Showing 27001 words to 30000 words out of 133887 words
karye.
Kokarin kwace kanta ta ke yi, amma ko gezau ta kasa ture wannan giant wanda ya riga ya gama kekketa zuciyarta, yake shirin dumping dinta nan ba da dadewa ba. Ina ruwansa da ita? Ina ruwansa da rayuwarta?Meye dalilin sa na zuwa dakinta yanzu? Yadda ta yi alkawari za ta cika da izinin Allah, ta san ba ta da matsayin samar wa zuciyarta abin da ta ke so a yanzu, wato ci gaba da rayuwa da shi har karshen rayuwarsu, fitina ce kawai da giggiwa irin na zuciya.
Idan Abdulazeez mai son kai ne (selfish) hakika ya kwatanta adalci a cikin (selfishness) dinsa. Ya kamata ita ma ta kwatanta,ba a biye wa zuciya sai ta kai mutum ta baro. Ya ci gaba da rayuwa da ita alhalin babu soyayyarta ko digo a zuciyarsa? Ta ruguza masa farin ciki don amfanin kanta? Ko wannan shi ne kokari na karshe da za ta yi a rayuwarta sai ta tabbatar ABDULAZEEZ ya auri MUAZATU...... sai ta tabbatar ya cika burinsa... sai ta yi hobbasar da mahaifiyarsa ba ta yi fushi da shi ba a kan hakan.
Daina mutsu-mutsun kwatar kannata ta yiganin cewa wahalar da kanta kawai take yi, bai yi mata sassaukan riko ba, bai rike tada sauki don ta kwace a sanda ta so ba, ta kwantar da kanta kawai a kirjinsa kukanta na raguwa a hankali har ta daina shi bakidaya. Hannunsa na dama ya sanya cikin yatsunta ya sarke su sosai na hagun na rungume da ita tsakiyar kirjinsa. A wannan lokacin ta tabbata da zaa tsaga jikinta ba za a samu digon jini ba ya hau ya yi sama saboda duniyar gajimaren da ta tsinci kanta. Balle kuma data tsinci tattausan bakinsa cikin nata. Dukkaninsu idanunsu sun rufe sun manta da kowanne irin nauin aure suke yi. Abin da suka sani kawai shi ne, su maaurata ne, kuma suna tsananin bukatar junansu. Alamarin ya fi karfi daga Abdulazeez a matsayinsa na namiji wanda ya kawo wadannan shekarun bai taba kusantar mace da irin wannan kusancin ba. Idanunsa sun rufe, hankalinsa ya gushe, ya soma sumbatarta da sumba mai tsayi da zurfi a duk inda bakinsa ya kai daga kan fuskarta da masangalin wuyanta, cikin wata siga mai nuna tsananin bukatar miji zuwa ga matarsa.......
Abubuwa da yawa ke yawo a kan Hafsat suna ankarar da ita rayuwar da Abdulazeez zai jefa ta idan ya samu wannan nasarar a kanta, kuma ya sallame ta kamar yadda ya kudurta; bazawara... second hand... ko mai ciki da goyo babu aure, babu martabar zama a dakin aure...... ! Sai gantali a jamia, amma ba ta da martabar da za a kira ta matar aure, ko matar Barrister Abdulazeez Hamzah Attikou!Wannan sai MUAZATU. Ita sunanta sauta ga wawa..... bazawara under twenty years!!! Don haka a take ta soma protest. Zuciyarta ba ta afu ga Abdulazeez a yau don wannan rayuwar ba ne kawai, sai don ci gaba da rayuwa tare da shi har karshen rayuwarta.
Protest ta ke sosai da dukkan karfinta da iyawarta, wanda hakan ya tayar da hankalin Abdulazeez fiye da zatonsa. Lallashi ya koma, duk da ba cikin hayyacinsa yake lallashin ba ya san kalaman sun yi tsauri a ce Suhaana yake gayawa su. Wannan jaririyar kanwar tasa da aka haifa akan idonsa ta girma a gaban mahaifiyarsa. Kalaman da yake gaya mata ta ki yarda ko kadan su yi tasiri a tare da ita, don ta amince na yaudara ne da neman cimma buri, ba ta hango komai a wannan lokacin sai zawarci babu budurci. Wani mai matar za ta aura ba ta da damar gina family nata na kanta irin na gidansu sai na gidan wasu. Ko kishiyar Muazatu ba ta isa ta zama ba sai kanwar mijinta.
