Showing 66001 words to 69000 words out of 82431 words
ke faruwa.
Shima da gudun yabi bayana yana kiran sunana gaba na ya sha yana Haki yace"Ke ke ina zaki..?
Cikin duhun Korodin dakin Jamal na balla masa Harara ina fadin"Tafiya zan yi..Zan tafi ne wlh bazan zauna dakai ba"
Na fad'a masa cikin Tabbacin mganata sai ya Rude ya fara fadin"Ban gane ba.
Wani irin tafiya kije ina kuma..?.
Kai Tsaye nace"In da baza'a takurani ba sannan inda nima zan kai kararka.Nima ai ka jingine shekaru ina maka gadin ya'yan ja wa na taba kai ma kararka..?sai ni Zaka kai ma Mama karar na hanaka kaina ina ce ba kai ka ce na kyaleka ba..?
Ba kai kace na barka kayi Sabuwar Rayuwa da wacce ka zaba ba .?
Meyasa sai yanzu zaka matsamin na gayamaka aurena dakai ba aure ba ne yanzu,Jingina ne.."
Na karishe fad'a cikin Tsawa lokaci daya ina kuka sai ya kasa mgana Saboda yadda na ke ture hannunsa in yakai min zai rikeni Cikin fitan Hayyaci yace"Ke ba ki Afuwa ne Fa'iza..?wlh na yi nadama na tuba na bi Allah na biki kiyi ma girman Allah ki saurareni"
Da Sauri na daga masa hannu ina Fadin"Bazan saurareka ba. Na fada maka ka daina cewa aure aure, auren mu a jingine yake in ka cigaba da matsamin na rantse da wanda raina ke Hannunsa zan bar gidan nan Daman ya'yan ka ne kuma sun yi girman da zasu kula da kansu. Ahmad ne matarka ta had'a da na Hannunta da wanda zata haifa ta rike maka ammh in dai na tafi to Har abada BAZAN DAWO BA"
Na karishe fad'a ina Tsaida kallona a kansa Cikin Firgici yace"Eh. A'a kije ina.?Fa'iza kina son ki kasheni ne..?
In kika tafi to na zauna da uban wa.?.kai Tsaye nace"Ka zauna da Zainab wacce ka zaba sama da ni"
Kara girgiza kai yayi yana fadin"Aa ba inda zaki.Ba zaki tafi ba Fa'iza in ba so kike na laalace ba"
Cikin kuka nace"To wlh in ka kara matsamin sai na tafi kuma nayi Rantsuwan in na tafi bazan dawo ba. Sannan in ka kara kai karata ba ma wajen Mama ba,wlh ni kuma sai na Fallasa ma duniya komai, tasan Tsakanina Dakai auran jingina ne"
Kamar na watsa mai ruwan zafi haka yaja baya yana fadin"Na shiga uku don Allah kiyi hakuri Fa'iza, eh naji Wlh naji na yarda bazan kara matsa miki ba ammh kimin rai kada ki fad'i wannan mganar wani yaji don Girman Allah.."
Kukana na Tsagaita kafin nace"To naji bazan tafi ba. kuma kamar yadda nayi maka alkwari tun a baya sai dai kai ka fadi mganar da bakinka ammh ni nayi maka wannan alherin kamar yadda ka Rokeni,kada ka kara cewa zaka Takuramin ba wani hakkin ka dake kaina, domin tun kafin auran ka da Zainab ka rokeni da nayi maka adalci na kyaleka kayi rayuwa da wacce ta dace Dakai a lokacin ban yi maka korafi ba. sannan ban taba maka gaddama ba har Tsawon yau din nan To nima bana son kayi min Korafi abunda ka zaba ne, nake yi maka kada ka kara damuna ni bani da jikin da zan baka ka mora sannan ban chanchanci wannan binbinin daga gareka ka ba. kyaleni don girman Allah.
"Na karishe fad'a cikin Kuka ina Had'a Hannayena jikinsa a Sanyaye yace"Duk naji na yarda mu koma cikin gida kuma ki daina kuka ga yara chan kada su dauka na Dake ki ne"
Ban yi musu ba na daina kukan na Share hawayena na kama hanya na koma yabi bayana muna Zuwa Tsakar sai ga Hafsah ta fito daga Dakin Mama abinci ta kai mata tana ganin mu tace"Fita daman kuka yi..?
