Showing 60001 words to 63000 words out of 133887 words

Chapter 21 - Auren Kwangila Book 2 & 3 Hausa Novel Complete

Takori   

12 Dec 2024

556

dakin Malam su yi sallama. Ta yi sallama da Dada da matan su Yaya Tijjani, da sauran kannenHabiba da basu koma gidajensu ba tun jiya, an hada musu tsarabar Jimeta rankatakaf! Yara suka yi ta kwasa suna kaiwa mota. Mammah ta fita ta shiga mota suna jiran Abdulazeez.
Kusa da dakin Malam dakin Nuru ne autan Dada, yana makarantar da yake koyarwa a lokacin da yake ranar aiki ce jumaa da safe. Hafsat ta tafi don cika umarnin Mammah, amma sai ta ratse ta shige dakin Nuru ta rufe har da saka sakata.
Ba ta son ganinsa, ba ta son wata alaka ko ta gaisuwa ce ta sake shiga tsakaninsu. Me ya saura a tsakaninsu? Babu for now! Sai yan uwantakar musulunci da zumuncin haihuwarsa da Maryam Dakata ta yi ya riga ya hada. Da ta san haka zafin saki yake a zuciyar diya mace da ba ta yarda da wannan yarjejeniyar ba. Da ta san haka zafin so yake, da ba ta yarda ko kusa Abdulazeez ya shiga rayuwarta ba. A sanda suke tare, the feeling is so sweet a yanzu da rabuwa ta zo, itspainful, very painful. Zuciya ta yi duhu, babu komai cikinta sai kunci mai azabtar da ruhi. Hawaye ke zuba daga idanunta suna sauka a kan tafukan hannayenta.
Abdulazeez Dakata zaune a dakin Malam Babba, Mammah ta ce da shi, ga Hafsat nan zuwa. Ji ya yi kamar ta dauke masa wani nannauyan dutse da ya danne zuciyarsa. Kokari zai yi ya karbe takardar daga hannunta tun wani bai ji ba bai gani ba, ya yi repenting. Ya san Hafsat na da sanyin zuciya, sannan tana girmamashi, tana yawan yi masa uzuri, kalamai kadan za su wanke wannan gundumemen laifin nasa (kamar yadda yake tsammani). Daga shekaranjiya zuwa yau ya nutsu ya tantance aya da tsakuwa, ya yarda rayuwarsa ba za ta taba komawa daidai ba, ba tare da dawowar Hafsat cikinta ba. He can do without Muazatu, but he cannot do without Hafsat, wannan wani abu ne da ya yarda da shi daga jiya zuwa yau kadai ganin yadda rayuwar ta birkice shi (upside-down) ta maida shi wani birkitacce susutacce. Rokon Allah yake ya sa Hafsat ba ta yi zancen wasikar nan da Mammah ba.
Kai ba ta yi ba... babu wani canji a tare da Mamman har ta shiga mota.
Don haka ya ci gaba da taraddadin jiran fitowar Hafsat ya maida hannun agogo baya. Amma har ya kwashe mintuna talatin a zaune babu Hafsat balle kamshin sanyayyan turarenta.
Hankalinsa ya soma tashi ne lokacin da Daddy da Mammah suka shiga kiran wayoyinsa da ke aljihun rigarsa, da fari kamar ba zai amsa ba amma suka ci gaba da kiran. Dole ya amsawa Daddy.
Har yanzu sallamar ba ta kare ba ne Yayansu? Akwai tafiya fa a gabanmu rana tana yi.
Ga ni nan Daddy. Kawai ya ce a sanyaye. Ya tabbata Hafsat ba za ta fito ba kenan. Da za ta fito da tsawon mintuna talatin din da ya share a zaune sun isa su fito da ita, daga dai cikin gida zuwa dakin Mallam. Wannan ma shaida ce mai tabbatar masa da cewa Hafsat ta karbi sakonsa;(And she acts accordingly).
Cikin sagewar gwiwa da debe tsammani ya fito daga gidan Malam Hashim Babbah Jimeta, ya ja motar da iyayensa da kakanninsa ke ciki, suka soma fita daga shiyyar Demsawo. Tafiya sannu-sannu har suka hau titi dodar suka bar garin Jimeta. Ji yake tamkar ya bar wani bari na gangar jikinsa cikin Jimeta, barin da bai san yadda zai yi ya dawo da shi jikinsa ba. Anya bai tafka kuskure ba? Ta yaya ya tabbatar rabuwa da Hafsat shi ne babban tsanin da zai samo masa Muazatu daga wajen mahaifiyarsa? Anya hakan ba shi ne kuskure ba maimakon ya zamo MAFITA a gare shi? Da wadannan tunanukan masu nauyi Abdulazeez yake tuki yana wuce dazuzzuka da bishiyoyi, garuruwa da kauyuka yana mai jin tamkar karshen rayuwarsa ya zo! Da wacce kalma zai kare kansa ranar da Mammah ta karbi sakin da ya yi wa Hafsat don ya samu Muazatu???

