Showing 75001 words to 78000 words out of 82431 words

Chapter 26 - Kana Naka Book 2 Hausa Novel Complete

Janafty   

07 Dec 2024

206

duk da haka bai nuna ba nan take na tayasa murna ya amsa yana fadin"Wlh ban taba saka rai aiki nan zai dawo gareni ba,Ammh sai ga shi sun kirani sun bani takarda har da karin girma da kuma sauyin wajen aiki"sai na tare sa da fadin"Haka Allah ke lamarinsa. Sai ya baka ya kwace in kuma yaga dama sai ya maida maka mafiyinsa"
Cikin gamsuwa ya gyada kai yana fadin"Hakane wlh. Allah ya datar mu"
Na amsa mai da Amen mun yi sallama yace zuwa anjuma zai kamo hanya ina shirin nace sun yi mgana da Abba?sai na sha'afa sai ga shi ma Abban ya kirani da kansa ina Dauka yace"Congratulation Dougther yanzu na samu labari wajen Dr.Lawal"
Cikin mirmishi nace"Daman yanzu nake shirin kiran ka Abba"
Kai tsaye yace"Gashi ni na rigaki,Duk na kira sauran yan'uwaki na shaida musu. Allah ya tayasa riko Zaki koma kusa da yar'uwanki Fadila tana ta jin dad'i da na shaida mata"
Sai mirmishi na ya Dauke da yake da cijewa muka gama wayar nan,yinin ranar sai amsa waya nake yi har mamakin yarda mganan ta Je, kunnen kowa nake yi,Yaya Asiya tace min Goggo ta fad'amata sai ban yi mamaki bam Saboda ni na kira ta da kaina na fad'a mata.
Ranar ya dawo da Daddare,yana shigowa ni ya fara cin karo dani a Tsakar gida ina kaye kayen kaya sai ji nayi ya Daukeni Caraf ya dagani sama yana juyi dani cikin Firgita nace"Innalillahi ka sauke ni don girman Allah"bai saukenin ba sai da yaji muryan Mama sannan ya saukeni Tana fitowa ya sakeni ya nufeta yana Fadin"Mama.."
Cikin jin dadi tace"Na'am Ishaq naji abun arziki Allah ya sanya alheri"
Ya amsa mata cikin fara'a ta dafa kansa tana sakamai albarka,mganarsa yaran sukaji suka firfito suna masa oyoyo d'aya bayan d'aya ya dinga dagasu yana saukewa Anum sarkin mgana tace"Daada yanzu Lagos zamu koma..?cikin shafa kumatunta yace"Sosai chan zamu koma."
Musty yace"Daada dukkan mu?
Ya gyad'a masa kai Lokaci d'aya yana fadin"Dukkan mu mustapha.."
Amir ne ya kalleni yana fadin"har da Umma da Mama..?
Kai tsaye ya bashi amsa da"Eh har da Anynku dasu Farhan"
Sai suka saka Ihu,yana biye musu da Dariya ni dai sau daya muka hada ido na kauda kaina,Daki na koma shi kuma da yaransa suka shiga Dakin Mama sai chan ya fito Hafsah tayi mai Fatan alheri ya amsa bakin nan har har kunne.
Garin ana d'an zafi zafi da ruwan Sanyi yayi wanka na kai masa abinci yana ci yana bani labarin abubuwan da suka faru cikin hirar nasa ne yake ce min"Sai zuwa gobe zamu yi shawara Fa'iza. nan da wata d'aya suka ce zan fara shiga office bana so na kara raba iyalaina Waje d'aya zan had'eku bari kudi su shigo kawai"
Ina kallonsa nace"Yaushe su sukace zasu maida maka kudaden na ka..?
Yana lomar shinkafa yace"Ko wani Lokaci zan iya gani suka ce"
Ni dai ina jinsa yana ta Tsara abubuwansa nayi masa gum sai in ya sako sunana ne zan daga kai nace tom ko Umh,naja bakina na tsuke ni dai gajiya nayi naje na kwanta shi da yaran sa falo suka Dawo suna ta Shagalinsu tun ina jinsu sama sama har barci ya Dsukeni.