Da Sauri yace"Eh eh.."
Dagaji bai da gaskiya ni dai daga shi har ita rabasu nayi na shige ciki Suna cin abinci yaran Anum har ta mike taga nayi Zaraf na shige Daki har da banko kofa,sai suka yi wani shuru Baban nasu na shigowa suka sakamai Ido duk sai ya Daburce Anum ne tace"Daada me ya samu Umma..?
Da sauri yace"Umma.."
Ya kasa mgana Amir ne ya kwace sa da Fadin"Kila bata da lafiya ne" jin haka yasa yace"Eh eh bata jin Dad'i kuci abincin ku"
Daga haka ya wuce Dakinsa yana Zufa yaran suka bisa da kallo harda Hafsah da ta zargi wani abu na faruwa sai dai bata ce komai ba ta kira Amir ya Dauki abincinsa yakai mai,sai gashi ya Dawo dashi yace bazai ci ba. nima kuma sun kawomin nace su Dauke bazan ci ba,da suka shigo ma sun fara min Hayaniya na koresu nace kaina na ciwo,Su kansu sun san an tabani gabad'aya har wayewan gari suma duk sun yi wani iri ban ma fito ba Hafsah ta musu komai Hatta zobo ita ta Dafa ta barmin na hada ta wuce makaranta shara da wanke wanke kuma Anum tayi shi ban fito ba sai da rana Saboda zuwan dangin Mama daga yamai dole ta sani na Dora girki,Yaya Ishaq na dakinsa in ji Anum ammh ban ko duba barayinsa ba,Da yammah Halisa tazo nayi mata Dilka washegari da Safe muka hadu na gaisheshi ya amsa sannnan na gayamai yau zan je gidan Anty Binta akwai Walima ba gaddama yace a dawo lafiya, ni kadai na tafi yara suna makaranta Anum kuma tun safe tabi Anty Hure suka tafi.
Sai Dare muka dawo chan Badariya ta iskemu an yi walima ni nayi zobo da kunin Aya sannan tare da ni akayi cake din Rabo,Da Sassafe kuma na koma Saboda girki duk da ta Dauki ma'aikata ammh ni zan rika nuna musu komai yara basu je makaranta ba Hafsah da ta shiirya ita da Badariya ta taho da su,Hajiyar Dala ta zo ita da Suwaiba,Yaya Asiya ce bata samu zuwa ba Yaya mariya ma tazo abun mamaki har da su Anty Nasara,gida cike da baki na nesa da na kusa, aranar za'a Daura aure,sai washegari Lahadi da safe a wuce da Amarya mun yi waya da Nana Fatima da farko ban fad'a mata zan zo kano ba saboda nayi Tunanin in na tafi wazan bar ma gida? ammh Daga baya sai na fasa nace sai naje shi ya zauna ya kula da gidan da ya'yan sa.
ban yi anko ba saboda bata nuna ma kowa ba,ammh nima na yi shigar alfarma cikin kayan da Hajiya ke dinkamin ne super wax na saka,Da Daddare gida na muka dawo da su Anty Nasara yaya mariya dai chan muka barta daman nasan bazata Biyoni ba.
Amir na aika nace ya gayamasa zan raka Halisa kano,kai Tsaye yace Allah ya kiyaye hanya,Da yake shima da Safen ya shirya ya fita saboda Daurin auran Safe ne Na fad'ama Mama zanje kano sannan zan bar yara Saboda makaranta Ga Hafsah ga babansu tace ai daman ya kamata naje ni ko bata sani ba gidan ne da D'anta suka isheni. zan yi musu yaji na kwana Biyu.
Kaya kala Biyu na dauka da abunda zan Bukata,Anty Nasara ce zataje Goggo gida zata koma Hajiyar Dala Daman yan gida ne suna cikin masu tafiya.
Karfe goma da rabi aka Daura aure zuwa sha biyun rana an fara tafiya Saboda kada ayi dare ni mota D'aya muka hau da Badariya da Anty Nasara,Yaya mariya bata je ba megidanta bai barta ba.
Anum har da kukanta sai taje sai da nayi mata Jan ido Amir daman bai da damuwa sauran kuma suna wajen Babansu.
