Showing 33001 words to 36000 words out of 133887 words

Chapter 12 - Auren Kwangila Book 2 & 3 Hausa Novel Complete

Takori   

12 Dec 2024

545

shirya in ya dawo su je Dominicta ci Pizza ta sha ice-cream ladan adduarta. Fitarsu ta biyar kenan zuwa (Dominic) hakan ba karamin faranta ran Hafsa yake ba.
In ba ya nan tana tare da su Mammah a waya. Ko ta dauko Alqurani tayi ta tilawa da sauran littattafanta. Baba Azumi ma ta dawo daga Sokoto duk sanda Mammah ta kira ta, ko ita ta kira ta za ta hada su su sha hira. Haka kawai zai ce kada ta yi abincin dare in ya dawo za su fita su ci a Chinese restaurantko KFC. Don haka a wannan dan tsukin Hafsat ba ta da damuwa ko cikin cokali.
SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870

*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*

Daki ta shige da gudu ta rufe kofarta. Ba ta kara fitowa ba sai washegari bayan ta idar da sallar asubah ta fito kitchen don hada masa abincin kari da zai fita shi, tunda ranar (office) ce.
Da wuri ya shirya don ya ba ta haushi, duk saurin da ta yi ta gama tana fitowa daga kitchen din ta ga ficewarsa daga falon. Da sauri ta koma kitchen ta dauko basket din, amma tana fitowa yana yin reverse zai fice daga gidan ga Danfulani ya wangale masa get. Yana hango fitowarta ta madubin motar har tana tuntube don sauri, ya fizgi motar da gudu ya fice daga gidan. Allah ne ya so ta kananan duwatsu ne shimfide da harabar gidan bakidaya, la-shakka da ta sha kura.
Kasa daurewa ta yi sai da ta yi hawaye, sabon salon da zamansu ya dauka ke nan. A ganinta laifin da ta yi bai yi kamarin da zai yi wannan fushin ba. A kan gaskiyarta ta ke. Yaushe ta tashi daga matar wucin-gadi zuwa parmanent wife? A cikin ajandarsu babu auratayya. Ba kowa ya fahimtar da ita wannan shi ne aure ba, shekarunta da kwakwalwarta ne. Abin da ta ke ji a kan Abdulazeez ma zuciyarta na son fahimtar da ita maanarsa da gangan ta ke kin karba. Idan wannan alamari da Abdulazeez ya bijiro a gare ta shi ne aure, hakika auren abu ne mai matukar nauyi kwarai, kuma zai iya ruguza duk wasu tubala da suka gina auren nasu a kai, tunda ba zaa fara don a daina ba. Ga shi ta sha alwashin taimakawa Abdulazeez ya samu abin da yake so ya cika burin rayuwarsa.

*****
Kwanaki sun shura ana wani irin zama mara dadi tsakanin Abdulazeez Dakata da matarsa Hafsat-Suhaana. Shi yake fushi da ita ba ita ke fushi da shi ba, fushin da in zaa daura masa wuka a makoshi a tambaye shi dalilinsa ba zai iya fada ba. Hafsat ta fi shi gaskiya in gaskiyar yake so. He attempted to cross the limit, ita kuma ta ankarar da shi. Me ye laifinta fisabilillahi? Ya daina cin abinci da ita, ya daina hira da ita. Ya daina zaman gidan.
Shakuwarsu da Sagir da iyalinsa ta karu a dalilin yawan zuwa gidan da yake yi yanzu don debe kewa, ko gidan iyayensa. A ganinsa janyewa Hafsat shi zai ceto shi daga katoton ramin da zuciyarsa ke son jefa shi, ramin da in ya kuskura ya fada sai ya yi tsalle dubu bai iya fitowa daga cikinsa ba.
Dole ya lallashi Muazatunsa suka shirya domin ya yarda har da nisa da ita cikin dalilan shakuwarsa da Hafsat, shakuwar da ba za ta haifar da Da mai ido ba, sai tarin nadama.
Sau-tari ya kan samu kansa cikin zurfi a tunani, Hafsat matarsa ce da addini ya halasta mishi iyaye da duniya bakidaya suka shaida. Yana da damar kusantarta no matter what, rashin samun damar hakan na iya jefa shi cikin wani hali a yanzu da yake tsananin bukatar mace a tare da shi. Ya ture komai ya karbi hakkinsa, shi ya ga abin da ya gani, ba yarinya ce kankanuwa ba irin daukar da yake yi mata. Ko protest din da ta yi masa ya nuna Hafsat na da wayonta, ta san abin da ta ke hangowa a cikin aurensu duk da tana da feeling a kansa wanda in ya yi rantsuwa ba zai yi kaffara a kan hakan ba. Tana da wani feeling na daban a kansa a yanzu bayan aurensu da zamansu tare na tsayin watanni, zuciyarsa ce ke karyatawa da gangan. Da hujjar cewa; yarinya ce, shekarunta ba su kai ta bambance da abin da zuciyarta ke so ba, sai wanda aka karkatata a kai.