Wani kuka ne ya taho tun daga kololuwar zuciyarta ta rusa masa shi tunda karfinta ya yi kadan ya raba ta da Abdulazeez a daren yau. Sosai ya tsorata da kukan mai kama da na an yanki naman jikinta, ya koma gefe ya dafe kansa a gefen gado da dukkan hannuwansa. Wannan damar ta samu ta ja duvet ta lullube jikinta tana ci gaba da gabza kuka kamar wadda aka aiko wa sakon mutuwa. Haushi da bakin ciki ne ya sanya shi maida Pajamas dinshi ya bar mata dakinta.
Da sauri ta sauko ta murza wa dakin key ta bar mukullin a jiki. Ba ta sani ba ko ta bar dakin a bude a yadda ya zuciyan nan ba dawowa zai yi ba. Shi kadai ya san cikin halin da ya kwana.
Amma ga Hafsat abin ba haka ya ke ba. Bayan ta goge ido daga kukan kwantar kan data rakito barci ta yi har da munshari da saleba, cikin mafarkinta kalaman Abdulazeez ne wadanda ya fada mata a lokacin da ya tashi daga Barrister Abdulazeez zuwa MIJIN HAFSAT! Sunan da ba za ta fada a fili kowa ya ji shi ba saboda har gobe tana tantama a kansa. Su ke nanata kansu cikin barcinta suna kara armasa mata shi.
Sosai ta makara sallar asuba don a rayuwarta ba ta taba ganin dare mai tsayin na yau ba. Wanda ta sanya shi cikin darare masu dumbin tarihi a gare ta. Wani dare daga cikin dararen da ba za ta taba mantawa da su ba. Ko da ta yi sallah ta shiga kitchen don sama musu abin da za su ci duk da ta makara, alamu ta gani na an yi girkin taliyar indomie da dafaffen kwai. Duk da lahadi ce yau ya ki zama a gidan, ba ta san inda ya tafi ba.
Yadda ta yi girkin rana haka na dare ya tadda shi a dining Abdulazeez bai taba ba, kuma ta tabbatar ya dawo gidan, don ta ji motsinsa sake fita ya yi ba tare da ya neme ta ba. Murmushi ta yi ta kwashe ta ajiye a kofar shigowa babban falonsu inda ta ke ajiyewa Danfulani abinci ya zo ya dauka da kansa.
Fushi Yaya Azeez ya ke yi da ni? Ta fada a hankali. Ya fi mini. Ta fada a fili. Wannan alamari ya fi karfina, sai Yayata abar sonka Muazatu, tunda na gane shi ne muhimmi a cikin auren ba kamar yadda na zata ba. (Its not a crime) idan akwai aure, kuma sai an kai zuciya nesa zaa iya bijirewa. Balle daga Abdulazeez din da ta yarda zuciyarta daban ta ke daukar kowanne alamarinsa.
Lumshe idonta ta yi tana tuno yadda ya ke kissing idanun kansu ba su tsira ba. Labban bakinta ta cije don ji ta yi kamar yana bayanta yana sake kissing din su.
Ya Ilahi. Suhaana ta fada a fili, tare da kwashe kwanukan daren ma ta koma kicin da su ta adana abincin a firji, ta rufo kitchen din da sauri jin horn din motarsa ya dawo gidan misalin karfe tara na dare. Gidan Barrister Sagir ya tafi, a can ya ci abincin dare, Hafsat ta jika nata ta cinye.
SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870
*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*
******
Kiran lambobi masu tsayi ne ya tashe ta daga barci bayan ta yi sallar asubah ta koma. Code ne na kasar Amurka. Barcin idonta ya wartsake nan da nan sai dai kafin ta amsa kiran, ya katse. Ta ciji yatsa za ta kira, kiran ya sake shigowa. Wannan karon ta yi nasarar amsawa.
