Showing 39001 words to 42000 words out of 133887 words
wayarta ta dauka ta yi gaba. Ya bi bayanta.
Sai da ya rufe koina na gidan ya kashe wuta da kayan wuta, sannan ya same ta a dakin. Ta jefa filo a kan resting chair ta yi kwanciyarta ta rufa da zanin atamfarta. Yana shigowa ya ce,
Me ya yi zafi na kwana a kujera Hansatuwa Addar Mammanta? Na yarda a yi kwanciyar kai da kafa.
Tashi ta yi tana murmushi jin sunan da ya kira ta da shi, Ka yi alkawari?
Alkawarin me?
Ba za ka canza position din kwanciyar ba.
Na yi alkawari Hafsat, amma in kafata ta tsokale miki ido ba ruwana.
Kana juye-juye ne in kana barci?
Juye-juye kai! Har da mirgine-mirgine.
To ni zan je karshen gado, kai kuma ka zauna a farko, kuma still kai da kafa.
In aka yi hakan bargon ba zai ishe mu ba.
Dauko wani, kowa ya rufa da guda daya.
Ya marairaice fuska, Ga shi kuma guda daya ne Babana ya sai min, ke ce Mammanki ta saya miki da yawa.
To bari in je in dauko nawa.
Ok, go.
Ta mike ta nufi kofa ta murda ta fita. Da dan banzan gudu ta dawo ganin wani uban duhu. Gabadaya fitilun gidan ya kashe bai bar ko guda daya ba. Dariya sosai Abdulazeez yake yi. Ya mike ya isa ga dan firjinsa, madarar oldenburger fresh milk ya zubo a kofi ya kawo mata. Zama ta yi a gefen gadon tana ta fushin dariyar da yake mata.
Mika mata ya yi, Karbi ki sha, ba kyau kwana da yunwa, daga ni har ke ba mu yi dinner ba.
Ba musu ta karba ta kwankwade, ya kara mata ta shanye ta ba shi kofin ta haye can karshen gadon ta nufa da zanin atamfarta. Zama ya yi a farkon gadon yana shan madarar a hankali.
Dauki duvet din ki rufa ke daya na bar miki.
Ta kuwa janye ta kudundune a cikinsa. Shi ina zai iya rufa da wani quiltbayan zai kwana cikin zafi babu AC sabida ita? Dama tsokanar ta yakeyi. Sai da ya gama abin da zai yi, ya yi addua, sannan ya yi (light off) ya kwanta.
Shi ya tashe ta da asubah suka yi sallah tare. Cikin sauri ya yi wanka ya shirya cikin farar shaddah kal yar ciki da babban riga, ya kafa hula zanna-bukar ya daura agogon rolex a damtsen hannunsa duk Hafsat na kallonsa. Lokar jikin gadonsa ya janyo ya dauko wani tsohon envelope da yake ta boyonsa ya sa a aljihunsa.
Turare ya dauka yana fesawa sai ganin Hafsat ya yi a gabansa, ta mika hannu ta karbi turaren daga hannunsa ta shiga fesa mashi. Daga shi har ita murmushi suka kama yi, wanda ba su san dalilinsa ba. Sai da ya rike hannunta mai turaren don ya yi masa yawa. Kallon juna suka yi na yan sakanni kafin Hafsat ta sunkuyar da kanta. Horn din mota suka ji diiiit-diiit! daga bakin gate Sagir na jira. Da sauri ya saki hannun Hafsat ya sumbaci goshinta ya juya da sauri ya fita.
Shafo wajen ta yi, ta sa wa yatsun ido tana kallo. Ba ta san dalilin murmushinta ba. A fili ta ke yi musu adduar dawowa lafiya. Gadon Abdulazeez ta koma ta haye ta yi kwanciyarta tare da nannadewa cikin duvet dinsa wadanda ba sa komai sai tashin kamshinsa.
A yinin ranar bakidaya kasa tsinana komai ta yi, kewarsa ta ke yadda harshenta ba zai iya bayyanawa ba.
*****
To fah! Ga AUREN KWANGILA ya dauko wani sabon salo, ko yaya zaa kare??? Ni kaina ban sani ba!!!
