Showing 126001 words to 129000 words out of 133887 words

Chapter 43 - Auren Kwangila Book 2 & 3 Hausa Novel Complete

Takori   

12 Dec 2024

869

fitowa tun daga karkashin zuciyarta. Hakika kalamansa sun ratsa har tsakiyar ruhinta sun haifar da farin ciki da annashuwa marar misali. Tuni ta mance da shirmen Ishma ta rungume mijinta. Rokon Allah ta ke cikin zuciyarta ya biye bakin Abdulazeez Dakata. Ya sa in mutuwa ta zo ta dauke su tare, in ya so su bar ma Mammah yayansu ta goya. Cikin wannan nishadin suka shige bedroomdinsu ba sa ganin kowa da komai a gabansu da bayansu sai junansu
8/13/20, 8:13 PM - Mmn Nasreem: SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870

*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*
Bayan sadakar ukun Azumi mutanen gidan suka dawo gabadaya duk jikkunansu a sanyaye cike da kewar tsohuwa Azumi. Abdulazeez ya san da rasuwar, shi ma kuma ya fi kowa jin dadin hukuncin da Mammah ta dauka na rashin sanar da Hafsat. Adduar da ba ta yi mata ba ya hada yake yi musu su biyu. Har Azumi ta yi arbain da rasuwa Hafsat ba ta sani ba. Ranar sadakar arbain Daddy ya aika wa iyalinta kudi masu yawa a sayi duk abin da ya kamata a yi sadaka, da ma kuma sun tafi da komai nata da ke gidan. Rayuwa kenan, Azumi kamar ba a yi ta ba a gidan tsohon Ambassador Hamza Atiku. Allah ka sa mu cika da kyau da imani, mu gama lafiya da kowa, amin.
******
Hafsat ta ci gaba da rainon cikinta karkashin kulawar uwa/suruka ta gari Hajiya Maryam Hamza Atiku. A gefe tana ci gaba da karatunta cike da kwazo. Semester ta kare suka yi jarrabawa amma hutun na sati biyu kacal. Wannan karon ko Yola ba ta je ba balle ace America, Mammah ta ce ita da hawa jirgi sai ta haihu kuma. Ga hutun daman ba yawa, shi ma a nasa bangaren da ya gama semester din farko ya so ya zo gida, amma yana da dissertation da zai rubuta a cikin hutun, dole ya hakura tunda kullum suna tare a waya da daddare. Sai da cikin Hafsat ya cika watanni bakwai Mammah ta gaya mata gaskiyar rasuwar Babarta Azumi. Hafsat ta sha kuka kamar ranta zai fita, kamar a lokacin aka yi mutuwar, hatta Abdulazeez ta yi fushi da shi kan shi ma bai gaya mata ba, Mammah ma an yi fushi da ita na kwana biyu tana ta lallashi tana bada hakuri. Abdulazeez ya ce.
We want to save lives, wasu na tafiya wasu na zuwa! Haka rayuwar ta gada, take heart sweetheart.

******
Ranar wata litinin Hafsat ta sankato katon danta a asibitin (DIFF) mai tsananin kama da ubansa. Lokacin watanni biyu suka rage wa Abdulazeez ya gama L.LM dinsa. Fadin farin cikin da wannan family suka samu kansu a ciki ba daga su ba, ba daga mutanen Yola ba, ba zai misaltu ba. Zo ki hango jika a hannun tsohon Ambassador Dr. Hamza Atiku Dakata yana ta tofe shi da addua ya hana Maryam dauka wai in ta ga ya fi shi kyau sakinshi za ta yi. Gefe ta koma tana bai wa Hafsat tea a baki tana fadin.
Ka yi ka gama Daddy, ga sabon jini ba abin da zan yi da tsoho mai furfura.
Duk da Hafsat cikin hajijiyar haihuwa ta ke sai da ta yi wa maganarsu dariya a fili. Daddy ya haskawa Baby camera da galleliyar wayarshi ya dana masa hoto ya tura wa ubansa. Wannan ya faru tun a asibiti kafin su dawo gida. Kwanansu hudu suka tattaro bakidaya suka yo Kano inda Mammah ta ce a can za a yi taron suna.
