Showing 1 words to 3000 words out of 133887 words

Chapter 1 - Auren Kwangila Book 2 & 3 Hausa Novel Complete

Takori   

12 Dec 2024

533

SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI


*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*

A yadda ransa yake a jagule din nan, ya san Muazatu ce kawai za ta iya tafiyar da damuwarsa, ga shi ya mata laifi, ya bata mata rai tun jiya yake ignoring call dinta. Tun kafin ya karasa dakinsa ya kira ta. Ya manna wayar a kunnensa ya murda kofar dakinsa, ya shige ya mayar ya rufe, har da murza key.
Kamar a mafarki Muazatu Rufai wadda ta fita hayyacinta cikin kwana biyu ta yi firgai-firgai saboda tashin hankalin da ta samu kanta a ciki, ta ga sunan Habeeb-qalby da ta sanya wa Abdulazeez Dakata na yawo a screen din wayarta. Sai ta dauka gizo ne idanunta ke mata kamar yadda suke mata tun jiya, don haka har kiran ya kare bata taba wayar ba, sai ma wasu azababbun hawaye masu dan banzan yaji da ta ji sun kwaranyo mata. A karo na biyu wayar ta ci gaba da ba da ruri da Habeeb-qalby, ta kai hannunta ta damke gashin kanta tana ta cije labbanta na kasa da hakoranta tana rokon Allah in mafarki ta ke ta farka.
A nasa bangaren Abdulazeez jikinsa ne ya yi sanyi, ya tabbatar bai kyauta wa masoyiyarsa ba, kamar wani wanda ya yi auren soyayya da zai janye jiki daga gare ta don kawai an kawo masa amrya? To me ye gaminsa da amaryar da ya janye wa Muazatu dominta? Wata zuciyar ta ce da shi, Ba don amarya ba ne, kalamin bakinta ne. Ba ta iya magana ba. Ba ya so kowa ya shiga (personal life) dinshi hatta iyayensa haka Allah ya halicce shi, don haka yake kara kyamatar wannan auren, don a ganinsa Mammah ta shiga rayuwarsa da yawa ta rushe masa future ta hanyar aura masa yarinyar da ba ta yi daidai da tsarin rayuwarsa ba. Zai kuma bi duk hanyar da zai bi ya gyara rayuwarsa yadda ya riga ya tsara tun lokacin da ya mallaki hankalin kansa. Ya yi fushi da Muazatu amma ya huce, ya kuma kara tabbatarwa kansa ba zai iya rayuwa ba tare da ita ba, dole ya lallashe ta.
Ki yi hakuri Muazatu.
Abin da ya rubutakenan ya tura mata.
Muazatu ta karanta abin da Abdulazeez ya turo mata. Lumshe idanunta ta yi, wata rahma ta sauka a zuciyarta. Kalaman (are short, yet they mean alot to her) girmansu ya yi na ruwan kogi ya wanke zuciyarta. Duk da haka ba ta mayar da amsa ba, ba ta kuma kira shi ba sai da ya kara ragaita. Ya turo mata sako na biyu.
Muazatu please, Im sorry.
Sannan ya sake kira.
Wannan karon ta amsa kiran, amma maimakon ta ce komai, kuka ta sanya masa. Kyale ta ya yi ta yi har ta gaji. Ta share hawayenta sannan ta ce,
Na huce.
Murmushi ya yi, ya gyara kwanciyarsa cikin niimtaccen gadonsa, ya ja quilt ya rufe rabin jikinsa, ya canza rikon wayar daga dama zuwa hagu.
So soon haka?
Murmushi ta yi kamar yana ganinta.
Tunda ka san ka yi min laifin, ka kuma amsa ka yi, ci gaba da fushin nawa na mene ne?
Au, ni ba ki san kin yi min laifi ba? Ki dubi tsabar idona ki ce wai.....
In ana sulhu ba a tone-tone. Ta katse shi.
Ki yarda to ba ni kadai na yi laifi ba, dukkanmu mun yi wa juna. Muazatu bana son raini, ko da aure tsakaninmu bai kamata ki ce min kada in kusanci matata ba. Ina ruwanki? This is my personal world, mind your own business. Im sorry once again for not picking your calls. In na ce ban yi kewarki ba na yi babbar karya. I love you Muazatu, you are the goal I want to achieve now, believe me or not.
Wata doguwar ajiyar zuciya Muazatu ta sauke, duk da kalamansa na farko sun yi radadi a zuciyarta, to na karshen sun wanke radadin. Haka yake, haka Allah ya halicce shi, ba ya boye gaskiyar abin da ke zuciyarsa don ya faranta maka, ba ya karya don a so shi, in za ka so shi ka so shi a yadda ka same shi. Ta dade da fahimtar hakan.
Im sorry too...
...and I love you more...
Dariya ta saki har da wata irin shesshekar shauki. Suka ci gaba da hirarsu yadda suka saba, amma ta yau ta fi ta kullum gardi.
Bayan fitarsa da rufo kofarsa Hafsat tasowa ta yi ta dauki ledojin da ya aje ya fice ta bude. Sunkin gasassun kaji ne suyar (YAHUZA) da juice da fresh milk da daurin (shawarma) har guda biyar. Harira ta yi sallama ta yi mata izinin shigowa. Ta aje mata abincin da ta dafo (express). Cikin sanyin muryarta ta ce da ita,
Ga shi kuma ya sayo da baki dafa ba.
Ba komai, gobe sai in dumama in ci.
Ta mika mata leda daya ta karba, ta yi godiya ta dau abincin da ta kawo ta fita tana fadin,
Allah ya tashe mu lafiya, in kin ci ki sha magungunan naki.
Hafsat ta ce, Insha Allah. Ta fita ta rufo mata kofar.
Zama ta yi a tsakar dakinta ta ci kazar nan ta koshi, ta sha magani sannan ta yi sallolin nafila kamar yadda ta saba. Ta sanya kayan barci masu laushi, ta yi addua ta kashe wuta mai haske, ta bar dim-lightta kwanta.
Asuba ta gari Hafsat-Suhaana.

