..nabi Allah na biki Fa'iza na dade da sanin kin fiyemin kowacce mace amfani a Rayuwata kuma na dade da sanin nayi kuskuran furta kalaman jingianan auran mu fa'iza,ki bani Dama mu sake gyara rayuwar auran mu a karo na biyu don Allah Fa'iza.."
Yafad'a lokaci d'aya yana jimke hannuwana cikin nasa sai kawai nayi Dariya lokaci d'aya da kuka kamar Mahaukaciya kafin nace"Fa'iza ce fa,kurma diyar Bebiya,Baka mummuna,Mara ilimin boko,mara gata mara kyau da nasaba,macen da bata chanchanci namiji kamar Ishaq kabir karofi ya so ta ba.Ni ce fa Fa'iza yar gargajiya nan,ina nan ban sauya ba.Ni ce dai wacce ka ke ciyar dani Saboda ina zaman kula da ya'yan ka, Fa'izan ne da ka ke tafiya wajen wata macen kafi wata biyu baka kirata a waya kaji yaya lafiyanta ba, Fa'izan da da bata san komai ba, sai ibadar aure da kula da ya'yanta da aka bar mata amanar su Fa'izan da ka rabata da kowa nata ciki har da mahaifiyarta marainiya da bata dukan wani gata, bata da uba bata da wani babban yayan da zai Tsaya ma rayuwarta ita ce dai wannan Fa'izan da Mama da Anty Binta suka maida abar wulakantawan su da cin mutumcin su, wannan fa Fa'izan da baka san ganinta Fa'izan nan ce da kake jin kunyar nuna ta amatsayin matarka, ita ce wacce kake jin kunyar duniya taga ya'yan da kuka Haifa tare ita wannan Fa'izan bata d"
Ban karisa ba ya rufemin baki da Hannunsa ina kuka,hawaye jage jage,da majina shima idanuwansa Jajir kamar zai yi kuka yace"Fa'iza ki bar tuna baya..Na rantse da zatin Allah na gane kuskure na,Wlh kin fiyemin kowacce mace a wajena yanzu.Ki yi min aikin gafara ki yafemin laifuka na nayi miki alkawarin zamowa mijin da baki taba jin Labarin kamarsa ba'
Don Allah Fa'iza ki yi hakuri"
Kauda kai nayi kada kalamansa su sakani rauni cikin shakewar murya nace"Saboda yanzu ka rasa komai yasa nake da amfani a wajen ka..?
Da Sauri yace"Wlh Talllahi ba haka ba ne. Allah ne ya dubeni da idon Rahma..Ya ganar da ni da wuri ba sai na mutu kasa ta kasa karb'ana Saboda bazan zamo adali gareki ba,Wlh Fa'iza in baki yafe min ba to Baba ma dake chan kabarinsa bazai taba yafemin ba"
Kiran sunan Baba da yayi sai rauni ya kamani cikin kuka nace"Allah sarki bawan Allah mai son zumunci da son ya'yan yan'uwa. Allah ya jikan baba da Rahma"
Da rawan jiki ya amsa da ameen Lokaci d'aya yana fadin"Ki yafe min Fa'iza ko don darajan Baba.Ki yafemin ki kuma bama Rayuwar auran mu Dama ta biyu don Allah.."
Sai kawai na kallesa ina fadin"Ta ya ya zaka Zauna da wacce baka taba so ba..?
Da Sauri ya Rumgumeni yana fadin"Wlh INA SON KI FA'IZA..wlh ina sonki"






*Janafty*
*KNKB2011*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

Kalaman Ina sonki Fa'iza. Sun shiga jikina sun kusa kassarani sai nayi masa kuri da ido kawai,bawai don na yarda da mganarsa ba,Ba kuma don na taba rikesa a raina ba,so nake ya kyaleni yasa na yi saurin cewa"To ka sakeni mana"kara kamkameni yayi yana fad'in"Sai kin ce kin yafe min. kuma kin amince ki bama rayuwar auran mu Dama ta biyu"
Cikin Sarkewan numfashi nace"Na yafe maka ban taba rike ka a raina ba Yaya Ishaq,a komai in kayi min bana ganin laifinka. alfarman da kayi min da kake zaune dani baka taba korana ba,shima wani abu ne,na yafe maka duniya da Lahira"
Sai kawai ya kara kamkameni yana Dariya cikin farinciki yake fad'in"Thank you so much Fa'iza.Na gode nagode.."
Lokaci d'aya yana sumbatar bakina nayi saurin kwace jikina ina fadin"Na yafe maka ammh kuma ina da Sharad'i na"
Sai jikinsa yayi sanyi ya koma yayi min kuri,yana kallona bakin sa na rawa yace"Me ne sharad'in Fa'iza.?
Yana bani mamaki sunan Fa'iza a bakinsa kamar shi ya rad'amin.
Ina kallon cikin idanuwansa nace"Na yafe maka duka abubuwan da kayi min. Sai dai indan har kana so na kara bama auranmu wata Dama, sai dai kayi min alkwarin bani Lokaci har zuwa sanda naga dama sai nayi maka mgana"
kamar ya had'iye wani abu sai da naji karan miyan da ya wuce ta makogwaronsa mukut.
Ban damu ba, na cigaba da fadin"in kuma  ka matsa min to zan fasa yafe maka.sannan kuma bazan iya cika muradinka na bama auran mu wata Damar ba"
Da Sauri yace"Aa to to na amince.ammh Fa'iza har zuwa wani lokaci?kada ki dauki Lokaci kinga fa Halin da nake ciki..?
