Showing 45001 words to 48000 words out of 133887 words
za su yi kyau da na malamin makaranta saboda tana da hakuri, sanyin rai da juriya.
Hafsat na jin dadin karatunta a NILE fiye da tsammani, ta yi kawa wata mutuniyar Zamfara mai suna Mami, aiki ne ya kawo mijinta Abubakar Sadik Abuja, Mami za ta girme mata da wajen shekaru hudu don shekarunta ashirin da biyu. Komai na Hafsat da yanayin shigarta na kamala da tsantseni na burge Mami wadda ainahin sunanta Rabia Sada. Mijin Mami maaikacin Etisalat ne, duk ajinsu babu wanda Rabia ta ga ya kamata ta yi abota da shi sai Hafsat Dakata, ko don ta amfana da ita saboda cikin dan lokaci hazakarta ta (good foundation) din da ta samu ta fito fili, kowa ya fahimci talented ce. Daga assignment har test ita ce zakaran gwajin dafi. Ita dai Hafsat ba ta zura jiki a kawancensu da Mami sosai, saboda yadda Mammah ta tsoratar da ita a kan kawayen Abuja, amma yadda Mamin ke nace mata ya sa dole ta ke kula ta, amma a abin da ya shafi harkar karatu kadai. Ba ta taba yarda wata magana bayan ta karatu ta hada su ba.
Har ga shi watanni sun gangara suna shirin fara jarrabawar (first semister) wanda ya zo daidai da kammala (Law-school) din Muazatu wadda ta shafe watanni goma a jihar Yola.
*****
Yau a kan idon Mami da mijinta Abubakar Abdulazeez ya dauki Hafsat, da ta bude motar ta shiga ta zauna, sunkuyawa ya yita saman kanta yana gyara mata sarkar wuyanta da ta harde cikin gashin kanta ta baya,gashin yake zarewa daga cikin sarkar a hankalihannayensa zagaye da ita. Yayin da kanta ke kusa da kafadunsa. Sosai Mami ta saki baki da hanci da ido daga nesa ta ke kallonsu da mamaki, don ba ta taba sanin Hafsat na da aure ba ganinta yarinya karama danya shataf. Couple din sun zauna mata a zuciya sun kasa bacewa, sai zancensu ta ke yi wa mijinta a hanya. Ba ta taba ganin matar da ta dace da miji irin Hafsat Dakata ba, har kishi ya sike Sadik ya ce.
Wallahi zai ajiye ta a gefen titi, ina ruwanta da kallon mijin kawarta har ta ke yaba shi a gabansa sabida jahilci? Sosai Mami ta kama kanta don ta san halinsa sarai zai iya ajiye ta a titin a kan kishinsa, amma ta sa a ranta za ta tirke Hafsat sai ta ba ta labarin rayuwarta da inda ta hadu da wannan handsome da ta dade ba ta ga namiji mai tarin abubuwan da ya mallaka ba.Duk da itama ta san ba abune mai sauki samun hakan daga Hafsat din ba yadda take ji da class dinnan da zata tsaya tana wani bata labarin rayuwarta ko na mijinta. Amma ance a rashin tayi akan bar arha. Zata gwada saarta.
A washegari da ta turke Hafsat da tambaya, nan da nan tayi fuska, ta ce ita ba mijinta ba ne, Yayanta ne.
Amma irin Yaya a dangi ko familyfriends din nan ko? Saboda ita dai ta ga abin da ta gani wanda ya sanya ta shakka a kan zancen Hafsat. Murmushi Hafsat ta yi har kuncin nan ya lotsa ciki sosai. Murmushin da Mami ta kara dorawa a sikeli.
Ke me ye damuwarki Mami a kan hakan? Daga ganin mutum ba ki san ko wane ne ba sai ki ce mijina ne? To babu ko daya.