******
Washegari da safe bayan ta yi sallar asubah ta yi wanka. Ta shirya tsaf cikin wata lallausar atamfar (holland) koriya shar, ta yi daurin kai sosai ya zauna mata a kai cif-cif gwanin ban shaawa. Dressing din da bai dameta ba amma Mammah tace dole ta dinga yin shi yanzu ta rage zama da dogayen rigunan nan nata, ta feshe jikinta da turaruka masu kamshi, wadanda Mammah ta cika mata gaban madubi da su. Ta zura kyawawan kafafunta cikin (flat shoe light green) samfurin polota fito falo.
Motsin Harira ta ji a inda ta fahimci kitchen ne, sai ta bi ta can. Daga bakin kofa ta tsaya tana dan murmushi,
Anty Harira ina kwana, mun tashi lafiya?
Harira ta saki dariya jin an kira ta da Aunty, ta juyo, Lafiya kalau Hansatu, ya karfin jikin?
Na warware, ba inda ke min ciwo.
Haka ake so, na kammala abincin kari ina zanik-kai muku?
Me ya sa ba ki jira ni na zo mun yi tare ba? Jiya ma haka ki ki yi girki ke kadai.
Murmushi Harira ta yi, a ranta ta ce, Mene ne amfanina?
A fili kuma ta ce, Kina fama da rashin lafiya zanis-sa ki aiki Hansatu?
To na warke. Yanzu tare za mu dinga yi, ki yi shara, wanke-wanke da sauran ayyuka, ki bar min girki.
Shi kenan Hansatu, tunda haka kinka bida. Zo ki gani, ashe gidan cike yake da kayan abinci, firinji cikke da nama da kihi har da markadadden kayan miya bokiti guda.
Hafsat ta idasa shiga kicin din suna dubawa tana sanya wa Mammah albarka cikin zuciyarta. Ita ta kwashe tangarayen da harira ta zuba soyayyen dankali da Agada (plaintain) da farfesun kayan ciki ta kai kan kyakkyawan dining table wanda aka yi wa muhalli a can wata kusurwa ta falon. Ta dawo ta dauki flask din shayi da tea cupsda kayan hadin shayin duka ta jera su a diningta samu wuri a daya daga jerin kujerun falon ta zauna.
T.V ta ke son kunnawa, ba ta san ya za ta jona ta ba, sai ga shi ya fito rike da gown dinshi a hannu (bakar rigar lauyoyi) da wiga kansa (hular lauyoyi) yana tsuke tie din wuyansa. Gabadaya falon ya gauraye da kamshinmasculineturarensa (Creed Aventus) har Hafsat ta ji turaren jikinta ba kamshi yake ba. Kafafunsa cikin (black covers) kirar Italy yana takun nan nasa gab-gab-gab shi ba sauri ba, shi ba tafiya a hankali ba. Idanu suka hada sosai, dukkansu sai suka dauke kai cikin koinkula. Ita ta fara dauke idonta ta mayar wani gefen, wata hudubar Mammah ta fado mata tun tana karama, Duk inda ki ka ga babba ki gaishe shi ko da da shekara ya girme miki. Sakamakon hakan sai ta samu kanta da zamowa daga cikin kujerar da ta ke zaune cikin nutsuwa bakinta ya ambato kalmar, Sabahul khair. Da accentdinta mai taushi.
Barrister Abdulazeez Dakata ya mirgina kai ya amsa a ginshire, Lafiya lau.
Ya ci gaba da tafiya a falon zai fice. Hafsat ta samu kanta da cewa, Ga abincin karin kumallo. Cikin harshenta na Brussels. Sai bayan ta fada ta shiga cikin nadama da juyayin wa ya aike ta? Bai ce ta shiga rayuwarsa ba a rayuwar auren da ya shirya musu. Amma ga mamakinta sai ya ba ta amsa da turanci, don shi ba wai ya kware a yaren nasu ba ne, amma yana ji.