Nayi muku alkawarin cigaban bazai jima ba.
SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870
*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*
*****
A falo ya tadda Hafsat, ta yi daidai da takardu irin na zane manya-manyan nan tana zana World Atlas. Wani assignment ne na cikin hutu (holiday assignment) aka basu akan wani kwas map analysis. Zane ta ke yi na kwallon duniya world map ta maida hankalinta kacokam kan abinda ta ke yi. Idan ka kalle ta a zuciyar ka abinda zaka fara cewa shine; (A Geographer withdetermination and enthusiasm). Ko shigowar motarsa ba ta ji ba balle takun sawunsa. Tsayawa ya yi a bakin kofar shigowa falon ya jingina da kofar hannunshi na hagu na dogare da kofar dayan na cikin aljihun wandonsa. Langabar da kansa ya yi gefe yana kallonta. Watanni goma sha biyar kenan cif da aurensu, wanda ya yi daidai da SHEKARA DAYA da watanni uku.
Abubuwa da yawa sun faru cikin wadannan watanni goma sha biyar din wadanda ba za su taba shafewa daga kwakwalwarsa ba! Masu dadi da marassa dadi, na ban dariya dana ban haushi. A cikin wadannan watanni, Muazatu ta gama LLB tayi karatu a Law-school ta gama ta fito a matsayin cikakkiyar lauya daidai da burinsa na matar da zai aura.
Ya zauna da Hafsat-Suhaana cikin wadannan watanni zama wanda aka tsara yadda zai kasance tun farko, amma abin mamaki ya rikide ya jirkice zuwa ba yadda aka tsara shi ba. Ya zo da abubuwa masu yawa beyond his mere or casual assumption......
Awata rana irin ta yau daidai wannan lokacin yana rungume da Muazatu a ofis dinsa yana daukar mata alkawurran da baa so musulmi ya dauka saboda ba shi ke iko da rayuwarsa ba. Gabadaya rayuwarmu rubutacciya ce tun haihuwarmu a Allon Lauhul-Mahfuz. Manzon Rahma (S.A.W) ya ce, yana daga cikin alamomin munafuki in ya yi alkawari sai ya saba, in aka amince masa sai ya yi hainci, idan ya yi zance sai ya yi karya (Bukhari).
Ya yi wa Muazatu alkawari, in ya saba sunansa MUNAFIKI. Ya yi wa Muazatu zance tun daga karkashin zuciyarsa, in ya canza shi ya yi KARYA. Muazatu ta amince masa, in ya zabi Hafsat ya barta ya yi HAINCI. Ta rabu da kowanne Da namiji saboda shi. Shekaru ukku kenan cif tana dakon soyayyarsa mai wahala a zuci. Lokaci ya zo da zai aiwatar da kalaman bakinsa yana so ko ba ya so. To amma anya babu babban kuskure a cikin alamarin nan? Yaya rayuwar Hafsat za ta kasance in ya rabu da ita? Karatunta zai dore? Mammah za ta barta ta ci gaba da makaranta babu aure? Zuciyarsa wadda har yau ba ta baiwa Hafsat matsugunni guda daya a cikinta ba ta ce da shi.
Tun farko ba ka yi wa Hafsat alkawarin rayuwa mai dorewa da ita ba, kuma ta san wannan. Abu daya ka ke yi wa shi ne SABO! Ba mutuwa ake yi wa kuka ba sabo ne, da sannu zai gushe tamkar ba a yi shi ba. Babu mai mara maka baya ka auri Muazatu kana tare da Hafsat. Matsayin da Hafsat ke da shi babu soyayyah sai emotion. Wani irin emotion na can karkashin zuciya. Wanda a kullum yake da nauyi kamar ansababban dutse an danne shi. Zuciya mugun nama.. ta ci gaba da angiza shi da cewa... Muazatu na jiranka Abdulazeez da tarin soyayyah mara algus..... za ku shimfida rayuwa mai maana irin wadda ka ke buri..... soyayyah irin wadda ka ke mafarki... yadda ta yi maka tanadin kanta tsawon shekarun nan ta tsayar da soyayyarta a kanka kai kadai, ta cancanci ka watsar da komai ka cika alkawarin da ka daukar mata... sai ka rabu da Hafsat ne za su dubi alamarinka da Muazatu da idanun basira.