*******
Sai da ta ji tashin motocinsu sannan ta koma cikin gida. Dada ta tambaye ta sun tafi? Ta ce sun kama hanya. Kwananta uku ba inda ba a kai ta ba gidajen yan uwa da dangi. Ranar da ta cika sati gidan Yayanta Modibbo ta wuni a Use-Demsawo tare da matarshi Kaltum. Washegari kuma gidan mahaifinta wanda ke cikin gidajen malamai na jamiar Yola. Matarshi Aunty Kubra maaikaciyar gwamnati ce a hukumar haraji ta jiha, mace ce da ta san ciwon kanta, ta ke kuma rungume da su Imamu da zuciya daya.
Cikin sati daya da Hafsat ta yi a gidan mahaifinta Dr. Bashar tare da shi da yan uwanta na ciki daya Imamu da Abdurrahman tunda Modibbo da suke kira Hamma Modibbo yana nasa gidan, Modibbomaaikacin (Immigration Office) ne. Sabo mai tsanani ya shiga tsakaninsu musamman Imamu, wanda ke karatunsa a (American University Yola) a kan tsimi da tanadi. Shikuma Abdurrahman yana aiki da gidan wayar Etisalat. Rayuwar gidan abar koyi ce domin kowanne na da abun yi, sun fahimci juna kuma ilmi ya ratsa kowa. Tsakanin Imamu da Abdurrahman da Dr. Bashar din kansa har rige-rige ake wajen farantawa Hafsat da suke kira (GAAJI) wato auta da harshen fulatanci. Wannan ya taimaka kwarai wajen mantar da ita Abdulazeez da duniyarsa.
A karshen satin Daddy ya shirya musu tafiya zuwa NUMAN ainahin asalinsa don su kai Hafsat ta ga sauran yan uwansa tunda iyaye babu sun kare.
A motar Dacta Bashar kirar Sienna suka yi tafiyar har Hamma Modibbo da maidakinsa Kaltum. Ita da Kaltum na kujerar can baya, Abdurrahman, Modibbo da Imamu na kujerar gabansu, Daddy ke tukin motar, Aunty Kubra na gefensa. Tafiya ce mai dadi da sanya nishadi a gare su, suna tafe suna hira har suka isa garin Numan.
Yan uwan haihuwar Dacta Bashar su uku ne ke raye, Baffa Saadu, Malam Zakari da Surajo duk tare suke da iyalinsu a can Numan kowanne na da kwakkwarar sanaarsa. Su Malam Zakari sun ga yar dan uwansu sun kuma ji duk abin da ya faru da Habiba. Addua kan Habiba ta sha ta kamar yadda Hajiya Maryam ta sha tofin albarka da fatan alkhairi.
Bayan dawowarsu daga Numan da kwana daya Dada ta aiko Nuru ya zo ya dawo mata da Hafsat ta yi shirin komawa gidan mijinta, Mammah ta yi mata waya cewa hutun su Hafsat ya kare za su koma makaranta ranar litinin kwana uku masu zuwa.
Tun barin su Mammah Jimeta Hafsat ba ta kara kunna wayarta ba. A ganinta wayar ba ta da sauran amfani a gare ta. Ba ta da sauran alaka da wanda ya mallaka mata wayar amfanin me zata yi mata? Mammah kuwa da Baba Azumi in ta samu nutsuwa za ta dinga kiransu ko ta wayar Dada ne tana gaishe su.
