Showing 1 words to 3000 words out of 133189 words
PAID PAGE 1️⃣
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
Tsammanin dawowarsa da kuma tsumayi na shiga sabuwar rayuwa da sabon gida ya hanani runtsawa. Da zarar na rufe idon sai na ji wani yanayi na dabam, mafi munin tunani shi ne na Zafeer, a wane hali yake ciki a yanzu? Ya rayuwa zata kasance masa a yanzu da lokacin da ya tabbatar da rabuwarmu? A take wata zuciyar ta raya min be kamata na yi tunanin wani namijin da ba muharramina ba a karkashin inuwar wani namiji da yanzu aljannata take karkashin takun kafarsa.
Forcing kaina na fara yi ina son bachi ya dauke ni, amman ya ki ya ba ni hadin kai, tun ina jin abun normal har na fara jin tsoro daman bana son kasancewar ina kadai a guri, kowa ma ya san wannan a gidanmu. Saukowa na yi a hankali ina kara rufe jikina da mayafin da Hafiz ya yaye min, na fara taka tile din mai tsananin sanyin da zan iya cewa na ac dake dakin ne, bakunta bata bar ni na karasa kofar da sauri ba, kamar wadda zata yi sata haka na isa gurin na rika kofar dakin na bude kadan na leka falon da aka kawata da kayan alatu, sai dai ban tsaya tantance abubuwan cikin sitting room din ba, domin ba su ne a gabana ba. Numfashin da nake ta hanci ne ya dawo yana fita ta baki saboda tsoro da kuma mamakin a ina Hafiz ya tafi? Na juyo a hankali na rufe kofar na dawo saman gadona na hau, na janyo filo na dora daga tsakiya, fitar numfashina na kara ta'azzara saboda tsoron da ya nufato ni. Rumgume pillow na yi sosai ina kallon agogon dake dakin, tun ina kirga dakika har na fara da mintu, awanni suka biyo baya. Shiru babu Hafiz babu labarinsa sai da, sanyin saukar hawaye na ji a fuskata sun gangara zuwa kunne kasancewar ina kwance ne. Ba ni waya balle na kira shi na tunatar da shi idan ya manta da ni, domin tsoro na neman haddasa min tashin hankali a cikin daren Amarya ci na.
“Ko dai ya manta ya auro ni? Ko kuma be gama rarrashinta ba har yanzu? Ko kuma wani abun ya faru?”
Na kasa samun amsar duka tambayoyina ukun, natsuwa kuma tace min yau ba ni tare da ke Noor, tsoro da kadaice ya maye min gurbinta, na yakure guri daya kamar marainiya. Ina kwance shiru akan gadon har karfe hudu na Asuba, misalin Biyar daidai na ji karar murda kofar an turo, tsoro ya saka ni kasa motsawa bana son na yi arba da abun da zai daga min hankali.
“Noor Amarya... A gafarce ni dan Allah ko kin yi bachi...”
Jin muryar Hafiz ya zabtare rabin tsoron dake tare da ni, cikin hikima da azanci na sauke ajiyar zuciya, na yi hanzarin rufe idona dake cike da kwalla domin na fahimci yana kokarin zagayo ne ta gurin da fuskata take facing.
“Bachi kike yi”
Ya tambaya yana taba ni, ni kuma ban motsa ba har sai da ya fara shafa fuskata yana girgiza ni a hankali, na bude idon sai dai ban iya tare hawayen idona ba har sai da suka zuba, sai da na yi hanzarin kai hannuna na share.
“Amarya tashi asuba ta yi...”
Ya riko hannuna yana murza yatsun a hankali, jiki ya dan fara rawa ina jin kamar babu dadi, ba kuma dan ba a taba rika hannun nawa ba, sai dan nashi rikon nake jinsa dabam wata kila saboda ina kallonsa a wani yanayi ne na dabam.