(Anya kuwa Abdulazeez?).

Shi da kansa ya soma saukowa daga dokin fushin nasa ba tare da kowa ya lallashe shi ba. Ganin halin da fushin nasa ya jefa Hafsat. Ta shiga cikin matsananciyar damuwa da rashin walwala, in bai yi kuskure ba zai ce har ramewa ta yi jiya da ya saci kallonta tana gyaran falon, a lokacin yana zaune tsakiyar 3-seater ya mike kafafunsa da system a kan cinyarsa yana duba wani aiki. Amma duk da haka ya sa a ransa zai rage kusancinsu don tserar da kwangilarsa. Daga jibi Alhamis zai soma azumin tadauwai don samun lafiyarsa.
Washegari suka wayi gari da baki na ba-zata. Mammah da Baba Azumi, Ismael ya tuko su ya kawo su. Shi bai fito ba ma. Fitowarsa daga wanka kenan Danfulani ya kira shi ya sanar da shi, wai suna da baki ga su zaune a cikin mota sun ce daga Asokoro ne. Bai tsaya goge ruwan jikinsa ba ya sanya kaya, bakin wandon Jeans da shudiyar T.Shirt yar gidan Nordstrom. A gurguje ya fito don ya san babu wasu da ya sani a Asokoro sai iyayensa.
Ilai-kuwa, Mammah da mai aikinta Azumi da kaninsa Ismael ke fitowa daga mota.
Mammah!
Ya fada cikin bayanannen farin ciki.
Karasawa ya yi da sauri, shi ba abin ya rungume ta ba ta ce ya yi girma, shi kuma a yau ban da rungumar bai san me zai yi mata don nuna mata jin dadinsa ba da tako kafarta muhallinsu.
Hannayenta biyu ya kama, You arehighly welcome to our home Mammah.
Murmushi ta yi ta kwace hannunta tayi gaba, ya russuna ya gaida Azumi, ya ba wa Ismael hannu, ya karbi handbag din Mammah ya shige cikin gidan da sauri yana kwala wa Hafsat kira, Hafsa! Hafsa!!
Mammah ta ce, Wannan kira haka ai sai ka ba ta tsoro. In ka kyale ta har dakin zan isko ta.
Kwance ta ke lamo a cikin quilt kasancewarta mai yawan son dumi ko da gari babu zafi, kanta a kan filo ta cure gashin kanta a gefe, kwance ta ke kawai ko wanka ta kasa tashi ta yi saboda nauyin zuciya. Ba tunanin kowa ta ke ba sai na Abdulazeez din da ya hana zuciyarta zama lafiya a duk kwanakin nan, da tunanin hanyar da za ta bi ya daina fushi da ita. Kamar daga sama ta ji yana kwala mata kira da wata murya kamar ba tasa ba. Kasa amsawa ta yi, amma ta mike zaune cikin faduwar gaba. Sai ga shi ya shigo dakin, da sauri ya iso gare ta, har gadon ya isko ta ya zauna a bakin gadon. Hannunsa daya ya nutsa cikin sumar kansa ya iko hannunta da dayan ya dube ta cikin ido.
Mammah ce. Don Allah Hafsat ki rufa min asiri, mu koma shirinmu na dade da hucewa wallahi.
Yadda ya marairaice yana mata maganar ya yi balain ba ta dariya. Sosai ta dake ta dauke idonta daga kansa jin wani abu na fizgar zuciyarta daga cikin kwayan idanunsa. Ta rasa dalilin da ba ta iya jure kallon idanun Abdulazeez masu dauke da wani maganadisu da ba ta taba ganinshi a idon kowa ba. Hannayenta biyu ya kamo ya matse su sosai cikin nasa.
Kina jina Hafsa? Don Allah ki manta komai, babu lokacin magana save it, za mu yi ta in sun tafi. Duk wani punishment ki tanadar min zan dauka, amma ki saki ranki don Allah.