Da ta dawo Demsawo ta tadda sakon Mammah daga bakin Dada, rasa me za ta ce ta yi. Ta fito fili ta ce da Dada ba ita ba Abuja, mijinta ya sake ta ko me? Kwata-kwata ba ta son tuna cewa an sake ta kalmar tana yi mata maqaqi a zuciya. Wa za ta gaya wa tsakanin Malam, Mammah da Daada ba tare da hankalinsa ya tashi ba? Ko dai shiru za ta yi ta koma Abujan ta ci gaba da zama gidan Mammah ta cigaba da zuwa makaranta tunda ba za ta iya barin karatunta ba? To amma Yayan Haleem ya sake ki, kuma ki koma ki ci gaba da zama gidan mahaifinsa? Alhalin ba rasa muhallin zama ki ka yi ba? Wata zuciyar ta ce.
Haba Hafsatu? Kada ki zam-makaho warke ka karya sandarka! Har abada ba ki da gidan da ya fi na su Abdulazeez din in har duniya da halacci da amana. Koma gaban Mammah ki ci gaba da karatunki in har za ta barki, ki kuma cika alkawarinki na taimaka wa Abdulazeez ya cimma burinsa...... Wani hanin ga Allah baiwa ne!.
Da wannan shawarar Hafsat ta soma shiri kamar yadda Dada ke ta yi mata itama don komawa Abuja. Sai dai irin hakukuwa da sauyoyin da Dada ke damawa kala-kala tana ba ta, ta ce ta shanye a kan idanunta kasa gane kansu ta yi. Da ta tambaye ta ko magungunan me ta ke bata? Cewa ta yi na gyaran aure ne. Bakinta ta ja ta yi shiru ta ci gaba da shirya yan kayan da ta zo da su wadanda duk sun ji jiki saboda maimaita su da ta yi ta yi tana wankewa kasancewar ba ta debo kaya da yawa ba.
Ana i-gobe Hafsat za ta koma Abuja, Mammah ta kira ta a wayar Dada, ko gaisawa ba su yi ba ta soma yi mata fadan rashin amfani da wayarta da ta ke yi. Hakuri ta yi ta ba ta, ta gaya mata sun yi tafiya zuwa Numan kuma tun zuwanta ba ta zama. Ziyarce-ziyarcen dangi ake raka ta nesa da kusa. Mammah ta karbi uzurinta, ta kuma gaya mata goben jirgi za ta hawo ta dawo. Abdulazeez ba ya kasar, ya je America graduation convocation na Ismael daga jamiar Harvard, daga can za su wuce na Usman a Brussels sai nan da sati biyu za su dawo shi da Ismael da Usman din. Don haka nan Asokoro za ta taho in ya dawo sai su koma gidan nasu.
Wata ajiyar zuciya Hafsat ta yi cikin sanyin murya irin nata ta ce, Toh Mommah, sai Allah ya kawo ni lafiya. A gaida Baba Azumi da Daddy.
Za su ji, ki gaida Dada da Malam da duk mutanen gidan.
Da wannan suka yi sallama.
Washegari Dr. Bashar da kansa da Imamu suka kai Hafsat da kayanta filin jirgin saman Yola, jirgin Azman ta bi zuwa Abuja. Babanta ne ya biya kudin tikitin duk da Mammah ta aiko mata da kudi ta account dinta, ita a wajenta har gobe nauyin Hafsat yana wuyansu ba abin da ya canza.SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870

