Showing 18001 words to 21000 words out of 133189 words

Chapter 7 - Taki Zaman Aure Book 2 Hausa Novel Complete

13 Dec 2024

252

ita duk ba mu taba ganin wannan abun ba”

“To waya saka miki? Ina kika samu? Ni zan dauko na saka miki a jaka?”

“Sai idan Aisha ce ta saka min saboda ta yi min sheri, Wallahi ban san na miye ba”

Ina fadar hakan sai ya sake ni, ya sauka daga kan gadon ya fita daga dakin. A nan an samu damar daukar maganin na duba na sake duba balloon din har biyu sannan na nufo falo na duba jakata da ke kasa sarka da yan kunne da na cire na saka a ciki tun a gida suna watse a kasa. Naira biyar ma ba ni da ita a jakar to a ina zan siye magani? Kuma maganin miye zan siya, wane chemist bayan cikin gidan mu ban san na taka ko'ina ba. Ban gama shiga tashin hankali ba har sai da Aisha ta shigo falon tare da Hafiz.

“Noor ni na saka miki magani da condom a jaka? Ta ina? Da zaki fita na karbi jakarki ne? Kuma ai tare kuka dawo da Barrister idan na saka miki wani abu a ciki zai gani, Kuma na rantse da Allah bayan fitarku ban shigo dakin nan ba, me zai saka ma na yi haka?”

Ta juya gurinsa da sauri ta zube kasa.

“Na shiga uku kar ta kashe min aure, daman burin yan matan yanzu kenan, Wallahi ba ni na saka, idan ni na saka mata shi a jakarta kada Allah ya ba ni abun da nake so Wallahi ba ni ba ce Barrister Innalillahi Na shiga uku...”

Ya rika ta ya mikar da ita tsaye, gaba daya sai suka daure ni na rasa ya zan zarga ita ko kanwata? Ko kuma shi da ya saka min jakar a lefe? Yanzu ta ya zan wanke kaina.

“Tafi bangarenki”


Ta kalleni tana kuka.

“Allah ya saka min gareki, na barki da Allah saboda kar a zarge ki shi ne zaki maida laifin a kaina? Ba ni ba ke Noor daga yau kowa ya tsaya bangarensa....”

Na kasa cewa komai sai kallonta nake hawaye suna sauko min kamar ba gobe. Ta rufe fuska tana kuka sosai ta fice daga falon, kamar fitarta yake jira ya juyo kaina.

“Ta rantse ba ita ta saka miki ba, daman makasudin kiran kenan, fada min ina kika samu wannan? Yanxu kika samu ko kin dade?”

Na yi shiru kamar wadda kalamai suka karewa.

“Ba magana nake miki ba?”

Ya sake daka min tsawa. Still ban iya ce masa komai ba, domin babu wasu kalmomi da zan hada na wanke kaina.

“Shiyasa auren mace mai mutunci mai tarbiya da natsuwa yana da dadi, ka aureki saboda na rufa miki asiri amman kullum matsala kike ba ni, ni ban taba samun matsala da matata irin wannan!”

Yana matsowa ina matsawa baya jira kawai nake ya kai min duka a jiki domin alamar hakannta bayyana a jikinsa da fuskarsa. Kwafa yayi ya nufi ledodin da muka shigo da su ya kwashe gaba daya ya fice daga falon. Ranar kwana ne amman be kwana a dakina ba sai ya kwana a dakin Aisha, ni kuma na kwana a falon cikin kunci da rudani mai tsananin daure kai.
A haka muka kwashe sati biyu be shigo bangare na ba, da girkina da ba nawa ba duk baya zuwa gurina, sai dai na hango shi ta window idan zai fita ko ya dawo. A lokacin damuwa ya fara shiga raina, na tabbatar Zafeer ba zai iya min haka ba, gashi Baba ya aurar da ni ga wanda bana so kuma be iya zama da ni ba. Kukan safe dabam na rana dabam da dare ma idan zan kwanta dabam ga abinci amman bana iya sarrafawa na ci saboda damuwa sai ruwan sha yi babu bread domin ya daina kawo min komai, wani lokacin kuma na dafa taliyar yara kadan na ci.