Kai Tsaye nace"Ba ruwnka da Lokacin da zan d'auka  alkawari shine kada ka takuramin in kuma ka takuramin zan fasa gudirina"
Da Sauri yace"To bazan takura miki ba"
Yafad'a harda daga hannu,Hawayena na Share ina kara rike zanin gadon hannuna kada ya subucemin,a marairaice ya kalleni kafin yace"Fa'iza ki yi ma girman Allah ki barni na rumgumeki ko na samu saukin abunda nake ji"
Ido na sakarmai cikin mamakin kalamansa kafin na daure fuska nace"Sai yau ne ka fara shiga wani Halin Saboda ni ko yanzu ka fara di'n..? Ban basa damar mgana ba nacigaba da fadin"kuma kada ka fara karya alkawarin ka,nima zan karya nawa"
Da Sauri ya matsa baya yana fadin"Na bari.Wlh na bari bazan kara tab'aki ba,sai kin ce na tabakin"
Sai ya kusa bani Dariya sai da na murmusa,kokarin mikewa nake yi ya mike zai riko zanin gadon na balla masa Harara da Sauri ya juya yana Raruman kayana ya mikomin yana fadin"Dama..dama kayan ki zan d'auko miki"
Ban yi musu ba nasaka hannu na karba,da sauri ya bani Hanya yana fadin"Ranki ya dad'e ki huce lafiya".
Ban tankasa ba na fara tafiya ina Tattare zanin gado yabi ni da kallo har na fice ya koma ya zauna saman katifar yaraf kamar an sauke kayan wanki kansa ya dafe yana fadin"Allah na tuba..Allah ka yafemin..Ya Allah ka lallashi zuciyar Fa'iza ta sake bama auran mu wata damar"
Ban kara ganinsa ba,tunda na koma dakina naci kukana sai da na koshi sannan naje nayi wankar Tsarki na Tsabtace jikina, ranar ko Kunin aya ban yi ba zobo kawai na Dafa,Shima Daki ya yini sallah kawai ke fitar dashi ,sai da Hafsah ta dawo ta kai nikan kunin ayan,abinci kad'ai nayi mana sai gyaran gida,ko da Daddare kwanciyata nayi a daki ban fito karatun dare ba, Anum tazo na korata bace bani da lafiya ba jimawa sai ga shi ya shigo har gadon ya zauna yana Taba goshina da Sauri na jaye kaina ina bata rai da wata murya yace"To taba goshi ma sai ya zama laifi..?
Saurin matsawa nayi ina fadin"Ai a shari'a ma yanzu kai ba mijina ba ne,in nace bazan zauna dakai ba,ba wanda zai matsamin na zauna dakai"
Ina gani jikinsa yayi sanyi cikin wani yanayi yace"Fa'iza wata shari'ar ce ta ce haka..?
Kai tsaye nace"Baka sani ba..?ai musulunci yace Haramun ne ka yi wata Hudu baka kusanci matarka ba. Sannan jinginan aure a musulunci kamar sakin aure ne"
Kafin na karisa yayi saurin tareni da fad'in"Ba saki ba ne Fa'iza wlh ban sake ki ba. kuma har abada kinsan auran mu ba saki in sha Allahu"
Ina jinsa ban tankasa ba na koma na kwanta shi kuma sai ya mike yana fadin"Da alamu dai lafiyan ki lau yau laifina ya shafi ya'yan Umma kenan..?.
Baya na juyamai ban kara masa mgana ba ina jinsa har yana gyaramin bargo ya fice yana fadin"a huta lafiya Fa'in Ishaq"
Tun daga ranar bai kara matsamin ba da ya fara na d'ago na ballamai harara sai ya koma gefe yace"Yi hakuri".
Ko Allah ya baki hakuri,Daganan sai na samu lafiyansa,ko bakomai na daina fargaban zai ritsani ko zai mamayeni irin na ranar,ammh duk da haka ina taka tsantsan da shi Saboda naga da gasken yake yayi nadama,kuma na karb'i nadamarsa ammh ba domin zan iya karban bukatansa na sake basa wata damar ba.
Mama ta dawo bayan tayi kwarari wajen wata biyar a yamai, yan'uwan ma sun so tayi zamanta achan ne Mama taki sana'o'i suka dinga yi a chan ita da Anty Hure kuma sun had'a mata yan kudade kafin ta dawo da su aka samu aka biya kudin makarantan yara,aka siyan kayan abinci tunda yan kudad'en hannuna mun cinyesu wajen siyan abinci sannan ya turama Jamal shima wani abun,Ga Badariya itama suna shirin zuwa bautar kasa ne ita laluranta kad'an ne babban abu shine kud'in haya da kud'in makarantar Jamal tunda shi ajin karshe zai shiga ya maimaita aji hud'u,yana karatun Software enginearing ne.
Kudin Hayan nan da shi nake kwana araina,kud'i ba yan kad'an ba wajen dubu Dari hudu ne wannan gidan,Shi kan shi ya damu tunda mai gidan ya fara mganar kudinsa tun watan daya gabata sai ya bashi hakuri yace ya karamai Lokacin,mai gidan daman ba shi da kansa ba ne,Komai na Hannun babban d'ansa ne,kuma ba wani kirki da ya cika ba,Don ma yana ganin mutumcin Yaya Ishaq da Tuni ya fara yi mana sallama.
Zagayowar wannan shekaran sai dai Godiyar Allah jamal ma gida ya Dawo,Anty Binta kuma da an yi mgana sai tace tana da biki a gabanta,bata da kudi shi bai ma nemanta,Mama ce ta kan kirata a waya tana fad'a mata sai ta fara korafin itama akwai hidima agabanta,Abuja ma yanzu sai yafi wata bai je ba,Ita Zainab din ne ma,takan turo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login