*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*

******
Tafe suke cikin kwazazzabo cikin farar mota hilux mai hawa kowanne irin tudu da kwari cikin wani kauye wai shi Kufana a Southern Kaduna. Muazatu na ta korafi, Regina ta ce, Dadina da ke wutar ciki Muazatu, garaje da rashin hakuri. Tunda na ce miki matsala aka samu kuma zai gyara ki adana min wannan rashin hakurin naki har mu isa.
Dole Muazatu ta yi shiru ba don ta so ba. A ganinta Regina tana daukar alamarinta da wasa don ba ita ta fada cikin abin da ta fada ba. Har suka iso karkashin wata bishiyar kanya nesa da wani hawan dutse. Regina ta faka motar. Tare suka fito ta sa mukulli ta rufe motar, fili ne fetal ba gida gaba ba gida baya, sai wani dogon dutse a tsakiyar filin. Wannan dutsen Regina da Muazatu suka nufa har suka iso gabansa, kowacce ta tattare zani suka fara hawa dutsen nan kamar kadangaru daya na zamowa daya na tallafo ta har suka iso bakin wani dogon kogo na rarakakken dutse, Muazatu takalmi, dankwali da mayafi duk a hannu saboda wahala, har hawaye ta ke yi. Zuwanta wannan wajen na biyu kenan bayan Regina ta ce in ka zo sau daya ba ka kara dawowa bukatarka ta gama biya.
Haduwarta ta farko da Abdulazeez Dakata a ofishin mahaifinta ta fara sonsa kamar ta ciro rai ta ba shi. Ba irin kyautata masa da ba ta yi ba don ya so ta, bata taba tunanin neman soyayyarsa ta wata hanya bayan kyautatawa ba. Amma sai ya bada mata kasa a ido, ta hanyar nuna mata shi babu wannan a gabansa, yana da abin da ya kawo shi Law School ta yi hakuri ya ci gaba da bata girman da yake ba ta na kasancewar ta yar malaminsa. Duk wasu dabarunta sun kare, ta kasa canza wannan murdadden lauyan data fahimci ba abinda ke canza masa wani irin raayin rikau irin nasa.
Regina abokiyar karatunta ce wadda ta fito daga jihar Benue. Hira ta yi hira a tsakaninsu irin ta shaqiqan aminairannan sai ta ke gaya mata yadda ta samu kanta a kan Abdulazeez da raddin sa gare ta, da kuma matsanancin halin data ke ciki akan hakan. Ba da wata manufa ta fadawa Regina ba sai don ta rage radadin dake ranta, irin wanda dan adam ke samu idan ya raba damuwarsa da wani nasa. Wani sakaran kallo Regina ta yi mata ta ce.
Ke wa ya gaya miki yanzu ana tarar namiji haka zikau, a ce ana sonsa ba tare da an tabbatar an kama shi a hannu ba?
Muazatu ta ce, ita ba za ta iya biye-biyen malamai ba, saboda in aka fara baa dainawa, ta ga Mamanta na yi amma ita ta hane ta, ta sha ce da itaadashi ne wanda baa dauka. Regina ta ce, Ina da inda zan kai ki a yi miki aiki a kansa, in aka je sau daya babu komawa, kuma aikinsa na har kabari ne (har wanda aka yi wa ya mutu). Idan kuma na ce ki kara komawa kada ki kara kallon inda nake.
(Mafarin zuwan Muazatu Rufai wajen boka Chiwonzhu a Kaduna-South, kauyen Kufana).
A kan idonsu ya kamo tunkiya ya kalli kudu ya farke mata ciki, zuciyar tunkiyar ya tsigo tana yararin jini ya dora ta a kan wani kasko ya zuba hayaki a kai ta hau tiriri har sai da jinin jikinta ya kone. Bata zuciyar ya yi a tafin hannunta ya ce ta gutsire ta sau goma sha biyu, duk gutsira daya ta ambaci sunansa har ta cinye. Duk kyankyamin da Muazatu ke ji haka ta cinye danyar zuciyar tunkiyar nan. Ya hada ta da wani garin magani ya ce a ciyar da shi a abinci tsayin kwana talatin ba tsallakewa. Wanda ta nufa da wannan asiri ba zai taba samun nutsuwa da kwanciyar hankali ba har sai ya aure ta. Zai iya ja da kowa a kanta, in yace kowa yana nufin kowahar sai ya aure ta.
Wannan shi ne makasudin Muazatu na fara ciyar da Abdulazeez abincin gidansu, daidai da rana daya ba ta taba kuskurewa ba, har zuwa cikar waadin da boka ya debar mata.
Dawowarsu a yau tsibirin boka Chiwonzhu ga su a gabansa, tun shigowarsu yake dawurwura a kansu yana zagaye su. Yana bugun kan Muazatu da wani gashi yana wasu maganganu da ba sa fahinta kafin ya yi zaman yan bori a gabansu. Idan ya yi hakan, yana jira ka fadi abin da ya kawo ka ne, ya gama duba matsalolinka.
Ya daina damuwa da ni, ya ki zuwa mu yi aure, ya daina kirana, ya daina amsa nawa kiran. Nema yake ya fasa aurena daga dukkan alamu.