Adda Hafsatu ta girka garwa a murhu ta soma wanke Hafsat da ganyen dalbejiya da runhu. Babyn ma ita ta ke masa wanka safe da yamma. A dakin Addar suke kwana ita da Mammah suna gado ita da jaririnta, Mammah na bisa carpet ta jefa filo bisa. Duk kukan darensa ba ya hana ta barcinta domin kuwa sun san yadda suke yi masa ya yi shiru. Azababben jego Addah ke mata har kuka ta ke yi in ana wankan nan na runhu da gashi da zaman ruwan zafi.
Ana i-gobe suna gidan ya kacame da shirye-shiryen abincin gobe, duk kannen Hajiya Maryam sun zo da yayansu gidan ba masaka tsinke, Aunty Mariya ta goye babyn ta rufe shi ta fita da shi dakin da suke. Hafsat ta fito daga wankan yamma ta shirya cikin atamfa (Vlisco) ruwan goro da ratsin blue ta daura dankwalin sama-sama ta kwanta tana hutawa. Tunanin Abdulazeez ta ke yi, rabonta da shi tun ana i-gobe za ta haihu, zafin nakuda ya sa ba ta tuna da wayarta ba sai bayan ta haihu. Da aka sallamo su ta neme ta a dakinta ta rasa har suka taho Kano ba ta tambayi Mammah ba saboda kunya, ta san da ta ji tana cigiyar waya ta san wanda ta ke so ta kira shi ya sa ta biyo gida (fillanci) ta yi shiru kawai.
Tana kwance tana wannan tunanin ta ji iskar da ta ke shaka tana sauyawa da wani atmosphere mai dadi da kwantar da zuciya;the familiar scent of creed aventus, idan mafarki ta ke yi tana rokon Allah kada ya tada ita daga wannan daddadan mafarki. Tattausan hannunsa ta ji cikin nata ya matsa shi sosai yatsunsa sarkafe da nata. A hankali ta ke bude idonta don tsoro ta ke ji kada ta bude idon gabadaya ta ga ba haka ba, gradually idanuwan suka washe a dakin hasken kwan fitila ya haska mata shi sosai. The last person da ba ta yi tsammanin gani nan kusa ba. Taimaka mata ya yi ta mike daga kwanciyar, abinka da danyen jiki koina ya yi taushi tubus ya yi wani irin fresh kamar da ka taba ta jini zai yi tsartuwa, ta zama kamar sai ka wanke hannu kafin ka taba. Gefenta ya dawo ya zauna kafafunsa na zube a kasa ya ciccibo ta gabadayanta ya aza bisa cinyoyinsa. Kallonta yake cikin ido da wani irin yanayi cikin kwayar idonsa. Kunya ta kamata sai kokarin guduwa ta ke yi, sai ji ta yi ya fara kissing dinta gabagadi ta inda duk ya samu a matukar dokance. Aunty Mariya da ta shigo kawo yaro ta yi kyakkyawan gani ai ba shiri ta juya sai ta ci uban tuntube da robar wankan baby da ba a dauke ba saura kadan ta fadi, ta dafe babyn da ke bayanta da iyakacin karfinta. Da sauri Hafsat ta dire kasa, shi kuma ya hau yi mata.
Sannu Aunty Mariya, dan waye a bayanki?
Wata uwar harara ta zuba masa, ta ce, Danka ne! Ina ma na fadi mun fadi ni da shi in ga ta karshen soyayya a cikin mutane?
Da ya yi wata zabura sai ga shi a gabanta, What? Jaririn kwana shiddan ki ke goyawa? Idan kafarsa ta lankwashe fa? Sauko shi, maza sauko shi.
Ya soma kokarin kwanto goyon daga jikinta da kansa. Kunya ta lullube Hafsat shaf! Ya manta da wa yake magana, kanwar mahaifiyarsa ce ba yar mace da dan namiji suke ba balle ya ce abokiyar wasansa ce. Shi yake abin kunyan, amma ita ke jin kunyar a jikinta. Mariya ta kwance masa dansa tana harararsa bai ko san tana yi ba ya tafi duniyar kallon kyautar da Allah ya yi masa kamar ya yi khaki ya tofar. Aunty Mariya ta fice tana ta fadace-fadace wai Abdulazeez ya yi mata rashin kunya saboda ta goya dansa.