Na makara, amma a sanya a basket a sa min a mota.
Cikin nutsuwa ta mike ta shiga madafin ta dauko (food-basket) sabo fil ta dauko kanan food flasksmasu kyau ta fito ta juye kowanne a flask daya. Ta dauki filas din ruwan zafi zata saka cikin basket din sai ya ce, Bar wannan, inada kettle ina shan (coffee) a office.
Kanta a kasa ta ce, Toh.Ya fice, ta bi bayansa tana dauke da kwandon.
A jikin kofar motar ta tsaya ya bude ya shiga, sannan ya mika hannu ya bude (lock) din kujerar baya ta sanya basket din. Sai ya ce mata,
Thank you.
Ya rufo kofar.
Juyawa ta yi ta koma, shi kuma ya murza kan motarsa kirar (GMC) ya yi reverse Danfulani ya bude masa kofa ya fice.
Kicin ta leka ta tadda Harira a dining din kicin din tana karyawa, ta gyare koina tsaf.
Sannu da aiki Anty Harira, ki dinga zuba wa maigadan gidan nan abinci don Allah.
Harira ta ce, Ba sai kin fada ba, na ba shi tun dazu.
Ta ce, Ok.
Falo ta koma wajen kayan wuta ta yi ta kokari har ta jona T.V ta zauna da remote a hannunta, har ta nemo wata tashar Larabawa suna girke-girken kasar Turkiya da yadda ake sarrafa su. Sosai abin ya dauki hankalinta. Sai ta ji shaawar gwada abin da suke koyarwa don haka ta shiga dakinta ta samo jotter da biro ta soma (jotting-down) daki-daki yadda za ta gane. Wani irin tsire suke nuna yadda ake yi na nikakken nama mai suna adana kebabi da recipe din, a zuciyarta tana fadin ta samu abin yi za ta gwada su ci ita da Anty Harira.
Sai wajen sha daya na safe ta kashe T.Vn ta leka kicin, Harira ba ta nan ta wuce dakinta. Nan ta hau hada kayan girkin da za ta bukata.
Kafin karfe biyu na rana gidan ya gauraye da niimtaccen kamshin tsiren mutanen Turkiya. Ta kwashe shi daga oven ta zauna a nan dining din cikin kicin tana ci. Bayan ta dibarwa Harira.
Kwana biyu ta sake yi don na farko yayi mata dadi,Harira ma wuni tayi tana santin tsiren, tana zaune a kicin tanaci tana tunani. Tunda ta zo yau kwana biyu ba ta yi magana da Mammah da su Ismaeel ba, sosai ta ke cikin kewarsu. Ga shi ba ta da waya, ko sanda ta ke gida ba ta rike waya ko da wa za ta yi magana da wayar Mammah ta ke yi. Tana wannan tunanin tana kai lomar adana kebab dinta ba ta ankara ba sai ganin giftawar mutum ta yi har ta so ta tsorata. Da sauri ta waiwaya, Abdulazeez ne.
Kai tsaye ya wuce ga firji ya bude ya dauko gorar ruwan Faromai sanyi ya bincire murfin ya kafa a bakinsa ya ringa kwankwada, sanyi da gardin ruwan na ratsawa har cikin kwakwalwarsa yana wanke gajiya da zafin da kwakwalwar ta kwaso. Ta dauke kai daga kallonsa yayin da ta sauke wata siririyar ajiyar zuciya, ina ma za ta iya? Da ta roke shi ya ara mata wayarsa ta kira Mammah da Baba Azumi da Yayanta Ismael Dakata mazaunin kasar Amurka ko ta ji dadin zuciyarta daga matsewar da ta yi mata wuri guda sabida kewarsu.