Kakansa ya lalata komai yarinya!.

Gabadaya suka dago a firgice suka dube shi.
Wani farin dattijo mai farin gemanya, mai tarin shekaru rututu. Yana can Arewacin Najeriya yana karya duk wani sammu da ke jikinsu ba tare da su kansu sun sani ba!!!.
Idanun Muazatu suka firfito cikin tashin hankali.
Yanzu ba wani taimako da za ka yi min ya aure ni? Ta fada cikin son kecewa da kuka.
Ko mun yi zai sake lalatawa, amma akwai aiki guda daya wanda ba yadda zai yi da shi sai dai daga gare ki amincewar take.
Fadi ko mene ne wallahi zan iya in dai ba zan rasa Abdulazeez ba. Muazatu ta fada tana kuka tare da zubewa a gaban Chiwonzhu.
Zai iya zama mai tsauri a gare ki, amma ina tabbatar miki kamar yankar wuka yake. Kuma ba a jikin jikansa zai zauna ba balle ya karya, a jikinki zai zauna har gaban abada.In ba ni ba babu mai iya karya shi.
Rokonsa Muazatu ta shiga yi ya yi mata wannan aikin, ko nawa ne za ta biya. Ita dai burinta ta auri Abdulazeez ko ta halin kaka.
Chiwonzhu ya ce, Aikin ba ya bukatar ko sisinki. Magani ne zan shafa a jikina in sadu da ke, idan ba a yi auren nan cikin sati biyu ba, kada ki kara dawowa inda nake.
A hankali Muazatu ta soma ja da baya, Regina ta soma harararta, Me ye a ciki? Ba kanki aka soma ba, na kwanta da shi ya fi sau goma, me ya ragu a jikina?
Girgiza kai Muazatu ta shiga yi tana kara ja da baya, Im a virgin Regina, aladarshi ba daya ta ke da tamu ba. Idan na je masa babu budurci ba zan taba yin daraja a idonsa ba....
Kuma aka ce miki haka za mu kyale shi bayan an yi auren?
Kamar ta ce da ita, An zo gurin, maganar Mamana ta tabbata;in aka farabinsu ba za a daina ba. Nikuma ba zan iya jura ba, ko zuwa wajen nan kadai balai ne balle hada jiki da wannan kazamin mutumin.
Shi dai boka wasu harkokinsa ya shiga yi a cikin kogon ya manta da su ita da kawarta suna ta jayayya. Da suka fara isarsa ya ce, idan ba ta amince ba su tattara su bar gabansa. Muazatu ta wawuri jakarta ta mike kan su ce me ye wannan har ta kai kofar kogon. Chiwonzhu ya dube ta cikin takaici, Ki sa a ranki ke da wannan mutumin har abada! Ba zai taba aurenki ba. Kina iya gwada wani bayan ni, don ki tabbatar da abin da na fada.
Da kuka wiwi Muazatu ta fito daga kogon Chiwonzhu, ta soma kokarin saukowa daga dutsen, ga rashin nutsuwa ga tashin hankalin abin da ya fada. Santsin dutsen da ta ke kokarin bi a hankali ya kwashi sassalkar kafarta ta yo suuuufa tun daga sama har kasa ta fadi a kan kwankwasonta.
Wata azababbiyar kara ta saki Regina na kallonta daga saman dutsen ta yi tsaki ta ci gaba da saukowa a hankali har ta sauko tsaf, ta kama ta ta mikar tana zuba ihu a haka suka karasa motarsu. Regina ta watsa ta kujerar baya ta tuka motar suka tafi.
Kwananta uku tana jinyar Muazatu wadda ko zama ba ta iya yi sai kwanciya, amma Regina don mugunta ta ki kai ta asibiti. Kwana ta ke kuka tana gaya mata pelvic-girdle dinta (kashin kugu) ya karye. Da ta gaji ta tattara ta ta sa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login