Tun daga washegari muka yi samun bakin Taya murna wad'anda basa kusa sun yi mana ta waya Goggo tazo Yaya isa ya kawota tayi mishi Murna,Anty Binta baki har kunne,ita da Mama,Jamal yana makaranta suna Jarabawa Badariya dai sai ta zo gida ta kwana Biyu,ranar da ta dawo zuwa tayi ta Rumgumeni tana fadin"Ina murna matar yaya. Allah ya sanya alheri"
Na amsa mata da mirmishi sai ta fara zolayata da fadin"Har mun fara kewa Anty Fa'iza yanzu chan ikkon zaku koma.?
Kai Tsaye nace"Za dai ku koma Badariya"
Cikin jimami tace"Ni ina kano kin manta,ban gama hidimar kasa ba"
gyada kai nayi ina fadin"Duk da haka dai. in kika gama chan zaki koma indai ba aure kika yi ba"
Daganan muka cigaba da Hira duk akan mganar aikin ne,ni da kaina na Kira Hajiya na sanar da ita,tace zata zo taya murna abun mamaki har da kawayen Mama da suka gujeta a baya har da su a masu taya murna. Hajiyar Dala bata zo ba ta dai kira mama a waya da dashi da Uban gayyar ta masa murna nima su Nana Fadila duk sun kirani ita har ta fara murnan zan dawo kusa da ita. ban ce mata komai ba sai yake a raina ko nace kiyi hakuri Fadila hakan bazai tabbata ba.
Baki muka yi ta samu ta ko'ina abun har mamaki yake bani,shi kan shi yace wasu wlh sun manta ma dashi Lokacin da ya rasa ammh sai ga shi har da su a sahun masu murna,mganar da yace zamu yi duk bamu samu mun yi ba. nasan kan mganar tafiya lagos ne tuni mutane har sun gama daukan zencen Lagos zamu koma gabad'ayanmu har da yara.
Yaya mariya bata zo ba. A waya ta kira ni bayan mun gaisa tace"Ashe kuma abun alherin da ya samu kenan..?
To Allah ya sanya albarka.Goggo ke tad'in Lagos zaku koma daa ke da yaran gabad'aya"sai kawai na ce mata haka yace,yaya mariya bazata sauya ba sai ta karkace baki tana fadin"itama yar abujan fa?ina fatan chan zai barta domin Lagos ke kad'ai zaki zauna kamar yadda ki ka bar mata Abujan ita kad'ai"
Sai nayi dariya kafin nace"Ya ce gabad'ayanmu zamu koma har da Mama"sai ta tabe baki kafin tace"A na nan dai jiya iyau"
Ban biye mata ba shiyasa bamu dad'e muna mgana ba muka yi sallama.
Bamu samu zama ba sai da mutane suka Tsagaita,Ranar ma da daddare,Dariyan Musty muka sha wai har yayi ma yan ajinsu sallama su zasu koma Lagos gabad'aya.ina Dariya nace"kaji yaro da zakewa. "
Yaya Ishaq na gefe yace"Ba wani zakewa ya fad'a musu gaskiya da ya tafi ba sallama fa..?
Amir yace"Umma da Anum na zuwa makaranta da tuni kowa ya sani"
Ita muka kallah yadda tayi yasa muka kwashe da Dariya,kowa yasan zata aika da bakinta kamar na aku,har fa gidan da muke kai nika da taje sai da tace lagos zamu koma zamu tashi Daga gidan nan kamar an tambayeta,Amir ke fadin da yaje kai nika suka tambayesa,kallonta nayi ina fadin"To wa ya aike ki gwana..?
Cikin Shagwaba tace"Umma sallama nayi musu kada suga min daina kai nika"Sai ko muka kara saka Dariya sai ta fara kokarin kuka Ya jawota jikinsa yana fadin"manta da su mamana ki fad'a ma kowa lagos zaku koma sannan ki kara da fad'a musu a jirgi zaku tafi"Da sauri ta waro ido tana fadin"Daada jirgi fa mai tashi sama..?
Ya daga mata kai kawai sai ta fara Tsalle tana murnan zasu hau jirgi Ahmad da Musty na tayata,Amir dai na zaune yana bin su da kallo.
Yaro shi yana son sauyin muhalli,Amir ne yayi hankalin cewa'Daada in muka koma chan wata makarantar zaka sakamu?
Yana dariya yace"Amir d'an makaranta. Kada ka damu makaranta mai kyau zan saka ku in sha Allahu"
Daganan ya cigaba da biye ma yaran suna masa tambayana yana amsawa.