Bride of the year. In ji (Brothern) da babu kamarsa a wajenta.
Illaila... Ta amsa tana dariya.
Sunan da ta ke kiransa kenan tana yarinya, ba ta iya cewa Ismaeela ba.
Mammahs doll (yar tsanar Mammah). Shi ma ya rama, kafin ya rufe baki ta rama, Bachelors of the century...
“Brides of the moment. Ismaeel ya amsa cooly, muryarsa cike da kulawa ga yar uwar tasa wadda ya shafe watanni bai yi magana da ita ba. Ya yi-ya yi Mammah ta ba shi lambarta ta ce ba ta da waya, Yayan nasa kuwa tunda ya bada masa kasa a ido a kan bukatarsa na a hada baki da shi a yaudari Mammah a kan sistern da bai da kamarta ya kulla gaba da shi. Jiya kamar daga sama kawai sai ga lamba Mammah ta turo masa, wai ta Suhaanah ce. Tun a lokacin ya so kiranta ya yi tunanin dare ne sosai a wajensu, haka ya yi ta daurewa har gari ya waye.
He so much missed her, she so much missed him. Akwai wata irin shakuwa a tsakaninsu wadda ta samo asali tun lokacin da suke taya Mammah rainon ta a Jeddah.Ta san da suna tare da ba ta shiga damuwar da ta shiga a baya ba. Hira suka shiga yi, amma ko kadan ban da zancen aurenta ko halin da auren ke ciki, hirarsu suke irin wadda suka saba tun ta yarinta. Ta tambaye shi ina labarin Usman, ya ce yazo America daga Brussels suna tare, ya je excursion birnin Orlando. Tana jin fitar motar Abdulazeez wajejen karfe takwas na safe, ba su yi sallama ba sai da cajin wayarta ya kare, wayar ta kashe kanta.
Ta sauko daga gadon ta sanya wayar a caji. Ta duba agogo, karfe takwas na safe. Bandaki ta shiga ta yi wanka, wanke baki, alwala sannan ta fito. Ta samu kanta da yin kwalliya sosai da (lace) mai tsananin taushi, kalar pusher pink da ratsin baki. Sosai kalar da leshin suka karbeta suka kwanta a sassalkar fatar jikinta. Ta fesa turare (christian dior) ta fada kitchen ta daura apronta hau girki.
Wata zuciyar na cewa, ta dafa da Abdulazeez, wata na cewa aa, ko kin dafa da shi ba ci zai yi ba, ina ma ki ka ganshi? Motsi ta ji ana zura mukulli a jikin kofar falon, ko kadan ba ta ji karar shigowar motarshi ba, domin ta kure qiraar Abdurrahman Sudaith a gidan gabadaya cikin Suratul Maidah, ko ba don haka ba motar Abduazeez GMC Terrain ba ta kara, sai in shi ya yi horn.
Ba ta fito ba ci gaba ta yi da abin da ta ke yi, tana mamakin me ya dawo da shi a wannan lokacin? Misalin karfe goma sha daya na safe.
Zama ta yi ta ci dankali na turawa da agadan data soya da farfesun kaza, ta wanke hannunta da liquid soap ta cire apron din ta adana a mazauninsa ta kora da gwangwaninfantasannan ta fito zuwa falon.
Ya watsar da gown dinsa da wig a tsakar falon, hatta briefcase din ta yi nata wurin. Kwance yake a kujerar da ta fi kowacce tsayi a falon, ko takalmin kafarsa da socksbai cire ba,he dont even loose his tie, kwanciyar da daga gani za ka fahimci ba ta lafiya ba ce ya yi. Ji ta yi gabanta ya yi mummunan faduwa, ta rabe ta bayan kujerar da yake kwance ta wuce dakinta ta rufo kofa a hankali.