“Taso mu yi alwala”
Kamin na yi wani yunkuri har ya fara kokarin sauko da ni kan gado, ganin hakan ya saka ni saurin saukowa da kafafuwana na mike tsaye, sai ya yaye veil din da na lulluba da shi ya aje min kan gado, ya rika hannuna zuwa bandakin. Tsayawa na yi sai da ya fara alwala sannan ya juyo ya kalleni.
“Shigo mana ki yi alwala”
Na fara takawa kamar bana son isa gurin. Shi kuma sai ya fita ya ja min kofar bandakin. Sai da na gama kallon bandakin da ya banbanta da na gidanmu a komai sannan na tunna gurin da na ga ya taba ruwa ya zo na fara wanke baki, sai da na yi rabin alwala na ji ina jin fitsari. Na nufi bathtub na yi tsarin a ciki sannan na dawo na sake yin wata alwalar. Ko da na bude kofar na dakin na fito na same shi yana sallah, na yi zaton ko zai jira ne sai na fito mu yi sallah a tare kamar yadda nake gani a fina fina wasu ma'autan na yi.
Mayafina na dauka na lulluba sannan na tsaya kan sallayar dake shimfide a gafensa, na kabbarta sallah na fara. Bayan na sallame muka hada ido sai ya sakar min murmushi ya miko hannunsa ya kama hannuna ya rike.
“Good Morning, Amarya a gafarce ni, na miki laifi biyu”
Na sauke kaina kasa haka nan kawai nake jin kunya abun da ba halina ba. Kamar ya san tambayar kaina nake laifin a zuciyata sai na ji ya ce.
“Na farko na manta, ban aje miki kayan bachi ko na sallah ba, gaba daya hankalina na dauku Wallahi na manta sam, abu na biyu kuma wanda shi ya fi kowane laifi shi ne na tafiya na bar tsaleliyar amarya mai kyau irinki ta kwana ita kadai a gafarce dan Allah”
Na yi shiru kaina na kasa sai saurarensa nake.
“Na je na rarrashi Yayarki ne, tun abun yana kuka zallah har aljannunta suka tashi”
Na kalleshi da sauri cikin wani irin tsoro, domin idan akwai mai tsoron aljannu a dubiyar nan to a bayana yake.
“Aljannu?”
“Eh Wallahi ni ma ban taba sani tana da su ba sai jiya, karki so ganin yadda muka kwana a wahale sai da na riketa, da zarar na motsa sai ta fara ihu sai asuba ta samu ta yi bachin kirki, na tsorata sosai saboda cikin dake jikinta”
“Subhanallahi, Allah ya bata lafiya”
“Ameen”
Na ji ya sunbanci hannuna yana murmushi.
“Abubuwan da ya kamata mu gabatar a darenmu farko na angonci ni da ke ba mu samu yi ba, wata kila sai yau...”
Ya kwantar da ni kafadarsa yana shafa fuska mai soft face dina.
“Wata kila kin kwana a cikin tsoro a gidan da baki saba ba ko Amaryata”
Na yi shiru ban ce komai ba. Daga ni daga kafadarsa ya tashi na nufi gurin da wasu ledodi suke aje a jiye tun jiya ya dauko yana fadin.
“Wata kila kazar nan ta buga ma, madadin li bude ki ci ko bana kusa na ki ne fa”
A nan ma ban ji zan iya cewa komai ba saboda haka na yi shiru ina kallon ledodin da aka fito da su daga restaurant din mutumen da ya zama silar haduwa ta da mijina a yanzu. Ya bude kazar da kabejin ya fara bugawa yana wari kaza ce har uku da yoghurt sai wani kalar lemu mai kamar giya. Ya ci kazar kadan ya aje ya dauki tissue ya goge hannunsa.
“Ba zan bari ki ci wannan ba zata iya lalata miki ciki, sai dai anjima na siyo miki wata”
Nan ma ban ce komai ba, har ya mike tsaye ya kwashe ledodin ya nufi kofa.