Ni har zan shige daki yace yana son mgana dani,dole na hakura sai da yaran suka yi mana Sai da Safe suka shige Dakin su,sanin in yace muje Dakinsa bazani ba yasa muka zauna afalo ya fara da gayamin EFCC ta dawo mai da kud'insa kimanin Naira miliyan Sitti,Tunda ba lalle kudin mutum su dawo duka ba.
Shine  ya ke ce min yanzu ya yanke shawaran zai fara yin gaba yaga yanayin garin da komai,zuwa ya sama mana inda zamu zauna tunda Abba yace zai had'asa da mijin Nana Fadila.
Ban yi mai musu ba nace shawaran shi tayi sai ya cigaba da fadin"gida nake son siya babba wanda zai wadace mu. In bai samu yanzu ba, sai na kama Haya zuwa gaba in na samu a hankali a hankali sai na siya na kaina"
Kai Tsaye nace"Gwara ka mallaki naka zai fi. Kuma mganar ka siya babba kada ka yi asaran kudin ka,ka siya daidai zaman mata d'aya da Dakunan yara,kana da maza sannan mace Daya gareka Anum,Ga mama ga su Badariya duk da ita tace sai ta gama hidiman kasa tukunnah"
Cikin mamaki yace"Bangane wajen mace da'ya ba.?ina miki bayanin itama Zeey na gayamata ta fara shiri,kila ku zaku fara yin gaba ita sai daga baya zata same mu achan"
Mirmishi nayi kafin nace"Ka gane mganata mana. ni fa bazan bika Lagos ba"
Sai ya yi karamin Tsaki kafin yace"To sai ki zauna a ina.?kai tsaye nace"A nan mana"harara ya sakar min kafin yace"kina Hauka ne.?ina wata Duniya kina nan?wazai barki di'n? kafata kafarki, kafar yarana Fa'iza"
Sai ban ce komai ba na kauda kai bai Damu ba ya cigaba da fadin"Abba yace na siya mota saboda zirgan zirgan  zuwa wajen aiki da sauran dai Bukatu"jin sa kawai nake yi ina tunanin ya dauka wasa nake yi sai na kara gyara zama nace"Da gaske nake yi. ni bazan bika Lagos ba"
Sai kawai ya mike yana fadin"Bina ko kamar kin gama shi Fa'iza meyasa zan barki.?ba mai kara rabamun hankalina yanzu iyalaina duka waje d'aya zan had'asu"
Kai Tsaye nace"Yanzu kuma.? Ni fa kada ka manta na saba zama ni kad'ai a baya ma kana Abuja ina katsina, kuma na zauna lafiya sai don ka koma Lagos..?
Kallon sai ki yi yayi min ya shige Dakinsa ya bugo kofa sai ya bani Dariya ya Dauka wasa ne?lalle ko zai ga wasa alokacin da bai yi tsammani ba.
Ya samu mun fara tattara kayanmu,ni daman ma na had'e nawa na yara ne ba'a gama had'awan ba,yace bazai saki gidan ba sai in ya siya wani inda zamu rika sauka inda munzo,tunda dagamu sai kayan sawa zamu tafi sauran kayan gida Sabbi za'a siya kawai,har sun yi mgana da megidan ma ya bashi kudin Shekara,Hafsah kuma daman bata da matsala Transfer dinta ya samu kaduna zata koma,ranar muna tattara kayan kitchen waje daya Anum tace"Umma shikenan kin daina zobo da kunin aya..?
Kai tsaye nace"In ji wa..?zobo da kunin aya yanzu na fara"
Na tuna ko ranar da Hajiya tazo min murna na fad'a mata lagos aka kaisa tun kafin na yi mata bayani tace duk inda naje kada na saki sana'ata domin sana'ar hannu abu ne mai kyau da amfani kuma na aminta da mganarta na Jaraba kuma naga riba,kuma dayake nima baama Lagos din zani ba ballatana ya dameni, inda zan koma da zama na tabbata zan rika yin ciniki sosai.