Hafsat duk wasu alkawururruka da ka daukar mata a yau Allah ya nufa ka cika mata su. Abu daya ya rage ka damka ta a hannun MAHAIFINTA, wanda in Allah ya so Ya yarda wannan ya zama tarihi. Zuciyar ta ci gaba da qawata masa komai na Muazatu ya fi na Hafsat sau dubun dubata. Hafsat har gobe kamata ya yi a ce tana gaban iyayenta suna ci gaba da rainonta... yadda ka shirya rayuwa da matarka ta aure da tarin bukatar gangar jiki da zuciya,me Hafsat za ta iya dauka a ciki? Wane martanin soyayya kake tunanin samu daga gare ta? Muazatun dai! Ita ce daidai da rayuwarka, wadda za ta zage ta nuna maka soyayya dakwanji, da jiki da zuciya.
Haka zuciyarsa ta yi ta kawo wahayi iri-iri na kyakkyawar rayuwar da zai shimfida da Muazatu in ya same ta. Bangaren kyakkyawan tunani ya toshe, idan ma akwai, to son cika alkawarin da ya dauka ya rinjayi komai... A ganinsa in ya cika wannan alkawarin ne zai kubuta daga sahun munafukai, makaryata, mahaintakuma rayuwarsa ta zauna lafiya.
Duk sanda zuciyarsa ta kawo masalaha ga rayuwar ita Hafsat din, daya zuciyar sai ta hambare. Da hujjarta na cewa, ita yar gata ce yanzu... mai iyaye, yan uwa da kakanni babu abin da zai dame ta don ta rabu da kai... Mammah kuwa in za ta yi adalci ai ka yi mata biyayya, lokaci ya zo da za ta karbi naka zabin ta ba ka yancin da Ubangiji ya ce ta baka. A zaman da ka yi da yarta ba ka taba cutar da ita ba... ba ka taba bata mata ba sai ko bisa ajizanci irin na dan adam, ko ka yi kuskuren ma kana kokarin gano kuskurenka da kanka ka yi repenting. Idan ba a gode maka ba a rikon da ka yi wa Hafsat, to a kalla ba za a yi maka tofin Allah tsine ba......!!!
Da wannan kwarin gwiwar Abdulazeez Hamza Atiku ya dauke ido daga kallon Hafsat, ya karasa shiga cikin falon. A lokacin ne Hafsat ta ankara da shigowarsa. Wani irin dadi ta ji a ranta domin sosai ta yi kewarsa a gidan tun fitarsa. Rashin abin yi ne ya sanya ta yin assignment din kuma map din ya yi kyau sosai kamar ba ita ta yi ba. Ga mamakinsa ya kasa hada ido da Suhaanah a yau, kai tsaye ya nufi dakinsa ba tare da ya ce da ita komai ba.
Hafsat ta yi dan jimm! Me ke damun Yayanta Abdulazeez? Ko wani ne ya bato masa rai a waje? Mikewa ta yi da niyyar binshi dakin, amma sai ta dakata. Sun dade da daina shiga dakin junansu. Sannan a lokacin da miji yake cikin fushi matarsa nesa-nesa ya kamata ta yi da shi. Damuwarta shi ne, ta shirya masa abinci mai rai da motsi da za ta so ya ci kafin ya shiga barci. Amma haka ta hakura ta soma tattara kayan zanenta don barin wajen.
A wannan daren mai cike da rudani ga Abdulazeez Dakata daga shi har Hafsat kowanne ya kasa barci. Cikin sulusin dare ya samu takarda ya yi rubutu ya ninke ya adana a lokar gefen gadonsa. Wata irin ajiyar zuciya ya saki ya maida kansa ya jingina a kan filo. Amma ga mamakinsa ya kasa runtsawa. Ya rasa takamaiman abu guda da kwakwalwarsa za ta kama, gabadaya ta hargitse, ta cukwikwiye, duk kuwa da ya yanke hukuncin da zuciyarsa ta fi amincewa da shi din. Kamata yayi ace ya samu (peace of mind) bayan zartas da hukuncin amma kamar ya kara hargitsa kwakwalwar sa fiye da baya.