Ban taba zaton zan iya tafiya na bar ya'yana ko da na yini d'aya ba sai ranar, na gwada ne daman naga ko zan iya sai dai muna tafiya ne ina jin kamar na bar baya da kura.?wazai kula da su..?Hafsah tana zuwa makaranta shi kuma bai iya komai ba ballatana ya Kula da su, sai dai hankalina ya kwanta da na Tuna na Horar da ya'yana Musamman Amir da Anum zasu kula da Sauran kannensu.
Dama already an yi ma amaryan jerenta gidanta mai kyau ita kad'ai,da muka isa abinci muka ci sai sallah sai kuma dan Saura gyare gyare kawayen Anty Binta sun kama komai yasa mukayi musu sallama sai gidan Yaya Asiya. chan muka kwana muna Hira harda Badariya,washegari Litini muka shiga kasuwa na raka Anty Nasara nima har na siya ma Anum takalmi mai kyau na mata, da muka dawo har da Yaya Asiyan muka leka gidan Amarya chan muka hadu da ya'yan Hajiyar dala sai dare Direban da zai maida su gida ya Saukemu gidan Yaya Asiya ranar Talata Anty Nasara tace mu tafi sai nace ta tafi zan taho bata Damu ba ta wuce karofi a ranar,ni kuma bansan Dalilina nakin komawar ba Yaya Asiya kuma tasha Ishaq ne ya barni Har tana jin dad'i.
Tun da muka zo bai kirani ba sai ranar Laraba da Daddare ina Dakin Yaya Asiya ita kuma tana wajen mijinta naga kiransa sai nayi mamakin sanin bai da waya bayan na Dauka mun gaisa sai yace"yaushe zaki dawo.? Yara sun damu fa"
Sai na basar da tambayar sa,ina ya samu waya na tambaye sa,kai Tsaye yace"Zainab ta aikomin daga chan"
Sai na yi shuru ban yi mgana ba ganin haka yasa sai ya mika ma yara wayar duk dai korafin Umma yaushe zaki dawo ne? nace zan dawo kada su damu ina Tunanin har da shi ya Dinga matsa musu su ji yaushe zan dawo ni ko a raina nace ba yanzu ba,ko zan dawo .har ga Allah ba da niyyar zuwa Dutse nazo ba sai da Yaya Asiya ke min Tadi'n ba nisa fa daga kano to Dutse gidan Nana Fatima kamar almara sai ko nace zani na kirata na Fad'amata ta daka Tsalle da Ihu tace in na hau mota da nazo tashar Dutse na Kirata zata zo ta Daukeni nan da nan naji Kwadayin zuwa na yi ma Yaya Asiya karya da ta tsareni da tambayan shin an bar ni..?
Nace mata eh mana ya barni sai ta kyaleni mijinta yarakani na hau Mota ranar jumma'a gabana na fad'i hakan nan na Daure bayan na roki Allah ya yafe min na yi doguwar tafiya mijina bai sani ba, Sai ko gani a Dutse ina kiranta sai gata tazo ta Daukeni har tasha muka Rumgume juna.
Sai gani a kayattacen gidan Nana Fatima mijinta babba ne Aikinsa D'an sanda farin kaya ne,Ita da mijinta kamar zasu goyani yana Dawowa a gaba na suka rumgume juna yana da fara'a kamar ita yana ganina Tun kafin na gaishe shi yace"Sannu da zuwa Fa'in mu maraba da zuwa Dutse"
Ina mirmishi na amsa masa duk yadda zan baku labarin gidan Fatima da Ahalinta sun wuce haka,Ya'yanta Jalil da jidda tun saba dani kamar sun sanni daman gani da son yara, Daki guda Nana Fatima ta ware min kuma har ta Kira chan gida ta fesama su Abba zuwana. Ammi tace kafin na koma Nana Fatima ta rakani har kano na gaida Hajiyar su tace in sha Allahu zata kaini,gani nayi dai ban kyauta ba, ranar da na kwana na yini na kirasa na fad'amasa ina Dutse gidan Nana Fatima. kai tsaye yace"Kika tafi har Dutse baki fad'amin ba Fa'iza..?ai naga dai duk lalacewar aure sunansa aure"
Sai na kasa mgana nasan ban kyauta ba yasa nace"Kayi hakuri.."