“Bari na saka lemun yayi sanyi”
Na bishi da kallo har sai da ya fice sannan na juyo na ina jin idona suna cika da hawayen da ban san na minene ba. Ina jin motsin taba kofar dakin na yi hanzarin share hawayena gabana yana faduwa sosai.
“Amarya... Let go back to sleep kamin rana ta yi masu zuwa ganin amarya su fara zuwa”
Ya rada min a kunne sannan ya kai hannunsa ya riko fuskata ya juyo da ni na fuskance shi, sai dai ban yarda na kalli idonsa har ya mikar da ni tsaye, muka nufi gadon sai da ya fara zaunar da ni sannan ya zauna kusa da ni sosai ya sumbanci kumatuna na dama, a na hagun ne muka ji an bugar kofar falo. Ya kalleni da dan mamaki sannan ya sake ni ya mike tsaye.
“Ina zuwa”
Da ido na bishi har ya fice babu jimawa na ji hayaniyar yara da na tabbatar nasa ne domin garin be karasa wayewa balle na yi zaton ko na masu zuwa ganin amarya ne ko na makota.
“Abba Abba Abba”
Na ji suke ta fada, hakan kuma ya faranta min dai domin bana sha'awar kwantawa a gado daya da Hafiz, kamar yadda bana sha'awar yadda yake taba ni ko kuma sumbantar da ya fara a yanzu. Cikin dakin ya dawo yana rike da hannayensu su uku duka mata babbar ta fi kama da shi sai kuma karamar da ta zuba shagwaba. Muna hada ido da su na sakar musu murmushi ta biyun ta mayar min babbar kuma kallona kawai take.
“To ku gaishe ta mana”
Ya fada musu sannan ya zauna ya dora su a tsakiyarmu yana shafa kansu fuskarsa cike da annuri kana gani ka san yana jinsu sosai a ransa.
“Ina kwana”
Babbar ta fada sai na amsa murya a dakishe, ta biyun ma ta gaishe ni har ta ukun.
“Anty zaku rika kiranta daga yau kun ji?”
Suka daga masa kai, sai ya sumbance su yana murmushi ya kalleni.
“Wannan ce babbar sunanta Walida, ta biyun kuma Ikram sai kuma Haulat ita ce karama a yanzu”
Na yi murmushin dole ina kallonsu domin jina nake a takure. Kamar ya fahimci haka sai na ji ya ce.
“Noor baki son magana, kamar ba ke ba yadda Kareem yake ba ni labarinki sai na ganki a dabam, ko da yake.... Zaki saba zaki sake mana nan gaba”
Na yi murmushin yaƙe ina kallon kasa.
“Abba Momy tace ka hadawa Haulat breakfast ita bata jindadi, Haulat kuma ta fara kukan yunwa”
Na ji babbar tana fada, sai ya daga Haulat din ya dora a cinyarsa.
“Haulatu kin fara jin yunwa?”
Ta daga kai.
“Na san halinki ai sarkin cin abinci, daman ke kina rigan kowa karyawa acici”
Kannen suka saka dariya. Sai ya kalleni a yayin da ya mike tsaye yana dauke da karamar.
“Anty zo muje ki gaishe da yayarki ko ki yi mata ya jiki”
Na mike tsaye na dauki mayafina na saka sai Ikram ta kama hannuna hakan ya saka na dan ji kwarin guiwar tafiyar, yana gaba da yaransa biyu ni kuma ina daga baya tare da Ikram, har muka shiga bangaren matarsa wanda ya kasance iri daya da na nawa bangaren sai dai nata furnitures din da komai ya fi nawa kyau, a kudi kuma kana kallo zaka san nata ya fi nawa tsada nesa ba kusa ba. Hoton Hafiz da na yaranta da nata a naka manne a falon, wani gurin sun yi a tare wani gurin ita da yara wani gurin kuma shi da yara dayan kuma yaran ne su kadai aka yi ma hoton. Uwar daka muka shiga wato bedroom muka shiga, shi ya fara sallama sannan ni ma na yi na shiga. Zaune na hangota kafafuwanta a kasa, sam bata yi kama da mai aljannu ba, haka kuma bata yi yanayi da marar lafiya ba, sai dai tsoron aljannu ko mutane masu aljannu da nake ya hanani karasa kusa da ita, sai na zauna a kujerar dake kusa da kofar ina kallonta, shi kuma ya karasa ya zauna kusa da ita.