Amma ga mamakinta ta kasa zaune ta kasa tsaye, so ta ke ta san me ya same shi, sai dai ta san ba ta da wannan matsayin. To amma ai ko babu aure Abdulazeez dan uwanta ne kamar Ismaeel, tunda Mammah ce ta haife shi, ba za ta taba son wani mummunan abu ya faru da shi ba, ko rashin lafiya. A haka lokacin sallar azahar ya yi mata, da ma tana da alwala ta matsa wajen ibadarta ta tada sallah.
Samun kanta ta yi a cikin sujjadarta tana yi wa Abdulazeez addua har da hawayenta, a kan ko ma me ye ke damunshi, Allah ya sa ya zo masa da sauki. Da ta idar tana so ta fito falo ta ga halin da yake ciki, amma ta kasa. Zama ta yi ta hada kai da gwiwa sai a lokacin ta tuna da wayarta, ko Mammah za ta kira ta gaya mata ya dawo a cikin wani irin yanayi ba lokacin da ya saba dawowa ba? Wata zuciyar ta ce.
Akul! Ki je ki tabbatar da abin da ya same shi din tukunna, yanzu haka ma ya bar gidan.
Mikewa ta yi cikin sanda kamar marar gaskiya ta bude kofa ta fito falon. Yana nan yadda ta barshi awanni uku da suka wuce, ko juyawa bai yi ba. Ya yi rub-da-ciki a kan hannayensa. Is touching him a crime? (Taba shi zai zama laifi?) Ta tambayi kanta. Ba ta sani ba, don haka ta je ta tsaya a kansa tana tunanin abin yi.
Lokacin sallah ya yi. Ta fada muryarta na karkarwa.
Ko motsi bai yi ba, sai ta tsugunna ta kai hannunta kan goshinsa. Zafi rau! Ta taba wuyansa shi ma kamar garwashi don zafi. Kawai sai ta durkushe a wurin ta sanya kuka.
Da kyar ya cira kansa daga kwancen ya bude idanunsa da suka kankance suka yi jawur yana kallonta. Ta dago fuskarta suka yi wa juna kuri da ido.
Wane taimako zan iya ba ka? Abinda ta iya tambayarsa kawai kenan cikin karkarwar murya.
Duk halin da yake ciki sai da ya yi murmushi,shes very soft-hearted. Ki duba lokar jikin gadona akwai paracetamol ki dauko min.
Dakin a bude yake?
Ya lumshe ido tare da daga kai, shi bai ma taba rufe kofar dakinsa ba wai don zai fita, ashe ba ta taba shiga ba? Mikewa ta yi da hanzarinta har tana tuntube zuwa dakin. A tsayin rayuwarta ba ta taba ganin dakin barci mai ban shaawa irin wannan ba. Yafi nata tsaruwa ninkin ba ninkin. Ko kuma idonta ne ya ga hakan? Bazata iya cewa ba.
(English Bedroom) komai fari da ruwan toka (white and ash), hatta labulayen. Ba ta wannan ta ke ba, drower din ta nufa kai tsaye ta debo kwayar maganin ta fito. Kicin ta koma ta samo gorar ruwa mara sanyi ta dawo. Taimaka mishi ta yi ya tashi zaune, ta sa mai kwayar maganin a hannunsa ya watsa su a baki ta kafa mai robar ruwan a bakinsa.
Komawa ya yi zai kwanta ta rike masa hannu, dan dago ido ya yi da kyar ya dube ta da idanun tambaya.
Kada ka kwanta a nan, ka koma daki.
Ba zan iya ba. Ya ce da ita a wahalce.
Ill help. Ta ba shi amsa.
Ciwo ya ci karfinsa, amma a ransa ta ba shi dariya sosai. Dube ta yar ficika da ita, ko ya za ta iya daga kato irinsa? Da zai iya doguwar magana da ya tambaye ta hakan.
Ki bari in kwanta kadan forsome minutes tunda na sha magani zan koma.
Ba ta ce komai ba ta koma ta zauna a gabansa, zuciyarta a jagule. Ya maida idonsa ya rufe sai bacci.