Daga kanta ta yi alamar ta ji, kuma ta amince. Sai jin sallamar Mammah sukai a bakin kofa, da sauri Hafsat ta janye hannayenta daga cikin nasa.
Mammah ta yi kamar ba ta gani ba.
Ba dai sai yanzu ki ka tashi daga barci ba?
Saukowa ta yi daga gadon da gudu ta yi kan Mammah ta rungume ta kankam. Abdulazeez ya ce, Ba ta jin dadi ne. Tun jiya ta ke fama da zazzabi, amma na ji yanzu ya sauka.
Ni ki cika ni kada ki kada ni.
Da kyar Mammah ta samu Hafsat ta cika ta suka zauna tare. Dakin ta ke bi da kallo, komai tsaf a gyare ban da gadon.
Ta ce, Zazzabi? Ba sai a je asibiti ba? Ana raina zazzabi ne?
Ta kafe Abdulazeez da ido. Sunkuyar da kai ya yi don gudun haduwar kwayar idanunsu. Ya san halinta sarai, kallo daya za ta yi masa ta karanto karya, ko gaskiya a kalamansa. Ba shi kadai ba har sauran yayanta.
Hafsat tuni ta yi kitchen ta soma tattaro abin saukar baki, kusan duk abin motsa baki da lemukan da suke da su a firji ta kwaso, Ismael na tsokanarta, Baba Azumi na tare mata.
Su matar gida manya, sai dai kuma babu wanka babu kwalliya.
Baba Azumi ta ce, Eh din, ta dai fi budurwarka mai kama da shamuwa da wasu kafafunta a bubbude kamar tayar mota, ko ba ta yi wanka da kwalliyar ba.
Dariya ya yi, ya ce, Wallahi Wasila ta fi Adda kyau, ga gayu, ga class, amma wannan tsami gayen sai Yaya ya hada da hakuri don bana jin ko girki ta iya.
Kumburi sosai ta yi tana hararar Ismael, Mammah da Abdulazeez suka fito.
Mommah, kin ga Illaila ko? Wai ni ce tsami-gaye?
Mammah ta ce, Ba dole ya ce miki tsami-gaye ba? Karfe goma na safe amma ba ki wanka ba, ba ki dafa wa mijinki abin kari ba, ba ki gyara gadonki ba balle ki yi masa kwalliya.
Kamar za ta fashe da kuka ta ce, Wallahi Mammah ina yi yau ne kawai.
Abdulazeez ya harari Ismael kasa-kasa. Mammah na fa gaya miki ba ta jin dadi.
Kana kare ta ne kawai amma ba zan yi miki uzuri ba Addah, shi ya sa ban gaya muku zan zo ba, zuwana na farko ga yadda na tadda ke.
Hafsat ta soma kuka kamar ta ce da Mammah in ta dafa abincin ba ya ci, ya daina kula ta dalilin hautsinewarta kenan, ta tuna rokon da ya yi mata yanzun nan na ta rufa masa asiri. Amma Abdulazeez ya cuce ta. Duk yadda ta ke hana idonta barci ta hada masa (verities) na abinci mai rai da motsi kullum sai dai ta zubar, ko ta bai wa maigadi, yadda ta ke kalkale gidan nan da kwalliyar da ta ke dandasawa ko kallo ba ta ishe shi ba yau daya sun tashi a banza! Ganin tana kuka zuciyar Hajiya Maryam ta tabu.
Abdulazeez cikin damuwa ya ce, Ishma, me ya sa ba ka iya wasa ba ne? Ni na ce da kai ba ta girki?
Ismael fa ba ya gajiya da tsokana, sai dai in bai ga abin fada ba, ya ce,
To Yaya a zubo mana man tunda an dafa?
Mammah ta janyo Hafsat jikinta.
Rabu da Ismael Addah, ni na dafo mana abincin saboda bana so ki sha wahala.
Ta dubi Baba Azumi, Karbi mukullin boot a shigo da coolers din nan gabadaya.
Ismaeel ya yi mata gwalo ya mike suka fita shi da Baba Azumi. Ta sake bara baki tana kuka, wai ya yi mata gwalo. Abdulazeez abin ya ba shi dariya, ya ce, Me ya sa ki ka zo da shi ne Mammah? Da Usman ki ka dauko.