Mami ta ajiye biron hannunta tana murmushi ta ke kallon Hafsat. Ni na ga abin da ya sa na tambaya ko kin ki gaya min Hafsat, a sanda ya bude miki murfin mota ki ka shiga ki ka zauna, ya sunkuya yana gyara miki sarkar wuyanki. Akwai wani babban alamari cikin kwayar idanunsa a kanki. In kin sani kina boye min ne ban ga laifinki ba, don na dade da sanin kawance na da ke bai dadaki da kasa ba. In kuma ba ki sani ba, ina mai sanar da ke wannan. Idan kuma da gaske Yayanki ne kamar yadda kika dage im telling you wannan Yayancin will turn to something very special nan ba da dadewa ba.
Bin labban Mami Sada ta yi da kallo, a lokacin da ta ke furta kalamanta. A ranta tana mamakin me ta gani da ya sa ta fadar hakan?Ko jiya Abdulazeez kwana ya yi da wadda yake so a kan waya, tsakaninta da shi ya kai ta makaranta ya dauko ta, ta dafa masa abinci ya ci. Ba ta da sauran buri a kan Abdulazeez yanzu, ta dade da yi wa zuciyarta fada, kuma zuciyar ta dade da shiga taitayinta. Ba ta sanya mata komai sai tunanintahowar ranar karewar KWANGILA wadda ta tabbata tana tafe nan bada jimawa ba. Bai gaya mata ba, amma tana lissafe da watanni, kuma ta ji yana fadin zai tafi Lagos (call to Bar Ceremony) din masoyiyarsa, ba ita ya gayawa ba, abokinsa Abdallah ta ji yana gayawa a waya.
Ga mamakin Mami gani ta yi idanun Hafsat sun cicciko da wata zazzafar kwallah. Ta kuma dade da barin jihar da suke ciki, ta lula wata jihar daban ta tunani mai zurfi. Wannan ya tabbatar mata akwai wani alamari mai girma tsakanin Hafsat da handsome din da ta kira Yayanta kamar yadda ta ke ikirari. Amma tunda Hafsat mutum ce da ba ta son a yi mata shisshigi cikin (personal life) dinta zai fi kyau ta kyale ta.
Ni dai shawarata ita ce, duk runtsi kada ki bari ya kubuce miki, nasan mijinki ne ba saurayi ba, irin wadannan daban ne Hafsat, alamu sun nuna yana daga cikin mazan da matan waje ba za su kyale wa matansu na gida kadai ba. In wannan ce matsalarki Hafsat ki cire kunya da kawaici ki damke mijinki da hannu bibbiyu, in ba haka ba za ki sha mamaki cikin garinnan.
Sosai Hafsat ta yi mamakin yadda Mami ta gane Abdulazeez mijinta ne. Maganganunta kuma kamar ta san me take ciki a rayuwarta da shi din. Bata ce komai ba sai binta da kallo.
A wannan ranar direban office dinsu ya sa ya maida ita gida sabida ayyuka da suka yi masa yawa. Don haka a hanyarsu ta dawowa ta kifa kanta jikin murfin motar ta yi kukanta mai isarta ta koshi. Kukan tausayin kanta... kukan rashin sanin mene ne aibunta da Abdulazeez ya kasa sonta har duniya ta fara gane tana da matsala makamanciyar wannan a tare da shi?
Aibubbuka da yawa Hafsat. Babban cikinsu rasin asali, don haka ki ci gaba da yi masa uzuri kamar yadda ki ka faro, watarana sai labari. In ji zuciyarta.
******
Sai da ya bari Hafsat ta kammala jarrabawar karshen zango da ta ke zanawa sannan ya je gida a wata ranar lahadi tunda ba ranar aiki ba ce, ya tabbatar Daddy yana gida a lokacin Ismael ya koma America, Haleem da Usman ne kawai ya rage ba su koma inda suka fito ba. Ya samu Mammah da Azumi uwar goyon Suhaana wadda a yanzu za a iya ce mata kaka a gare su, ya ce ya zo ne da muhimmiyar magana, yana bukatar su zauna a falo dukkanninsu.
Mammah ta je ta fito da Daddy ya same su a falon har Haleem.
Barrister da sanyin safiyar nan, ya aka yi?