Wannan aure jinsa ta ke tamkar an kawo ta kurkuku, ya yanke alakarta da kowa nata, Mamanta ba ta kara bi ta kanta ba, miji kamar malaika kullum fuska babu walwala, in yasa kafa ya fice sai goshin maghriba yake shigowa gidan daga nan bata karaganinsa sai wayewar gari in ya fito don tafiya office, in sun bashi abinci yana karba, in ta gaishe shi zai amsa, bayan wannan ba wata kalma dake kara hadasu, da alama ba ya son bude ido ya ga fuskarta, watakila bayan rashin so ita mummuna ce. Ita ma ba so ta ke ya so ta ba, amma akalla ya bude kofar da aurensa ya rufe mata na datse alaka tsakaninta da kowa nata.
Ji ta yi idanunta sun cicciko da kwalla kafin ta yi aune kwallar ta zubo, sharr! Da sauri ta sa bayan hannunta tana sharewa. Har ya wuce ya bar kicin din yana mamakin me ya yi mata ya sanya ta kuka? Daga kawai ya shigo kitchen? Watakila ba ta son ganinsa ne, in ba haka ba shi bai ga laifin da ya yi mata ba. Alkawururrukan da ya daukar mata tun a yau har ya fara kokarin cika su.
Ci gaba ta yi da cin abincinta tana hawaye, a haka Harira ta cimmata. Wai Abdulazeez ya ce a sanya mishi abinci a mota zai koma ofis. Nuna mata inda ta zuba masa abincin ta yi da hannunta, har tsiren ta zuba masa mai yawa, ba ta so ta yi magana Harira ta gane kuka ta ke yi. Ta manta cewa gaba take da ita. Murmushi Harira ta yi, ta ce.
Ki kai masa da kanki Hansatu, ki yi hakuri kin ji?
Wannan Hansatun da Harira ke kiranta da shi dariya yake bata, amma yau haushi ya ba ta. Ba ta ce komai ba ta mike ta dauki basket din ta fita.
Yana cikin motar har ya kunnata ya rufe kofar da alama ita yake jira, ba ta yi masa magana ba ta bude kujerar gaba ta ajiye kwandon ta rufe kofar. Ya ja motarsa da hanzari ya bar harabar gidan, daman mantuwa ya yi ya dawo, amma ba aladarsa ba ce dawowa gida cin abincin rana ba. Abin da ya tarar tana ci ne ya ba shi shaawa har ya ce a ba shi abincin.
Rayuwar amarya Hafsat-Suhaana da Abdulazeez kenan a gidan aurensu har tsayin sati biyu. Za ta yi girki sau uku a rana, kuma babu wanda ba ya ci, na safe zai fita da shi, na rana da ba ya samun sukunin dawowa zai turo direban ofishinsu ya daukar masa, na dare kuma in ya dawo masallacin unguwarsu sallar ishai zai ganshi a diningya zauna ya ci. Weakness dinsa kenan (abinci) kuma da a ce Hafsat na da wayo da ta dade da gane hakan. Ba ya son abincin sayarwa sai ta kama dole. Sanda yake (schooling) shi yake dafawa kansa. Da ya tafi Law-school daga gidansu Muazatu ake ba shi. Da ya gama ya dawo gida mahaifiyarshi ta sangarce shi da dadadan girke-girkenta wadanda dandanonsu yanzu ya yi masa daidai da wanda Addarta ke ba shi, wanda ke nuna ko dai ta koya ne a wajenta, ko kuma tare suke yi.
Kallon farko da yake yi mata na sangartacciya, ya soma gogewa.SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870