“Ina kwana?”
Ta yi min murmushi kamar yadda ta saba sannan ta amsa.
“Kin kwana lafiya Amarya? Ya bakunta?”
“Alhamdullahi”
“Madam ya jikin?”
Ta kalleshi tana wani irin lumshe ido ta bude kamar karuwa.
“Alhamdullahi ango”
Ta fada babu ko kishi sai ma murmushi da yake fuskarta. Ta kalli yaranta.
“Ku tafi falo, Abba zai zo ya hada muku breakfast yanzu”
“Okay”
Suka tashi suka fice daga dakin har karamar dake jikinsa. Kamar ficewarsu kawai yake jira sai ta kwantar da kanta a kafadar Hafiz tana kallona.
“Amarya karki ji haushi, dan Allah ki yi hakuri, jiya na kasa rike zuciyata ne shiyasa na yi kuka a gabanki ashe kuma wani abu zai biyo baya, bayan haka ban ma san na yi ba sai kusan azuba nan na samu kaina, uanzu haka jiri nake ji ina son na shiga bandaki na kasa”
“Ba komai Allah ya baki lafiya”
Na fada ina kallonta cike da tausayawa, shi kuma ya kai hannunsa ya daga ta daga kafadarsa yana tambayarta.
“Baki yi Sallah ba?”
“Na yi sallah ina son shiga bandaki ne na yi fitsari amman na kasa sai jiri nake ji”
“Lemme help you”
Ya fara kokarin kamata sai ta mike tsaye tana narke masa a jiki kamar wadda bata iya tafiya, ni kam sai mamaki yadda yake da kokari nake ba ma jin tsoron kar aljannunta su tashi ta makureshi. Bandakin suka shiga ya rufe, ina zaune shiru ina kallon furnitures din na ji an bude kofar kadan ta yadda za a iya jin sautin saukar ruwa ko murya. Kamar yadda na ji karar ruwan can kuma sautin karar kiss ya fara tashi. I was like da gaske kissing juna suke a bandakin? Mamaki da kunya suka baibaiye ni. Can kuma na ji ta ce.
“Dan Allah ka daina kai da kake da Amarya”
Kamar dai ta fada ne domin na ji, saboda muryarta yana daf da kofar bandakin. Ban ji me ya fada mata ba domin bana jin tashin nasa sautin, sai na ji ta kyalkyale da dariya sosai.
“Lafiya ta samu kenan tun da kika yi wannan dariyar”
Wannan karon na ji furucinsa domin yana daf da kofar ne a yayinta ita kuma ta bude kofar ta fito. Muna hada ido sai ta yi murmushi ya rika ta zauna bakin gadonta.
“Angon Noor ya kamata ka shiryawa amaryar abun karyawa, ni ya kamata na yi amman jikin ba dadi”
“Karki damu, yanzu zamu dafa wani abun”
Ta leko ni.
“Kanwata kuma yar'uwarta me kike son ki ci?”
Shi ma ya juyo yana kallona da alama amsata suke jira.
“Duk abun da ya samu, ba ni da zabi”
“Da dai kin fada zai fi, kar mu ba ki abun da ba shi kike ci a gidanku ba, ya bata miki ciki”
Furucinta na karshe sai na ji kamar bakar magana ta jefa min, kamar dai tana nufin babu a gidanmu na zo inda ke akwai. Hafiz na ji yace.
“Indan wannan ai ba matsala Noor tana son dadi sai idan bata samu ba, haka ne Amarya”
Na yi kamar ban ji shi ba, ban kuma amsa masa ba har ya mike tsaye ya karaso inda nake.