Murmushi ya yi ya sadda kansa kasa. Har gobe Dr. Hamza bai bar jan yayansa a jiki ba duk da dukkanninsu a yanzu babu wanda bai isa a yi masa aure ba banda Haleem, shi ma da a kauye ne ba irin rayuwarsu ba, da tuni ya jima da yin auren.
Sai da kowa ya nutsu ya ba shi hankalinsa, sannan ya fara ba su labari tiryan-tiryan tun hirar da yayi da Habiba aranar da alamarin zai faru, da bincike da ya soma a boye akan garin Jimeta, haduwarsa da Barrister Sagir Hashim Jimeta. Yadda ya rika nace masa duk da kasancewarshi ba mai son harka da jamaa ba, sai dalilin kamanninshi da Suhaana. Yadda suka zama abokai na jiki a watannin da suka gabata da yadda har yake zuwa gidansa cin abincin dare duk don ya shiga jikinsa, ya tabbatar da abin da yake son tabbatarwa.
Gayyatarshi daurin auren dan Yayarshi da Sagir yayi, da abin da ya faru zuwansu Jimeta ya kwashe duk ya gaya musu. Mammah da Baba Azumi sai kabbara suke yi zukatansu fal farin ciki. Dr. Hamza Atiku sunkuyar da kai ya yi yana tuna tarin wautar da ya yi a baya, yana kara istigfari cikin zuciyarsa.
Ka yi maganar da Addah?
Mammah ta tambaya.
Girgiza kai ya yi, Ban taba yi mata zancen ba har bayan da na tabbatar, saboda bana son abin da zai dagula karatunta.
Masha Allahu. In ji Mammah.
Tafiya Jimeta ta same mu, tunda ai ta kare jarrabawar ko?
Ta gama jiya.
Bari in yi wa mutanen Kano waya su shirya don gabadayanmu za a yi wannan tafiya.
Kan ka ce me ye wannan Mammah ta hau bugawa su Adda Hafsatu waya, su Luba, Mariya, Furera da Murja, har Aunty Zuwaira da ke nan Abuja ba ta bari ba. Matar Uncle Idris da matar Ibrahima da sauransu. Cewa su yi shiri za su tafi Yola an gano iyayen Addarta. Tsofaffin hotunansu da suka sha yi da Habiba a Jeddah ta hau bincikowa, Abdulazeez ma yana da wasu daga ciki, ya sanya a aljihu ya tafi da su har Jimeta da zummar in bukatar hakan ta taso ya fiddo su, to kuma da ya canza shawarar rashin tada maganar a lokacin daurin auren ya dawo da abinsa ya boye inda Hafsat ba za ta gani ba.
Shiri sosai wannan family ke yi na tafiya Jimeta (Yola North), wanda za su yi kwanaki uku masu zuwa. Mammah ta kasa bari har zuwa karshen mako don haka ta sanya tafiyar ranar Laraba, masu aiki su dauki uzuri.
Washegari a ofis dinsu ya tadda Sagir yana rubutu cikin wasu files. Gaisawa suka yi kamar yadda suka saba, tun kafin ya yi magana Sagir ya riga shi, ya gaya masa Dada ta ce a yi masa tuni kan maganar nan ko tana da rabon ganin yarta a sauran numfashinta. Ta fara kasa jurewa jiran.
Sadda kai Abdulazeez ya yi yana jin wani iri a zuciyarsa. Daga bisani ya ce da Sagir, abin da ya kawo shi kenan. Iyayensa sun yi shirin tafiya Jimeta a kan maganar Habiba ranar Larabar nan ya sanar da su Dada.
Iyayenka???
Sagir ya tambaya cikin mamaki.
Daga masa kai Abdulazeez ya yi da siririn murmushi a fatar bakinsa, ya ce,
Dogon labari ne Sagir, amma a gidanmu Yayarka ta zauna. Sauran bayani sai mun isa can.
Daskarewa Sagir ya yi a zaune, yana tazbihi yana kadaita Allah.
SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870
*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*
*****
WASHEGARI
An tara maza da mata, babba da yaro na nesa da na kusa, na zuriar Malam Hashim Babba Jimeta. Da zuriar Dr. Bashar Mai-jamaa Numan, wanda shi ma dan nan asalin Yola ne daga karamar hukumar NUMAN. Kamar yadda Malam Babba da Dada suka bada umarni; duk wani jininsu ya hallara an ga Habibah.
Tunda Sagir ya shigo da bakin falon ganawar wannan family kowa yake raba ido ya ga ta inda Habiba za ta billo, tunda an gaya musu wadanda suka rike ta ne suka kawo ta. Tun fitowarsu Mammah ta ja mayafin Hafsat ta rufe mata rabin fuska, ta ce ta rufe fuskarta ta kalli gabanta, sai ta ce ta bude za ta bude.
Ita dai Addah mamaki ya hana ta cewa komai, saboda ita dai tun tasowarta ba ta san suna da yan uwa a Yola ba. Jikin tsohuwa Dada da Malam Babba ya yi sanyi ganin har wadannan baki suka gama shigowa suka zazzauna babu Habiba babu alamunta.
Gaggaisawa aka fara yi, sannan Malam ya bude taron da addua. Daddy ya gabatar da kansu su ma suka gabatar da kansu a matsayin iyayen Habiba da yan uwanta, ga kuma mijin aurenta Prof. Bashar Mai-jamaa, karshe Malam ya tambaye su wane labari suke dauke da shi game da yarsa Habiba? Sannan ina ta ke yanzu? Dr. Bashar ya kara da cewa,
Lafiya nake zaune da maidakina Habiba tun ina matsayin Malamin makarantar sakandire. Rana daya na tsiri karo aure sakamakon kowa da rubutacciyar kaddararsa ta aure, amma ba don Habiba ta gaza da ni ta kowanne bangare ba.
Yaranmu uku, Modibbo (Ridhwan), da Abdurrahman sai auta Imamu a lokacin da na auro Hajara. Tun zuwan Hajara gidan ya ki zama lafiya, fitintinu iri-iri kullum da tashin hankalin da zan dawo na taras. Amma duk sanda na yi bincike a kan rikicin zan tadda Hajara ce ta tado shi. Zaman lafiyan ya kara tabarbarewa a gidan lokacin da Habiba ta samu ciki na hudu, Hajara kuma ta kwashe shekaru uku a gidan kenan babu ciki ba dalilinsa. Wannan ciki ya kara daga hankalin Hajara ta fiddo ainahin kalarta a fili, ta mace mai tsananin hassada akan abinda Allah bai bata ba.
Na sha ji tana fadi wa Habiba wannan cikin ba dai ki haife shi a gidan nan ba, ko dai ya bi rariya ko ki haife shi akan titi.Sai in tsawatar da kakkausan harshe, in kuma gaya mata Allah ya fi ta. Mugun bakinta ya kare a kanta. Saboda Habiba ba ta da fus, bata iya tashin hankali ba,rashin katabus dinta yayi yawa, shi ya sa Hajara ke mata duk cin kashin da ta ga dama. Ido wannan Habiba bazata daga ta dube ta ba. A karshe ni na koma kishiyar, saboda ni nake tare wa Habiba fadan in ina nan, in bana nan kuwa tana shan ukuba a hannun Hajara. Sabida haka ne na ga gara in sauwakewa Hajara auren nan ko ma samu kwanciyar hankali ni da iyalina.
Na saki Hajara saki daya, amma ta ki tafiya, ta ce gara ma in barta ta zauna a dakinta, don in ta tafi biyu-babu zan yi, don kuwa ta sha alwashin Habiba ba za ta haife cikinta cikin gidan nan ba.
A karshe ta karfi na fidda Hajara daga gidana, na watso mata kayanta waje, wannan shi ne dalilin rabuwata da Hajara na farko.