*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*



Sanin cewa Mammah na jiransa a gida ya sa ya ki shiga gidan da wuri. Bayan rabuwarsa da Muazatu ya tuko mota a hankali kamar wanda kwai ya fashewa a ciki, ya taho gida. Da ya zo kofar gidan bai karaso ba ya kashe motar daga nesa, ya kifa kai a kan sitiyarin motar ya rufe idonsa. A wannan dan lokacin ya tsara komai, ya tsara kalaman da zai yi wa Suhaana amfani da su. Ya yayyafa wa zuciyarsa ruwan sanyi a kan ta rage tsanar yarinyar, ta sake da ita yadda za ta fahimci duk abin da yake nufi. A kananan shekarunta yana da tabbacin shawo kanta ta yarda da tsarinsa ba zai yi masa wuya ba.
Sai da ya tabbatar ya shirya kalaman a kan harshensa ya yi bitarsu sun zauna sosai, sannan ya tashi motar a hankali ya karasa gida.
Mammah da ke dokon shigowarsa tana jin sanda maigadi ya bude masa get ya shigo ya adana motar a mazauninta. Ya tattaro wayoyinsa da brief-case hadi da kamfutar laptop ya fito. Yana rataye da falmaran din bakar suit din jikinsa a kafadunsa. Bai yi tsammanin ganinta a falon ba, don ya san karfe tara ta ke shiga barci, yanzu kuma tara har da rabi.
Ya sanya a ransa Baba Azumi zai sa ta yi masa magana da Addar, don haka ya shigo kansa tsaye.
Ta cika ta yi fam a kan kushin din falon, ya ja ya yi turus! Da suka hada ido, ta sassauta fushin da ke kan fuskarta, cikin sanyin murya ta ce, Na dauka ba ka kai wa magriba a waje in ba da wani muhimmin case a hannunka ba?
Ya nisa a hankali, Yi hakuri Mammah wallahi baki na yi suka tsayar da ni, sai yanzun na samu kaina.
Ta so ta ce da shi, Baki ko budurwar banzarka? Ta ga cewa shiga personal-lifedinshi ba girmanta ba ne, sai kawai ta mike ta nufi hanyar turakar maigidanta tana fadin,
Ka je study room Addar za ta zo yanzu.
A ransa ya ce, Ai a bari na ajiye kayan hannuna, na ba wa cikina hakkinsa, na dan yi freshen up kada ta ganni a jigace haka ta san cewa ta shigo rayuwata, ta takura ta da yawa.
Ita dai Mamma ta yi wucewarta, shi kuma ya nufi dakinsa.
Sai da ya gama duk abin da zai yi, ya yi wanka ya shirya cikin T. Shirt mara nauyi (black colour), an yi rubutu da farin fenti dara-dara (ARMANI). Ya hada da bakin wandon (jeans), ya taje sumar kansa, ya feshe jikinsa da turaren Eternity Moment.Zuciyarsa ma na hango masa EternityMoment dinsa da Muazatu kamar yau ne, in har yarinyar nan ta yarda su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login