Idan na zauna da tunani sai na rasa wa zan kaiwa kukana, Baba zan je na fadawa ko kuma Mama ko kuma dai Kareem zan fadawa shi da yake abokinsa? Ko kuma gidan iyayensa zan bincika na fada musu ko kuma na zauna a haka? Na zuba masa ido? Gashi babu wani dan'uwa da ya sake zuwa gurina na balle na bude masa ciki na fada masa damuwata. Amman har zuwa yaushe zai yi ta fushin da Ni? Zuwa yaushe zai sauko? Agogon dakin na duba karfe biyu da mintuna na rana, tashi na yi na dauki green hijab dina na saka na dauki jakar nan da na yi fitar farko da ita na sake dauka na bude marfin madubina na dauko balloon din nan da maganin na saka a jakata na saka talkamina na fito falon na leka windows din waje ban motarsa ba hakan na tabbatar min da baya cikin gidan kenan. Bude kofar falon na yi na fita sannan na janyo kofar ba gabana na faduwa na sauka entrance din na nufi gate. Kamin na fice har wani gumi ke karyo min domin idan ya tare ni a kofar gate din ko hanya ban san me zan fada masa ba. Mai gadin ne ya bude min na fita dama ko hagu sai na rasa ina zan dosa can wata zuciyar ta raya min dama domin ta nan muka bi lokacin da zamu tafi gida tare da shi.








#KhadeejaCandyPAID PAGE 7️⃣


©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024

Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar

And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....


You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153


_______•••_______


Na yi tafiya mai nisa kamin na samu Napep na tara ya fada masa inda zai kai ni na shiga. Sai da ya fara tafiya sannan na fara sake saken idan na tafi gida me zan fada? Na nuna musu abun da ya gani a jakar tawa ko kuma dai na fada ma Baba cewar ya daina shigowa bangarena? Gidanmu zan tafi ko kuma na su gidan? Idan ma na ce zan tafi gidansu ina zan bi domin ban taba tafiya ba be kai ni kamin auren ba, bayan aure kuma ba mu samu kwanciyar hankalin da zai kai ni gidan ba. Wata zuciyar kuma na raya min na tafi gurin Mama kai tsaye sai dai kuma ita ma zan iya shafa mata laifi. Ya mace bata da gidan da ya fi na mahaifinta saboda haka na fada masa unguwarmu kai tsaye.
Har kofar gidanmu ya faka Napep din na fita na shiga gidan da sallama. Yaya na fara cin karo da shi yana wanki sai kuma Hana dake gaban murhu tana girki har yanzu da sauran kuna a jikinta domin na same ta babu riga a jiki.

“Yaya dan Allah dari biyar zaka ba ni zan sallami mai napep”

“Lafiya?”

Ya tambaya yana kallon yanayi na, domin na shigo gidan ne cike da damuwar da ta kasa boyuwa a fuskata. Na yo shiru be sake ce min komai ba ya tashi ya shiga dakinsa ya dauko dari biyu da naira dari ya miko min.

“Su kenan suka rage min, nawa ya kawo ki?”

“Ban yi ciniki da shi ba, bari na tambaya”

Na juya na fita, ta inda na yi sa'a ina tambayar mai Napep din nawa ya ce min dari uku sai na mika masa na dawo cikin gidan na nufi kofar dakin Mama na zauna.

“Noor kin rame? Ko baki da lafiya?”

Hana ta fada satar kallon Yaya na yi dake kallona sannan na ce.

“Har yanzu konan be warke ba?”