Na maida hankali ga kula da Habiba duk da cikin ba mai matsala bane sam kamar haihuwarta na baya, ji nakeyi kamar wannan ne karo na farko da zaa yimin haihuwa bansan dalili ba. Muka ci gaba da kula da yaranmu da zamanmu cikin rufin asiri da kwanciyar hankali.
Wata rana cikin Habiba nada wata biyu ba kadan na wayi gari na tafi wajen aiki inda nake koyarwa a makarantar yammata ta (GGSS YOLA). Na dawo na tadda su Abdurrahman zugum-zugum a gida su kadai. Na kama Imamu da ke ta kuka na aza bisa cinyana ina tambayarsu ina Mamansu ta je ba ta gaya min ba, ba ta kuma tafi da Imamu ba? Suka ce ai ta tafi unguwa tun kan su dawo makaranta, shi ma Imamu shi kadai suka same shi a kofar gida.
Haka na shiga kicin na shiga nema musu abin da za su ci, muka ci gaba da zaman jiran dawowar Habiba, ina cike da mamakin abinda tayi don bata taba yin haka ba koda wasa, ba inda take zuwa bata nemi izni na ba, sannan wai ta bar karamin yaro kamar Imamu a kofar gida. Har rana ta fadi ba ta dawo ba.
Ban kawo komai a raina ba na sanya a raina cewa, babbar lalura ce ta fidda ita tunda ba ta taba yin hakan ba. Da na ga dare ya yi ne hankalina ya soma tashi, ga Abdurrahman da Imamu sun ishe ni da kuka. Don haka na sako su a gaba muka taho gidan Dada nan Demsawo, mu muna (Upper Luggere) a lokacin.
Tafiyar da har yau ba ta dawo ba kenan, ga yayanta duk sun zama maza, ban da Modibbo babu wanda zai iya tuna ta sai a hoto. Mun dukufa addua muna rokon Allah ya bayyana ta ba dare ba rana, mahaifinta kun ganshi nan ya yi shekaru ba ya bacci, ya kuma ce a duk istikharar da yake yi a kan Habiba Allah ba ya nuna masa komai a kanta. Dada ce ta ci gaba da rainon su Imamu ta ki bai wa kowa a gidannan su ko nawa dangin.
Rana daya na tsinci kaina ba abinda nake so sai dawo da Hajara gidana, na dawo da ita muka ci gaba da zama, amma Dada ta hana ta jikokinta.
Watanni shidda da bacewar Habiba malamai babu adadi Malam Babba ya baza, shima baa barshi a baya ba, suka mike suna addua dare da rana a kan kowanne boyayyen alamari ne tattare da Habiba Allah ya bayyana mana, Ya kuma maido ta gida lafiya cikin iyalinta.
Rannan na dawo aiki na tadda cincirindon mutane a kofar gidana. Ana hango ni aka shiga darewa ana bani hanya. Hajara ce ta ke hauka tuburan a tsakiyar unguwa, ta kekketa sutturar jikinta duk da yadda matan makwabta ke kokarin rufe mata tsiraici abu ya ci tura, da an saka za ta yage su, tana fadin duk irin sharrin da ta rinka shukawa a zamanta da Habiba. Wallahi wasu ko da wasa ban sansu ba, Habiba ba ta taba fada min ba. A karshe ta ke fadin, ita ta yi wa Habiba kurciya ta bar Yola, kuma ko za ta mutu a haukace Habiba ta tafi kenan ba za ta dawo ba. Gidana ma da ta dawo asiri ta yi min ta dawo, kuma ban isa in karya shi ba saboda a kogin Niger-Delta ta jefa.
A sanda ya zo nan hawaye sun jika fuskarsa, ya sanya gefen babbar rigarsa yana sharewa. Hafsat-Suhaanah, wadda zuwa yanzu ta fahimci ko a ina suke, da kuma dalilin zuwansu, da ko wane ne wannan farin bafillacen maabocin zati da kamala. Jikinta tsuma ya hau yi, tsigogin jikinta suka shiga tashi, ta kura masa ido ba ta ko kiftawa.
Wani irin feeling ta ke ji yana