Zo ki gani Hafsat yana tsotson bakinsa yana murmushi, may be he is saying welcome to me.
Tuntsirewa ta yi da dariya.
Ai tun jiya yake tambayarka.
Da gaske? Shi ne ba ki min waya kin gaya min ba?
Abin sai ya koma bai wa Hafsat tausayi, saboda shi tsakaninsa da Allah ya yarda. Fathers love. Ta fada a hankali har ya shiga kunnuwansa.
Which is like no other. Ya ba ta amsa, sannan ya sanya hannun hagunsa ya janyo ta barin hagunsa ya hada su ita da jaririn ya rungume ya lumshe idanunsa.
Allah ya yi muku albarka, Allah ya taya ni kulawa da ku. Idan bana nan Allah ya kula min da ku. Allah ya sa mahaddacin Alqurani ne, sanyin idaniya ga iyayensa da kakanninsa, abin alfahari ga alummah....
Hafsat na ta amsawa da Ameen-ameen. Cikin jin kunya.
Karkata kunnensa ya yi zuwa bakinsa yana masa kalmar shahada, ya yi masa khutbah da sunan da ba ta sani ba. Ya ciro dabinon da ya yo guzuri na (ajwa) daga aljihunsa ya tauna ya sanya masa a baki, yaro ya kama lashe baki, cike da annashuwa ya ce, Hafsat zo ki gani, ya san zaki.
Ta waiwaya ta sake waiwayawa bakin kofa da window. Yaya Azeez, don Allah ka bari kada a jiyo mu, za a ce kana rashin kunya, ko ba ka ji me Aunty Mariya ta fita tana fada dazun ba?
Wata banzar harara ya yi mata, ya ce, To hell with the kunyar, in samu Dan kaina na farko ba zan gode wa Allah ba? Ba zan yi farin ciki ba? Saboda kada ace banida kunya?
Sassauta murya ta yi cikin lallashi, Ba haka nake nufi ba, nufina ka boye kada ka bari a ji sai in kuna ku biyu kai da shi. Nan kuwa gidan iyaye ne kowa na iya ji.
Babban yatsansa ya sa na tsakiya da na farko ya dalle mata baki, ta dafe bakinta don azaba nan da nan ya kumbura. Idanunta sai da suka yi ja.
Ya ce, Gobe ki kara gaya mini traditional folkloresirin wadannan goya shi zan yi in fita tsakar gida kunyar ta makanta ki.
Ta ja baya tana kumburi dafe dda bakinta, bata kara magana ba don lebenta ya yi mata nauyi sai ga Adda Hafsatu ta shigo kawo mata gasasshen nama sai tiriri yake ya ji albasa da yajin daddawa, ta mika mata, Cinye maza kafin a kwashe tuwon.
Ta kalli jaririn da yake ta tsotson baki da hannu, ta ce. Shin yaushe rabonki da ba shi abinci?
Zumburo kumburarren bakinta ta yi, Adda wallahi da zafi, da karfi yake zukowa sai na yi hawaye.
Adda ta dube shi sai juya yaron yake a hannunsa yana kare masa kallo kamar bazai daina ba. Kai bata shi ta ba shi abincinsa, tun azahar rabon da ta shayar da shi, yaro mai hakuri amma sai kin kure hakurinsa, yau kwana shidda ana abu daya, haka za ki daure nan da kwana goma zai daina zafin.
Kallon Adda ya yi cikin mamaki. Nonon ne sai an roke ta take bayarwa?
Addah Hafsatu ta ce Wallahi haka ake fama da ita kullum.
Idanuwa ya watso mata.
Mugunta ki ka koma?
Ta kawar da kai nan ya yi nasarar ganin yadda bakinta ya kumbura daga dalli daya. Dariya ta kama shi amma ya dake, Adda kin ga matso ki rike min yaron nan, danneta zan yi wallahi sai ya sha ya koshi.