Hafsat kuma damuwarta me ke damun Abdulazeez ne? Ba ta taba ganinsa cikin wannan yanayin ba. Ko ba ya jin yin magana zai gaya mata ba ya son magana ta yi harkarta ta kyale shi. Amma a yau ko alfarmar hakan ta kasa samu balle ta ga kwayar idanunsa. Ga shi da alama yana cikin rudani irin wanda ba ta taba ganinsa a ciki ba. Ta samu kanta da mikewa ta dauro alwala ta dasa sallar nafila cikin daren. Addua ta ke ko mene ne matsalar Abdulazeez Allah Ya ba shi kyakkyawar mafita, Ya iya masa abin da ba zai iya ba, Ya shige masa a gaba a kan alamuransa (Allah sarki Hafsat).
******
Wani barci ne mai nauyi ya sure ta gabanin asubahi, bayan ta idar da sallar asubah. Ba ita ta farka ba sai wayewar gari tangararan. Lokacin tuni Abdulazeez ya tsufa a office. Takaicin kanta ne mai tsanani ya kamata. Haka ta mike ta yi wanka ta shiga kicin don sama wa cikinta abin da zai ci.
Abdulazeez bai dawo gidan ba har ta yi shirin barci, gidansu ya tafi a can ya ci abinci. Hatta Mammah ta lura cikin damuwa yake, amma da bai furta ba sai ta kyale shi. Yana gidan har karfe goma, Mammah ke tambayarsa ko ya gaya wa Hafsat maganar tafiyarsu Yola? Ya ce, abubuwa sun masa yawa, ya manta. Amma da ya koma zai gaya mata. Fada sosai Mammah ta hau yi masa na ba ya daukan abubuwan kowa da muhimmanci sai nasa. Hakuri ya ba ta ya kuma tabbatar mata yau zai gaya mata.
Da ya dawo ta dade da shigewa daki ta kashe wuta ta kwanta. Ko ta yi barci ko ba ta yi ba, ba zai iya cewa ba. Text ya yi mata a ciki ya ce ta shirya kayanta da na bukata wanda zai yi mata sati biyu za su tafi jihar Adamawa jibi dukkansu, har su Mammah.
Washegari tana kunna waya abin da ta fara gani kenan. Sai kawai ta ji gabanta ya fadi, me za su je yo wa a Yola? Wa suka sani a can? Har kuma sati biyu? Allah ya so ta hutunsu na sati hudu ne. A hakan dai cike da zullumi ta soma shiri tun a lokacin.
Karin kumallo mai kyau ta shirya ma Abdulazeez a safiyar ranar. Amma sai tsintar bude masa get da fitarsa ta yi tun kafin lokacin da ya saba tafiya office ya yi. Jikinta ya kara yin sanyi fiye da yadda yake a mace tun daren jiya. Haka ta kare wunin sukuku tana shirya kayanta cikin travelling bag.
Haka ya yi ta zillewa haduwarsu har zuwa ranar tafiya. Ba su hadu ba sai asubahin ranar da ya fito cikin shiri da nashi jakar kayan marasa yawa. A falo ya same ta a shirye don kusan kwanan zaune ta yi saboda zuciyarta ta kasa sukuni balle ta yi barci. Jikinta ne kawai yake ba ta canjin Abdulazeez yana da nasaba da wannan tafiyar.Ya kalle ta kasa-kasa yace ta koma daki ta canza mayafi wannan yayi shara-shara, nan ta ajiye hand-bagdinta ta koma dakin don bin umarninsa. Mamaki fal ranta don ita bata ga laifin mayafin data yafa ba, yanada kauri ba laifi kuma yanada girma, ita data fi amfani da abaya ma da dan mayafinsu bai taba cewa komai ba sai yau akan babban gyale. Tunda suka shiga mota ta gaishe shi, ya amsa bai kara ce mata komai ba. Nauyin da zuciyarsa ta yi kawai ya ishe shi.