Ka san Usman da gudu a titi, ni kuma bana son gudu shi ya sa na dauko shi. Na manta takura miki zai yi Addah.
Allah ba zan je gidansa ba, kuma ba zan je bikinsa ba. In ji Hafsat. Karaf! A kunnensa yana shigowa dauke da food-warmers din Mammah masu kyau,ya ajiyesu tsakiyar falon ya ce,
Ai gara kada ki zo din, balle ki koya wa Wasilata kazanta, rashin girki da rashin gyara.
Abdulazeez ya dau filon kujera ya jefa shi da shi. Filon ya cafe da hannayensa yana fadin, In ba za ki koyi gayu ba na rantse sai na yi wa Yaya budurwa yar gayu ko cikin kannenWasila.
Sosai Abdulazeez ya fusata, ya ce, Fita daga gidan nan Ismael, tunda babu gadonka a cikinsa.
Hannayensa biyu ya hada irin na rokon afuwa yana kallon Hafsat, Im so sorry uwargidan Ya Azeez. Amma kafata kafar uwata.
Mammah ta girgiza kai, Ni ma ba za mu jera ba, tunda kana fatan a yi wa Addata kishiya.
Na tuba na bi Allah na bi ku dukkanku. Baba Azumi ki gaya musu wasa nake, amma ai ita Adda ta sani ko a cikin kanne ita ta musamman din Illaila ce.
Zumburo masa baki Hafsat ta yi, Aah, yanzu ka daina sona.
Dariya ya yi wadda ta fiddo fararen hakoransa bakidayansu, Ke me ya sa ba wuya ne ki ce an daina sonki? An gaya miki ana fara son mutum don a daina ne? Youre special sis, ke da Yaya Azeez mutu-ka-raba takalmin kaza, ba yar gayu ba, ko yar sarkin Istanbul haka za ta ganku ta barku. Na tsaya miki sister, ko Mammah?
Mammah ta shimfida ledar cin abinci a tsakiyar falon gargajiyansu (African parlour) ta soma shirya plates da cokula ba ta kula shi ba. Can kuma ta ce,
In mutum ya ce shiga abin da ba ruwansa shi ne sanaarsa, ai sai kowa ya ja baki ya yi shiru ya zuba masa ido ya yi ta yi har Allah ya gajisshe shi.
Hafsa ta ce, Sosai kuwa Mammah.
Ta faki idon Mammah ta yi masa gwalo.
Abdulazeez bai kara kula su ba, wayar hannunsa yake daddannawa yana duba sakonni.
Funkason fulawa ne da sinasir da miyar agushi wada ta ji alayyahu da ganyen ugu da naman saniya, mammah ta dafo musu. Ita ta yi serving kowa. Daga Abdulazeez har Hafsat sun ji dadin abincin, sun bude ciki sosai sai ci suke don rabon kowannensu da cin kwakkwaran abinci cikin sukunin zuciya, tun fadansu. Babu wanda ya kara samun nutsuwar zuciya irin wanda ya samu a yau. Lallai UWA rahma ce, kuma komai girman Dan Adam yana bukatarta. Allah ka kara wa iyayenmu lafiya da nisan kwana mai albarka.
Mammah sarkin saido ta yi mamakin irin yadda suke ta narkar abincin nan. Ga shi da alama kowannensu ya rame idonsa ya fada, sai satar kallon junansu suke. Ko dai gaskiyar Ismael ne Hafsat ba ta girki? Amma da wuya hakan ta kasance don da ita dai ta san ba sakaran kiwo ta yi wa Addarta ba. Kusan koyaushe tare suke girki in tana gida, musamman da suka dawo Nigeria inda ba ta zuwa makaranta. Ta yi ajiyar zuciya har sai da kowa ya dago ya dube ta. Ta kudurce a ranta za ta binciki Hafsat ta tabbatar tana dafawa mijinta abinci ko ba ta dafawa.