Bai ce komai ba illah yaran da ya mika ma wayan muka yi mgana Duk sun damu da in dawo daman mun yi waya da Hafsah ta fad'amin Ahmad nata rigiman bana nan,sai na fara Tunanin komawa gida kwana hudu nayi a Dutse kamar kar in dawo,Nana Fatima macece mai kirki ita da mijinta sun fita dani naga gari sannan zama da fatima yasa na kara sanin ita mace mai Daraja ce sannan yar kwalliya ce.
A na gobe zamu tafi kano da ita ni dagachan zan wuce katsina take kara min mganar Zainab kai Tsaye nace"Ina da abokiyar zama ammh tana Abuja chan take zaune"
Cikin karin mamaki tace"kuma tana da ya'ya..?
Ina dariya nace"Sosai biyu har da cikin na uku ma"
Sai ta rausayar dakai tana fadin"meyasa ita tana Abuja ke kuma kina katsina..?
Ganin Nana Fatima ce akwai yarda Tsakanina da ita yasa na gayamata kadan daga abunda ya shafeni sai dai ban gayamata irin zaman da nayi da Ishaq da jinginar aurena dashi ba,sai dai na gayamata Dalilin da ya sa zainab ta zauna abuja ni ina katsina.
Cikin mamaki tace"Tab kuma tana zuwa gidan ki na katsina ki sauketa a Dakin ki..?
Ina Dariya nace"A'a dakin dai megidan"
Sai ta bude baki tana mamaki Dariya ta bani na kwashe da dariyan ina fadin"Rufe bakin Mana"
Sai ta rufe lokaci d'aya tana Fadin'"Lalle kina da karfin zuciya wlh bazaki kwanar min a shashe ba..Tabdijam"
Dariyan yadda take jinjina abun nake yi a raina nace don ma bataji ni ke Dawainiya da su ba da sai ta zageni,a kwana Hud'un da nayi da ita na kara sanin wasu abubuwa na kuma kara yarda kwalliya da ado na duka mata ne,ba na bambamcin Fata ko kyawun Fuska ba.
Na kuma kara sanin ko kana da kyau to ka kara da wanka sai kafi haka kyau gata dai mai kyau da ita ammh kwalliya da gyara bata rabo da shi har mgana nayi mata nace"Nana baki gajiya da kwalliya da gayu..?me zaki gyara ke da komai Allah ya baki mai kyau a jikin ki"
Dariya tamin kafin tace"Ko kana da kyau Fa'i ka kara da wankan sannan ki yi shuru kawai ba komai Allah ya bamu ba. muma duk barazana muke da kwalliya da gayun yana karamana kwarjini"
Kuma na yarda da mganarta,Domin naga gayu in da ake kiran gayu a wajenta tana fadin Ammi yar gayu ce sannan bata shiri da wanda bai son gayu,nace tabbas na shaida haka Sai naji nima ina so na fara gayun nan na shiga Sahun manyan mata Cikkaku.
Washegari Direban mijinta ya kaimu kano har gidan Yaya Asiya tare da ita muka dumguma zuwa gidan su Ammi,sun yi murna sosai sai nuna ni suke yi suna tambayan ita ce Fa'in Azizat mai turaran kamshi sai Nana Fatima ta gyada kai wasu daman mun Hadu Bikin Yaya Abdul'Ahad,Balle kuma daman Yaya Asiya ta zama yar gida,Duk yadda naso na wuce katsina a ranar bai samu ba saboda mun jima muna Hira a gidan su Ammi ita kanta Nana Fatima tayi yammh don dai motar gida ce.
Mun fito gidan su Ammi Nana Fatima ta nuna mana wani katon gidan Bene tana fadin"ina Engr din da zaku ji Abba na yawan mganarsa..?
Sai muka d'aga mata kai Saboda duk wanda yasan Abba yasan Labarin megidansa Engr.
Cikin Nuna mana gidan Nana Fatima tace"Ga gidan kakaninsa ta bangaran Uwa.nan aka haifi mahaifiyarsa dalilin makotansu da gidan su Ammi ma Suka hadu da Abba."
A tare da Yaya Asiya muka jinjina kai ina kallon gidan daga gani masu gidan suna da kudi sosai,irin kamar fasalin gidan da Abba ke ginawa a karofi sai dai wanchan ba gidan ba Bene ba ne.