“Madam a ba ni aron amaryar nan ta rika min wani abu a kitchen na rage mata kadaici”
“Aa ban yarda ba, ba zaka gajiyar min da kanwa ba, kana ganinta ka san yar hutu ce bata saba wahala ba, ba yar kananan mutane ba ce ai, ka tafi kai da yaranka ku yi aikin”
“Amarya karki zancenta tashi mu tafi”
Na mike tsaye a zatona da gaske yake, sai na ji tana masa gargadi cikin wasa.
“Barrister, ka san doka ka san Shari'a ka bar min amaryata mu yi hira”
Ya juya yana kallonta da dariya.
“Au amaryarki ce ma?”
“Eh mana abun ka ai abuna ne, ko kana da ja? Yanzu na zubar maka da hakware”
Ya girgiza kai ya daga hannu sama like yayi surrender sannan ya fice daga dakin. Na yi murmushin zamantakewarsu ta burge ni sosai, yadda bata nuna min kishi bata nuna masa sai na ke jin kamar ta cancanci a bata kambun Sarauta na Matan Arewa.
“Amarya zauna mana, amman fa karki yarda ki ba da ni, ba'a yi ma Namiji rawar jiki, Na ga yana cewa ki tashi muje kika tashi, ai mace yar sarauta ce da isa, balle kuma ke da ba wani son shi kike ba, Wallahi ki rika ja masa aji, gaisuwa ma idan ba shi ya fara yi miki ba karki yarda ki fara gaishe shi, kullum shi yake fara gaishe ni da safe ya bincika lafiyata idan na tashi kalau, and most of aikin gidan yawancin shi yake yi ban cika yin aiki ba gaskiya, Barrister yana da kirki ba ko wace mace ke samun irinsa ba”
Na sauke kaina kasa ina tunawa da gaisuwar da yayi min da dazun. Ta gyara zama tana fuskata.
“Akwai abubuwa da ya kamata ki sani a tare da mijinki, sannu sannu zan fada miki In Shaa Allah, amman dai ina shawartarki ki rage rawar jiki, ba ayi ma namiji haka kara ki rika nuna masa alfarma kika masa fa kika aureshi damam can ba son shi kike ba kuma ya sani, kin gan ni auren soyayya muka yi ni da shi, amman ya sha wahala kamin na amince masa a shimfida, haka ni ma na sha wahala suma na biyu, ban taba jin azaba irin ta ranar ba, Barrister ba shi da tausayi a wannan bangaren”
“Suma kuma?”
Mamakin suma ya mantar da ni mamakin fada min sirrin aurenta da nake ganin be kamata ta yi ba.
“Kwarai kuwa? Kawayena ba su fada miki ba? Wata kila saboda sun san baki son auren ne, ba dan kar na daga miki hankali ba da sai na turo miki wasu littaffan kin karanta ki fahimci yadda abun yake domin na fahimci ke yarinya ce kurciya na damunki”
Gaba daya ta firgita min kwakwalwata, daman ni ina jin cewar ba zan iya yarda wani namijin da ba Zafeer ba ya aikata wani abun da ni balle kuma yanzu da ta fada min waye Hafiz ko kuma na ce Barrister kuma ai ba zata masa karya ba a matsayinsa na matarsa uwar yaransa kuma mace mai kirki.
“Amman...”
Ta yi hanzari yi min alama da na yi shiru tana nuna min kofar dakin da Barrister ya turo ya shigo, yana Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un.
“Me ya faru?”
Ta tambaya ni da ita muka kallonsa cikin tashi hankali.
“Momy ta kwanta dama, mahaifiyar Kareem ta rasu yanzu...”
“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”
Ta fada ni kuma na mike tsaye da sauri ina kuka.
“Wayyo Allah Kareem, ya rasa uwa na shiga uku... Allah kadai ya san halin