Garin kalle-kallen Hajiya Maryam idonta ya fada kan kasaitaccen hoton Muazatu kafe a bangon gabas maso kudu na falon. Idonta ta kafa wa hoton tana son tuno inda ta san fuskar, kamar ta taba ganinta a wani wuri amma duk kokarinta ta kasa tuno inda ta gantan.
Adda wace ce wannan? Ta tambaya cikin mamaki tana mai nuna hoton da dan alinta.
A lokaci guda ita da Abdulazeez suka kai idonsu ga inda Mammah ke nunawa. Gudun jini ne ya katse a jikin Abdulazeez zuciyarsa ta yi wani irin bugu, wani rugugi ya ratsa a cikin kansa. Tun sanda ya kafa hoton don ya bakanta wa Hafsat bai kara tunanin zaman nasa kuskure ba ne, ko tunanin wani zai iya zuwa ya gani ya tambaya balle Mammah, mutum ta karshe da bai taba kawowa ba cikin masu ziyartar gidansa sabida fillancinta na alkunya.
Hafsat ya duba da sauri suka hada ido, ta yi saurin dauke kanta ganin ragaita da muzantar da ke cikin kwayar idanunsa. Saura kadan dariya ta kufce mata, amma ta hadiye.
Da ma an ce in za ka gina ramin mugunta ka gina shi gajere, ba ka sani ba ko kai za ka rufta. Halacci da yawa ya yi mata a rayuwar aurensu ta tsayin watanni shidda, ko da ya bata mata alherinsa ya rinjayi kuskurensa. Ta tuno ranar da ta san ko ita wace ce a cikinsu Abdulazeez bai kyamace ta ba, ya ce da ita; ita ba shegiya ba ce da ubanta a gaban iyaye da yan uwansa. Ya ce, uwar da ta haife ta ba ta yi kama da mutuniyar banza ba. Mace ce mai cikar mutunci, mai kirkin gaske. Ya sha alwashin nemo mata uban da ya haife ta da nemo mata yan uwanta na jini ya sadar da ita gare su cikin dan lokaci kalilan.
Kafin a yi haka Abdulazeez ya yi mata alheri da kyautayi mai yawa a cikin gidan nan... she adores him much... she respectshim alot... duk wata kulawa da ya kamata a baiwa mace a gidan aure yana bata kafin suyi fada. Samunbakinta ta yi da budewa yana bai wa mahaifiyarsa amsa ba tare da ta shirya kalaman a kan harshenta kafin ta furta su ba.
Kawata ce Mammah... sunanta Faizah.
Abdulazeez ya yi baya ya lumshe idonsa yana maida numfashi, ya dauki mintuna bai bude ba. Ya yi kasa da kansa, Hajiya Maryam mamaki ya kashe ta a zaune.
Kawa Addah? Shi ne ki ka makala ta a bangon dakinki? Kullum mijinki na tozali da ita? To bakya kishin mijin ne? Da gani ma wannan ai ta girme ki kuma da kyar in ba ta da aure? Ni yaushe ma ki ka canza hali har ki ka saki jiki da kawaye? Maza-maza sauke shi tun kafin in sabar miki.
Jiki na rawa Hafsat ta mike ta hau kici-kicin sauke hoton, amma ta kasa. Mammah ta juya akalar fadanta kan Abdulazeez.
Ban so zuwa gidan nan ba, ashe rashin zuwan nawa kuskure ne babba, kana ina Addah ta yi kawance da wannan mai soyayyen idon kamar an soya gyada marau-marau ba ka tsawatar ba? Dubi kirjinta duk rabi a waje bakinta kamar na karuwai an kafe ta a falonka wai matsayin kawar matar gida, kai kuma ka bari. Za ki sauke hoton nan ko sai na kwankwatsa shi a tsakiyar dakin nan?
Hafsat ta soma hawaye, duk

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login