Da ta ji yana sauke numfashi irin na bacci, sai ta samu kwanciyar hankali, ta koma daki ta yi sallar laasar. Kicin ta koma ta hado duk abin da ta soya a kan tray ta dafa shayi baki da lipton din tetly tea, ta zuba kayan kamshi su kani fari da citta kadan ta tace ta dauko ta dawo falon da su, ta ajiye a gefensa. Baccinsa ya yi nisa sosai, don haka sai ta koma daki ta kwanta tana ci gaba da yi masa adduar samun sauki.
Cikin dan barcin da ya soma figarta ta ji kamar ana kiran sunanta. Ta bude ido sosai, daga falo ne Abdulazeez ke kiranta. Da sauri ta fito, ya tashi yana zaune dafe da kansa da hannun damansa. Zama ta yi a gefensa ta hau zuba masa shayi ta zuba zuma, ta juya ta mika masa. Bai yi musu ba ya karba ya soma sipping a hankali.
Tana kokarin zuba agada da chipsya ce.
Bar wannan. Ba ni farfesun kawai.
Ta zuba a dan bowl na tangaran ta tura gabansa. Tana so ta ce ya cire suitdin mana saboda sai zufa yake yi, amma ta yi shiru, kada ta wuce makadi da rawa.
Kafafunsa ya mika mata bayan ya ajiye bowl din a gefe ba don ya gama ba.Cire min.
Dago ido ta yi cikin wata irin siga ta kalle shi. Kwayar idanunsu suka sarke da na juna. Ta ya ya za ta iya kama kafafunsa ta cire masa takalmi da safa? Aikin ya so ya yi mata tsauri. Shi kuma ba da wata manufa ya fadi hakan ba, zazzabin jikinsa ya sauka ne, zafi yake ji sosai. Ganin umarninsa ya jefa ta a gajeren tunani, sai ya fara kokarin cirewa da kansa.
“Sorry, you can go (za ki iya tafiya).
Sai ta ji ba dadi, mene ne a cikin cire safa da takalmi da ta kasa? Bashi da lafiya shine dalili. Bayan wannan ba wani abu.Mikewa ta yi kamar wadda kwai ya fashewa a ciki ta nufi daki zuciyarta babu dadi.
Da ya cire takalman ci gaba ya yi da shan farfesun kadan-kadan. Girkinta yana da wani sinadarin dandano irin na Mammansa. Ya fahimci hakan tun sanda yake cin abincinta, lokacin da tana amarya. Ganin cin abincin nata da yake yi zai haifar da wani bond na daban a tsakaninsu shi ya sa ya daina, ba don ba ya so ba. Auren da ba mai dorewa ba bai kamata ya bari ya yi tasiri mai yawa a zuciyarsa ba.
A nan ya bar bowl da spoon din da ya sha farfesun ya tattara shirginsa ya koma daki. Bai kara fitowa ba, wanka ya yi, sannan ya yi sallolin azahar da laasar da ke kansa, ya bi lafiyar gadonsa ya kwanta bayan ya kashe wayoyinsa.
Tufka da warwara yake, na yadda rayuwarsu ta gaba za ta kasance tsakaninshi da ita.
******
Ta ci abincin dare ta yi shirin kwanciya, amma anya za ta iya barcin nan mijinta na gefe ba shi da lafiya? “Ki daina kiranshi mijinki fa, mijin Mu’azatu dai�?. Wata zuciyar ta gyara mata.ď
Har yanzu hotonta da ya kafa musu a falo yana nan. Ta shafa wa kanta lafiya ne ta daina kallon bangaren da hoton yake.
Abdulazeez bai cancanci ki tausaya masa ba, saboda ba sonki yake ba, ko yau din ma da ya kula ki don ba shi da yadda zai yi ne, ba shi da mai taimaka masa. Manta da shi ki yi barcinki.
Amma abin mamaki ta kasa bin wannan shawarar ta zuciya mai gaskiya. Ko ba ya sona Dan Mommah ne, duk wani jininta amana ne a gare ni, ba za ta ga Da na ba lafiya ta kauda kai ba. Ni ma