Muna tsaye jikin motar da zata maida ta gida muke mganar Yaya Asiya ta ce"To ina masu gidan..?
Nana Fatima tace"Hajiya Tafisu ce mahaifiyar Hajiya Shukra ce kadai a gidan sai ya'yan yan"uwa Datake riko megidan ya rasu da jimawa daga ita sai yan aiki a cikin wannan gidan"
Na jinjina kai ina kara kallon gidan da akace mace d'aya ce aciki Nana Fatima ta cigaba da fadin"Shi Engr babansa bayarbene mutumin Beneu ne, Hajiya Shukra ce bahaushiya suna Abuja da zama. Sai dai dangin su kaf suna Beneu har kakansu tana chan da ciwo ya kamata ne ma ta koma hannun Hajiya Shukra,Engr kuma shi a Edo yake aiki"
Ni dai har gajiya nayi da labarin Engr Nana Fatima ko ta zage har Yaya Asiya na tambayan"Tab.To ya"yansa nawa..?
Nana Fatima tace"Tab. Bai da ya'ya fa, ya taba aure sau da'ya sati biyu matar ta kone da gas shikenen bai kara aure ba. kuma fa Abba ya girmesa, matashi ne sai dai yana da kirki sannan ya taka matsayi mai girma da kananun Shekarunsa"
Gani nayi sun bud'e hirarsa da Sauri na katsesu da fadin"Nana kada ki yi Dare"
Sai da nayi mgana ta farga Mukayi sallama Ta shige mota suka tafi,Dole na kara kwana gidan Yaya Asiya washegari motar asuba na hau sai katsina,Ance in mace mai ya'ya ta fi sati bata a gida sai abunda ta gani nima haka na tarar,kudin zobo da kunin aya sun ci ubansu,Hafsah sau Daya take yi a rana watarana ma in bata da Lokaci batayi,sannan kudin kuma suna tabaawa in zasu siya wani abu ,sannan yara wlh sun yi kewata ranar da na dawo yini Ahmad yayi Tsalle acikin gida,Shi kan shi Gogan bakinsa har kunne har da fadin"Mutanen kano da Dutse maraba"a Tsime na amsa masa nazo musu da Tsaraban Dutse da Nana Fatima ta bada a kawo masu,nafi kwana Biyu,gidana da kasuwancina bai Dawo daidai ba,Na yarda mace itace gida ranar da bata to sai kame kame har Mama tayi murnan Dawowata..
A satin kuma naje Karofi,Matar Yaya isa ta haihu naga ginin Abba an kusa gamawa a raina nace komai in da kudi an yi an gama,ammh duka duka yaushe aka fara ginin nan har an kusa gama shi..?ban kwana ba na dawo gida Hafsah chan na barta zatayi weekend,ina kuma Dawowa na iske wani sabon salo ban sani ba ko Mahaifin zainab ko ita wanda ya kirasa kan zainab zata baro aikinta ta biyo shi katsina ammh sai ta fara neman wani anan sannan zata zauna agidanta ne ita kad'ai in ya amince shi ko yace bai amince ba sai dai tazo mu zauna tare a wannan gidan.
Yana gayamin takaici ya kume ni na kallesa nace"To gidan da zata zauna wazai Dauki nauyin sa..?
Kai Tsaye yace"Daddy ne mana"
Nima kai tsayen nace"To meyasa bazaka barta ta zauna inda zata Sake ba.?Mganar gaskiya gidan nan yayi mana kad'an ban ga inda ita da yara zasu zauna ba abun kuma yayi yawa"
Hade rai yayi kafin yace"To wai haukatani zaku yi ne..?
Nace Haukatani zaku yi ne..?
To anan zata zauna nace"
Sai na bude ido kafin nace"Ba damuwa ta zo mu zauna din na d'an Lokaci ne, kowa zai san matasayinsa"
Mgana na gasa masa ammh bai gane ba,Ya gimtse bakinsa nima na kama kaina ina ji har Mama sai da tayi masa mgana tace gidan yayi mana kad'an ammh bai jita ba.
Har Anty Binta sai da mama ta kira ta shaida mata, itama fad'a ta hau yi masa na gidan ya yi mana kad'an,shi kuma yace ba ruwanta