Kuma ko da muke tattara kayan ina sana'ata ban fasa ba,Mama ma nata shiri tunda yace in yaje ya dawo har da su Anty binta za'a tafi saboda suga waje,Sati hudu Tsakani ya tattara ya tafi,jirgi ya bi daga kano zuwa Abuja,bayan ya isa headquater din su ya saka hannu sun bashi accepted letter,Daman yana zuwa ya kira mijin Nana Fadila shi Costume ne,gidanta ma ya sauka yaci abinci ya huta sannan suka fita duba gida,sun duba inda yafi kusa da ma'aikatan su anguwan Apapa lagos,ya siya apartmemt,gida ne mai girma ba sosai ba,Falo hud'u mai Dauke da bedroom da Tiolet guda takwas,yana da girma gidan tunda akwai Haraba sosai,sai kudi wajen miliyan Ashirin gidan tunda Sabo ne shima mijin Nana Fadilan wani kaninsa ke harkan gidajen shiyasa suka samu da sauki,Ya siya gidan sannan kuma yayi oder din gadaje da kujeru da sauran kayan bukatu da ya Kirani ya fad'amin sai nace"ka san kana da yara a siya musu kananun Gadaje. Ga uku anan ga biyu Farhan da Fadil,Anum kuma ko ita da Badariya sai ka had'asu,Mama kuma tana Dakinta ita kadai sai jamal kada ka manta da shi"
Cikin gamsuwa yace"ban manta da shi ba wajen zai isa ba takura fa. na Dauko muku hoton gidan in na Dawo zan nuna miki"Da haka muka rabu sai da yayi sati sannan ya Dawo da shirin zai tafi damu gabadaya Zainab kuma sai daga baya zata biyomu ita.
Sallama yace duk mu yi da abokan arzuka da yan'uwa da makota,Ranar a karofi muka yi yini,washegari kuma da muka dawo na zaga cikin gari naje nayi ma Sa'adatu da Habiba sallama saboda  sabo har suna kwallah,makaranta yara daman tun kwanaki naje na sanar da su suka ce zasu yi kewar hazikan Dalibai.
Hajiya ma naje mataa sallama,ta bani kyautan kaya da su Turaruka da mayama mai na gyaran jiki muka rabu cikin mutumci,Abba dai shi ya hana naje yi masa sallama duk da ko ba inda suke tunani zan tafi ba, yace shi zasu je har lagos suga muhallina.
Anty Binta da da Mama sai Anty Hure da tazo zasu tafi daga bangarena yace a samu mutum biyu sai Goggo ta wakilta Anty Nasara da matar Yaya Isa tunda Yaya mariya tace bazata samu zuwa ba,Yaya Asiya kuma yaronta bai da lafiya yana fama da kyanda.
Tafiyar jirgi yace zamu yi,zamu je kano daga katsina kenan,Ya siya mana Ticket gabadayanmu zamu tashi karfe uku na ranar talata,damu da kayan sawan mu,ana gobe Tafiyar na had'a komai nawa na kayan zobo na da kunin aya.
Sannan na cire soket din Freezer di'na,duk kulle kullen da Goggo ta aikomin da shi na had'a cikin kayan yaran nasa zai musu amfani.
Na zata ina da Dauriya sai ga shi na fara raunanaa, in naga yadda yaran ke Tsallen Murna ina Tunanin ya ya zasu ji gobe in har na ce musu ba Tafiyar mu d'aya ba..?





*Janafty*
*KNKB2020*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

Ko yaran ban bari sun fahimci Halin da nake ciki ba,daki na shige ina kokuwa da yanayina.
Nace kada su dameni da Hayaniya Hafsah bata nan daman tun jiya ta wuce karofi daganan Abba zai turo mota a Dauketa zuwa kaduna.
Yaran ne kad'ai da babansu ke ta Budurin su da murnan gobe zasu hau jirgi,sannan zasu koma Lagos da zama,kayan su dai masu muhimmanci na hada musu saboda tafiyar jirgi ce yace ko shi daga baya zai saka a taho mana da komai gabadaya,Badariya tana kano sun kusa gama Hidimar kasa bata da Lokaci sai dai zata taho daga baya.
Kwana nayi ina kuka Sai dai ban kwanta ba ina sallah hawayena sun kasa tsayawa sai kuma naji kamar abunda nake shirin yi bai kyautu ba.?kamar in nayi haka na karya raunin zukata da dama ciki har da ta yarana. da suka fi kowa shakuwa dani ammh sai wata zuciyar ta tunasar da ni Babban Dalilina da yasa naji na kara samun karfin zuciya.
Sai dai a komai in zan yi ba ma yin gaban kaina Allah nake fara sawa cikin Duka al'umarana,Shi na daga hannu na roka da kyawawan sunayensa sannan na yi masa magiya na yi masa naci ina kuka ina fadim"Ya Allah kasan damuwar dake damuna acikin zuciyata, sannan kasan wahalwahalun da nayi ta fama da su yayin biyayyan auran da kai ka Umarcemu da yin sa.