“Eh da saura, kin san wuta bata warkewa da wuri, kowa ma cewa yake na yi sa'a jikina yana da kyau ne”

“Ina Baba?”

“Dazun ya kawo cefa ne ya fita, anjima na san zai dawo cin abinci ai tun da yace ya gama da wuri”

Na sake kallon Yaya sannan na kalli rufin kwanon da aka yi da tsohon kwano a dakunan da suke kone, shi ma kuma daga dakinmu sai na Mama da take ciki na Yaya har lokacin a bude yake.

“Ashe an rufe”

“Eh Ya Nabil ne suka rufe shi da abokinsa, tsofin kwanon da suka kone ne suka rufe da su”

Duk maganar da nake Hana ce take amsa min shi dai be sake cewa komai ba sai dai ya kalleni. Ina zaune a gurin har ya gama wankin ya shiga yayi wanka ya fito Hana ta gama girkin ta zuba mana, na samu cin abincin da yawa kasancewar a tare muka ci da ita kuma muna ci muna hira. Bayan mun gama na yi alwala La'asar na yi sallah na zauna akan tabarma ina jiran shigowa Baba har lokacin na gagara fadawa Hana ko Yaya dalilin zuwan nawa. Yaya Nabil yana yi alwalar La'asar ya fice daga gidan, sai ya rage daga ni sai Hana ita din ma na kasa ce mata komai, gani nake kamar yayi wuri na fara fadar matsala wata kila ba za su yarda da ni ba. Shigowar Baba ta saka hantar cikina kadawa na kasa samun sukunin zama sai motsi na ke irin na marasa gaskiya.

“Ahh Yau Norriya ce a gidan na mu? Maraba maraba da zuwa Nooriyya an tuna da gida kuma?”

Na yi murmushin karfin hali na yi masa sannu da zuwa ya amsa Hana ta dauko masa kujera ya zauna kusa da ni yana kallona far'a kamar na zo masa da albishir.

“Ya gidan lafiya? Ina mijinki yana lafiya ko?”

“Lafiya Kalau Baba”

“Tun dazun kika zo?”

“Eh da rana na zo”

“Madallah kin ci abinci?”

“Eh na ci Baba”

“Haka ake so, Mijin na ki dai yana lafiya ko?”

“Eh Baba”

Na amsa cikin rashin sakewa, tsoron duka ko zagin da zan sha a gurin Baba ya hana ni fada masa damuwar da na zo da ita, haka na hade hannu ina kallon Baba yana cin abinci yana fada min wai kwanan baya ya kira Hafiz a waya be daga ba.

“Ina ta saurarensa yace zai kira ni kuma be kira ni, kuma na kira shi be daga ba”

“Wata kila baya kusa da wayar ne”

“Ni ma na yi tunanin haka, amman ai ya kamata ya kira idan ya ga kiran nawa, amman dai ba komai ai zai zo daukarki ko?”

“Eh zai zo, yace ma na tafi gurin Mama na dawo da wuri kamin ya zo”

Na yi karya ina jin kamar a gurin mahaifiyata zan fi samun sakewa na fada mata damuwa fiye da shi, da zai iya rufe ni da fada ko duka.

“Ah aha shi ne kuma kika zauna har yanzu? Tashi ki tafi mana ga yamma na yi sai ki dawo da wuri karki tafi ki zauna fa, ki dawo da wuri kar zo be same ki ba”

“Tohm Baba, amman ba ni da kudin abun hawa”

Ya saka hannu aljihu ya ciro tari bakwai ya ba ni.

“Tashi ki tafi, karki jima”

Na karba da hannu biyu na dauki jakata na mike tsaye ina kallon kanwata.

“Tafiya zaki yi”

“Eh ba zaki raka ni ba Hana?”