Adda kuwa ta karbi yaro ganin ya mike ya nufo ta da karfi ta ce.
Adda kawo shi!.
Ta yi dariya ta dora mata shi a cinya, juya masa baya ta yi ta janyo katon hijabi suka shige ciki ita da jaririn, ta bayanta ya leka, Adda za ta toshe masa hanci fa?
Adda ta harare shi, ta ce, Abin da ka yi wa Mariya za ka yi min ni ma? To ta toshe din, ko ka taya ta nakudarsa?
Da sauri ya tare ta tun kafin ta kai ga rufe baki. Amma ba don ni ba ai da ba a samu cikinsa ba...
Salati Hafsat ta saki daga cikin hijabinta, Addah ta tattara kwanuka ta bar dakin kunya kamar ta nitse. Mariya ba karya ta ke ba, Abdulazeez haihuwa ta sa ya zama fitsararre.
Tana fita ya sassauta murya.
Don Allah, don Annabi ki cire hijabin nan in ganku, Hafsat don Allah. Itssomething Im always dreaming oftundawowarki.
Kamar za ta yi kuka ta ce Idan ka takura ni yin haka a gidan nan ka shiga hakkina Yaya Azeez.
To shi ke nan na hakura, amma in mun koma gidanmu ba za ki dinga rufewa ba ko?
Shiru ta yi ta kyale shi, inda Allah ya cece ta shi ne isowar mutanen Jimeta da aka zo aka fada wadanda suka wuni a hanya, dole ya tashi ya bar dakin ba don ransa ya so ba don sun soma tuttudowa dakin.
An yi suna na gani na fada a washegari a gidan marigayi Malam Abdullahi Dakata. Fulanin Jimeta sun hade da kanawan Dabo. Tafe suke da motocin gara mai ban mamaki ta aure daban, ta haihuwa daban har da manyan bajimai da ransu guda biyar a motar shanu. Aka dinga saukewa a tsakar gidan don dakin da Inna Hafsatu ta ce a zuba ya cika. Gidan suna sai ya koma gidan wani gagarumin biki don su kam kamar yanzu suke ji sun zo auren Hafsat. Baffa Atiku fada ya hau yi a kan garar nan a cewarsa an riga an wuce gurin kuma su Hafsat ba surukarsu ba ce yarsu ce. Daada ta ce sun san da hakan su ma ba su ce yarsu ba ce, abin da alada ta gadar ne suke son a yi musu alfarma su yi ko yaya ne. Shi kansa Abdulazeez ya sha bandiran shaddoji manya-manya, hatta Daddy da Mammah nasu daban, jariri akwati biyu fal da kayan sawa masu kyau da tsada, haka mai jego akwati guda na turamen zannuwa da lesuka. Kakanni ma ba a barsu a baya ba.
An ce wai ko kogi ba ya kin yayyafi wannan gaara ta yi wa iyalin Dakata dadi duk da ba su taba kawo hakan a ransu ba. Na Baffa Atiku daban, na Adda Hafsatu daban. Aunty Zuwaira ta zo suna don Uncle Abdulkarim ya bude mata wuta wannan karon kuma a kan idonta aka yi komai. Tana zaune a gefen gadon da Hafsat ta ke lokacin da Ibrahima autan su Mammah ya shigo ya ce mahaifin Hafsat zai shigo ganin jariri, sosai ta muskuta ta baza ido a kofa.
Prof. Bashar Mai-Jamaa Numan ya daga labulen dakin da sallama, zaratan matasan yayansa uku na biye da shi. Kwarjini da kamala da tantagaryar boko ya dallare idanunta. Ita da kanta ta dauki jaririn ta kai masa a kujerar da ya zauna daga can farkon dakin. Hafsat baki ya ki rufo, ga kunya tana ji wai ita ce ta haihu Abba ya dau jika. Imaamu na ta tsokanarta wai ta zama Maama, Abdurrahman ya ce jariri bai dauko su ba da ya fi haka kyau. Aunty Zuwaira yau har da cewa da Abdurrahman.