A Asokoro ma ba su bata lokaci ba kowa a shirye yake. A motoci za su yi tafiyar. Manyan jifa-jifai uku na Dr. Hamza, sun biya sun dauki Uncle Abdulkarim da yaransa, za su tsaya a Kano su dauki su Adda Hafsatu don Anty Zuwaira ta ce ita kam ba za ta samu zuwa ba. Sanin halinta mijin bai takura ta ba.
Wajejen karfe sha daya na rana suna cikin Kano. Babu bata lokaci su Adda ma sun shirya su kawai ake jira su iso. Motar farko Abdulazeez ke ja, Hafsat da Mammah, Baba Azumi da Adda Hafsatu da Daddy ne a ciki, ta biyu Baffa Atiku, Dr. Idris Dakata, matarsa Dr. Tawheedah, matar Ibrahimada Minister Abdulkareem da dansa Ramadan ne a ciki, Ibrahima ke jan su, ta karshe su Aunty Luba, Murja, Mariya, Furerah, Usman da Haleem dasu Farhan, direban Daddy Salisu ke janye da ita suka kama hanyar Adamawa. Daddy ya ce, ba za su daura musu nauyi ba, Hotel zai kama musu gabadaya in sun isa.
Ana ta hirarraki a motar banda Hafsat da Abdulazeez, wanda ke tuki cikin nutsuwa da kwarewar tuki. Daddy ne a gefensa, a kujerar baya ta farko ita da Mammah ne, a ta biyu Baba Azumi da Adda Hafsatu. Hafsat kwantar da kanta ta yi a kujerar gabanta tun tana tunane-tunane har ta rasa na kamawa, barcin da ta ci bashinsa ya yi awon gaba da ita. In lokacin sallah ya yi suna tsayawa a gidan mai su yi sallah su ci abincin da Mammah ta yo musu guzuri sannan su ci gaba.
Akai-akai suna waya shi da Sagir har Allah ya kai su Jimeta lafiya, misalin goma na dare. Don haka ya gaya wa Sagir ba za su samu shigowa a daren ba sai gobe da safe sun wuce masauki. Sagir ya yi korafin cewa, don me ba za su karaso su sauka gidansu ba? Ya ce, suna da yyawa ne, sannan shi ma ba tsarinsa ba ne tsarin Daddy ne su yi hakuri. Sagir ya ce ya fada masa sunan hotel din da suke, zai kawo abincin da aka tanadar musu. Ya gaya masa sunan (Jireh Suites).
A reception din hotel din ya tarbi Sagir, ya karbi kabakin abincin ya kakkai musu, Mammah da Daddy daki daya suke, Baffa Atiku shi kadai. AbdulkarimDakata shikadai a dakinsa, Dr.Idris da matarsa Dr. Tawheedah daki daya, Usman, Uncle Ibrahim,Haleem dasu Farhan daki daya, Sauran yan tafiya duka mata ne daki guda suka hada. Daga reception Sagir ya koma.
Sun ci sun sha daga abincin fulanin usli, sun sha fura da nono kindirmo har sun gode Allah, sannan kowannen ya nemi makwanci don huta gajiya. Abdulazeez na tare da Baffa Atiku, Hafsat na tare da su Aunty Luba, Daddy dai ya dauka daki daya Abdulazeez din ya kama musu shi da Hafsat din tunda shi ya kakkama dakunan,ko kusa ba wanda ya gaya mata abin da ya kawo su wannan gari mai dumbin albarka.
Shi da Baffa Atiku suka kwana, wannan kadai ya debe masa kaso hamsin na daga damuwar da ke nukurkusar zuciyarsa. Domin dai Baffan kusan kwana suka yi yana ba shi labarin kuruciyarsa, ya gaya masa hesbrave, genius, and patriotictun yana yaro, babu abin da ke girgiza shi a kan raayinsa da determinations dinsa na son zama babban lauyan gwamnati. Yana so ya ci gaba da zama hakan a yanzu da ya zama cikakken mutum mamallakin iyali. Ya cigaba da amfani da wadannan qualities din akan aikinsa da iyalinsa.
Ji ya yi gwiwoyinsa sun