Jin haka ya saka ta shiga daki ta dauko hijab ta dora a saman zanen da take daure da shi, na yi ma Baba sallama da zimmar dawowa idan na tafi na fito Hana ta rako ni muka fito. Ko kadan ban yarda na daga kai na kalli kofar gidansu Zafeer ba, saboda ji nake kamar zan ganshi ne ko ya ganni hakan kuma ba zai mana dadi ba dukanmu. Har bakin Titi Hana ta rakoni na tari Napep ina tsaka da ciniki da shi na ji ta dafa ni.

“Noor Wallahi yanayinki kamar akwai matsala!”

“Akwai, ki min addu'a kawai Hana Allah ya min mafita”

“Ameen, je ki dawo sai mu yi magana”

Na daga mata kai na shiga Napep din. Yana tafiya ina hawaye har muka isa gidansu kakaninna. Farincikin ganin mahaifiyata da yan'uwanta da kuma su kansu yan'uwan mahaifiyata da suka yi farinciki ganina ya mantar da ni yar damuwar da na zo dauke da ita. Suka kawo min abinci har kusan hudu kasancewar gidan family house ne mai bangare dabam dabam irin na mutanen da da ake zama tare da jikoki da yaya da yan'uwa. Sai da na kebe da mahaifiyata sannan damuwa ta dawo min a take yanayi na ya canja.

“Ba zaki ci abincin ba?”

Mama ta tambaya, sai na kalleta ta yi jikinta ta yi haske kamar ba ita ba da alama hankalinta yanxu ya fi kwanciya fiye da lokacin da take gidan baba.

“Na ci abinci a gida kamin na zo”

“A gidan Baban na ki ko mijin? Ance ubanku ma aure zai yi? Kuma mai kudi wai Mama?”

Ta yi dariya.

“Eh ke ma ai Hana tace min aure zaki yi Mama”

“Eh In shaa Allahu jumma'ar nan ta sama za a daura auren, ina son daman sai an kusa na shirya na tafi na ga dakinki, yan'uwa sai yabawa suke, na san dai baki son auren amman ya miki komai Noor domin ubanki ba zai iya zuba miki wannan kayan ba, duk da dai ban gani ba amman ina jin ana ta yabawa”

Na yi shiru na sauke kaina kasa.

“ina abokiyar zaman naki kuna lafiya ko?”

Na dago na kalleta.

“Lafiya Mama sai dai...”

Sai kuma na yi shiru, ita ma shirun ta yi tana kallona.

“sai dai me? Noor karki fara dan Allah, yaushe aka miki auren balle har ace matsala ta fara shiga, shi zaman aure dan hakuri, kina kallon yadda na sha wahala gidan ubanki balle wannan dake kaunarki kamar ya hade, na san halinki Noor shiyasa tun farko na gargade ki, wauta da sakarci sun miki yawa, abun kadan zaki iya ganinsa ba daidai”

“Wata kila kuma ni nake da gaskiya Mama”

Na fada murya kamar zan fasa kuka, idona na tara ruwan hawaye. Sai ta hade min rai ta dauke kai.

“Bana son na ji, indai shi ya kawo ki gidan nan, to tashi ki tafi ba ki zo ganina cikin dadin rai ba sai zaki kawo min wani korafi? Je ki samu Babanki shi da ya daura miki auren ki fada masa, sai ni da kika raina, salon ace ni yanxu zan yi aure ke kuma na kashe miki aure? Noor kin san iya idon da yake kanki kuwa? Ana kalle da ke ana jiran wani abu ya faru, aure kasa da wata daya ki fara zuwa zaki fada min an miki ba daidai, daman miki daidai sai Allah Noor ki rufa ma kanki asiri ki zauna dakin mijinki, in har kika ce haka zaki fara da shi, to ko ba zaki taba zaman auren ba, ni bana son na ji komai tashi ki koma dakinki”