A gabana? Ai kuwa Abdulazeez ya fi Addah kyau, fari kawai ta fi shi.
Hafsat na kallonta a ranta tana mamakinta. Tunda ta taso ta san Aunty Zuwaira, ba ta taba yi mata kallon arziki ba, kalma mai dadi bata taba shiga tsakaninsu ba. Iyakaci ta gaisheta ta amsa a wulakance. Yau ita ce da yin wasa da dariya da yan uwanta don ta ga idon mahaifi. (Ya Allah ka barmu da iyayenmu ba don halinmu ba, ka kara musu tsawon rai da lafiya. Wadanda nasu suka rigaye mu Allah Ka sabunta rahma a gare su, ka jikansu ka yi musu gafara kama Rabbayaany saghirah).
Dr. Bashar ya dago ido ya dubi yarsa Hafsah cike da kauna.
Kina ina ki ka bari Abdulazeez ya kwashe komai shikadai bai sammana ko kadan ba?
Dariya ta yi ta rufe fuska, ya karanto adduoi ya tofawa baby. A bakinsa ne ma ta ji sunan yaro Abubakar-Sadiq (Khalipha) sunan da mahaifinsa ya zaba masa kenan.
Suna da kwana biyu yan Jimeta suka koma, yan Abuja suka soma nasu shirin. Adda Hafsatu ta yi tsalle ta dire ta ce nan za a bar mata masu jego ba za a lalata mata aiki ba. Mammah ta je tana mata wanka da ruwan (gass-cooker). Su tafi in ta yi arbain su zo su dauka. Mammah ba ta yi musu ba don ba ta jayayya da mahaifiyarta a kan komai, kuma ta yarda sai sun fi samun kulawa a nan fiye da wajenta.
Abdulazeez dama kwana uku zai yi ya koma U.S sai nan da watanni biyu zai dawo gabadaya.
A daren da su Mammah ke shirin komawa Abuja a washegari, shi ma a daren yake nasa shirin komawar. Jirgin da zai bi na asubah ne daga Kano, zai yi transit a Ethiopia. A dakin Uncle Idris na da yake kwana a soron gidan na farko. Wanda shi yanzu gidansa yana nan cikin gidajen likitoci na asibitin Malam, iyalinsa da su aka yi sunan Khalipha.
Mammah da kannenta mata hudu Luba, Mariya, Furairah, Murja da Hafsat dake can saman gado tana shayar da jaririnta. Sun saka mahaifiyarsu a tsakiya ana hirar bankwana kasancewar gobe ita Mammah za ta koma Abuja ita da Jummai mai aikinta, Abdulkarim da iyalinsa sun koma tun jiya. A cikin hirar ne Mammah ta sako zancen da ya dade yana cinta a zuci, ya kuma fi karfin a yi shi a waya sai yau da Allah ya hada su ido da ido. Ta dubi mahaifiyarsu ta ce.
Addah!
Ta ce, Naam.
Ki tambayi Mariya da Luba shin ko Saima da Halima sun tsayar da mazajen aure ne?
Addah ta ce, Ai da kunnuwansu, kuma sun ji ki.
Mariya ta ce. Halima sarkin ruwan ido? Tana nan tana ruwan idon nata wai mijinta ma ba a haife shi ba. Ni abin da ya sa ban damu ba ganin bana ne ta kammala secondary tana da sauran lokaci a gaba, amma Babanta ya fi so ya yi mata aure.
Luba ta ce, Saima dai akwai wani yaro da ta ke so, sai dai bana jin auren nan zai yiwu?
Mammah ta ce. Saboda me?
Yo, Yaya Maryamu tsiransu a haihuwa shekara uku, yanzu ne yake shekararsa ta farko a jamia ita kuma tana ajin karshe a secondary, sannan iyayensa sun ce ba za su yi masa aure ba sai ya gama degree ya yi hidimar kasa ya samu aikin da zai iya rike iyali. A matsayin Saima na mace yaushe za ta tsaya jiran wannan mijin?
Wata ajiyar zuciya Mammah ta yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login