Sannan kasan komai da ya faru tunda kai mai ji ne kuma mai gani ne na yanke wani Kuduri a raina ya Allah in har ba alheri acikin Tunanina, Allah ka hanani aikata wannan kudurin nawa in kuma Hakan shine alheri a gareni da Duniyata gabad'aya Allah ya bani Hakuri ka sanyamin juriya kada kuma ka barni ni kad'ai kayi Riko da Hannayena sannan ka yimin Jagoranci a duka al'murana,sannan ya'yana Allah ka tallafe su,  kayi musu albarka, ka kara shiryamin su cikin addininka"
Ina addu'an kukana yaki Tsayawa sai na kife kaina a kan hannayena ina ta rafzan kuka,ni da barci sai wajen hud'u na asuba shiyasa na makara sallar asuba sai da naji sa a kaina yana Tab'a kafafuna na bude idanuwana jajir da suka kumbura saboda kuka,na sauke a kansa cikin mitsike ido na ce"An yi sallah ne..?
Kai Tsaye yace"Har mun dawo masallaci ni da yara kina kwance ashe baki tashi ba..?
Jin haka yasa na yunkura Dakyar na mike ina fadin"Ban yi barci da wuri ba ne"
Kai tsaye na wucewa zuwa Tiolet sai ya bini da kallo yaga idanuwana sun tasa ammh ganina a kan darduma sai yayi tunanin sallar Dare nayi,Ficewa yayi falon wajen yaran har Anum ta kunna gas ta Dora ruwan zafi saboda wanka,Amir kuma ya saka a Heater tunda akwai wuta.
Sai da idar da sallah na fito falon ina ganin an saka ruwan zafi nasan Anum ce uwar zumud'i ban dora abun kari ba sai da duk sukayi wanka har da Baban nasu,sannan na fere dankalin Turawa na soya musu sai ruwan Tea muna da sauran kayan ciki sai nayi mana Ferfesu da yawa saboda Mama da Anty Hure,su Anty Nasara suna Karofi sai yau zasu taho ammh ina Tunanin zan Dakatar dasu.
Saboda tafiyar dake gaban mu yasa suna gama karyawa suka fara shiri ni dayake ban iya saka komai aciki na ba gabad'aya komai baya min dadi.
Yaya Ishaq yana dakin mama shi da yaran zainab ta kirani bayan na Dauka mu gaisa tace"Maman Amir yau sai kwanan Lagos ko?
Sai nayi yake kafin nace"Uhm ke bakin k'i mu je mu gyara gidanmu tare ba.?tana dariya tace"Wlh ba haka ba ne zan tsaya shirye shirye ne Daddy wannan karon bai bani matsala ba,da Full yes din sa zan koma ai ko Sati biyu baza'ayi ba zan same ku achan in sha Allahu"Jin haka yasa nace"To Allah yasa"
Ta amsa da Ameen mun taba Hira sama sama na tambayeta yara tace suna makaranta,mun yi sallama cikin girmama juna kamar yadda muka saba,har ta kashe sai na sake kiranta tana dauka nace"Maman Fadil ga amanan yaran nan. Don Allah ki kula da su sannan kiyi hakuri da su,Amir da Anum sun girma nasan zasu yi miki kokarin kula da sauran kannensu. In sun yi ba daidai ba ki tsawarta musu ki yi musu fad'a ki Tsaya kan tarbiyan su don Allah, in sun fi karfin ki ki had'a su da Babansu shi sai ya yi musu hukumci"
Bata gane kan mganata ba yasa tace"yaran da duka nakin da nawan kike hadawa ki rike Maman Amir..?kinsan bani da juriyan kwarammiya yara fa..?kina ma wata mgana muna komawa ai su Farhan daman ya'yan ki ne"Sai nayi mirmishi kafin nace"Ki rike mganata zaki tuna da abunda na gayamiki watarana"ban tsaya sauraran mganarta ba na katse wayata ina maida numfashi anya zan iya kuwa.?sai wata zuciyar tace min zaki iya in sha Allahu Fa'iza.
Anty Nasara na kira tana Dauka sai tace min gasu nan gidan Goggo yanzu zasu taho kai tsaye nace"Ku yi zaman ku nima ganinan tafe"
Cikin mamaki Anty nasara tace"Ga ki nan zuwa..?ban gane ba.?kun fasa tafiyar ne..?
Kai Tsaye nace"Aa.."
Anty nasara tace cikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login