Kamin ta gama bayanin kuka ya gama cin karfi, haka na tashi ina share hawaye na saka hijabina na dauki jakata na fito gidan ana sallah magariba. Hanya na kama na rasa ina zanje, yanzu kuma waye zan fadawa kukana? Ko dai na tafi gidansu? Kuma da wane idon zan kalli iyayensa? Me zan fada musu cewar ya ga wani abu a jakata yayi fushi da ni? Wata kila ya ji haushin haka ko kuma su ma su kasa fahimta kamar yadda shi ma be min uzuri ba, gashi ban san gidan na su ba. Ko dai na koma gida? Kuma idan na koma haka zai cigaba da yi min na san zuwa yanzu kuma ya dawo be same ni a gidan ba. A take zuciya ta raya min na tafi gidan Kareem na fada masa halin da nake ciki na fada masa abun da abokinsa yake min wata kila zan samu mafita, domin ina jin babu dadi yadda ya wofintar da ni babu ruwanshi da ni akan laifin da ban aikata ba. Mai napep din da na shiga be sauke ni ko'ina ba sai kofar gidan Kareem. Na bashi kudin Napep 400 sannan na doshi kofar na buga mai gadin ya bude min.

“Dan Allah Kareem yana ciki?”

“Gaskiya yana ciki be dawo ba, amman dai iyalinsa tana nan”

Sanin halin matarsa na rashin maraba da mutane, da kuma kokarin fasa min kai da ta yi a wacan karon ya saka ban yi sha'awar shiga ciki na zauna a gefen gate din cikin flowers din da suka yi ma gidan ado. Ina zaune a gurin har aka kira sallah Isha'i aka sauko daga sallah sannan motar Kareem ya tsaya a gaban gate din yana horn. Na mike tsaye da sauri na nufi gilashin motar na kwankwasa sai ya sauke farin gilashin yana kallona.

“Noor...”

“Na'am”

Na amsa ina hade hannayena waje daya yanayina na karantar da duk wanda ke kallona damuwata.

“Ke da wa kika zo nan? And lafiya?”

Hawaye ya fara sauko min.

“Kareem ina cikin matsala, kuma ina jin kai kadai zaka iya taimaka min, dan Allah karka ce ba zaka saurereni ba, ina jin tsoron Baba na kasa fada masa kar ya kure ni ko ya min duka, Mama kuma ta ki ta saurare ni”

Ya dan tsaya kallona kamin ya ce.

“Shiga cikin gida”

Na wuce sai da na fara shiga sannan na shigo da motarsa ya faka kusa da ni, ya bude ya fito ya kalleni.

“Hafiz ya san kin zo nan?”

“Aa be sani ba”

“Me ya faru?”

Na hade yawu.

“Baya shiga bangarena yau kusan sati biyu, baya min magana matarsa ma fushi take da ni, ba ni da walwala Kareem gaba daya na ji na tsani gidan na tsani kaina”

Ya ciro wayarsa ya fara tabawa.

“Wani abun kika masa ko?”

“Ban masa komai ba, kawai dai wani abu ya gani a jakata ya fara fada....”

Na fada masa komai cikin kuka.

“Minene to?”

Na Cire jakar daga kafata na bude na dauko maganin da balloon din na mikawa Kareem.  Sai yaja baya da sauri kamar ya ga abun kyama.

“What the F**uk, miye hadin ki da wannan Noor”

Na kalli maganin na kalleshi.

“Na minene? Ban san maganin miye ba Wallahi, wannan ballom din ma ban taba ganin irinta ba, Wallahi Wallahi ban san ko abun miye ba Kareem”

“To ya aka yi kika samu?”

“Ban san ya aka yi ba kawai shi ya ganshi a jaka”

“Wannan maganin hana daukar ciki ne, wannan kuma Condom ne”

“To me zai hada ni da maganin hana daukar ciki? Wallahi ban san shi ba ban taba ganinshi ba ma, ban san inda aka siyarwa ba, shi condom din me ake yi da shi?”

Yayi shiru yana kallona.

“Bayan aurenki baki hadu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login