Showing 75001 words to 78000 words out of 133189 words
Chapter 26 - Taki Zaman Aure Book 2 Hausa Novel Complete
wai Kareem ya fada masa ya nemawa Ya Nabil karanta a Sudan. Farinciki ya cika ni a lokacin da Baba yake fada min Kareem yana neman izininsa idan ya aminta sai ya fadawa Ya Nabil din ya kai masa takardunsa na SSCE.
Sanin da na yi ba karamin dadi Ya Nabil zai ji ba, ya saka ni farincikin da na kwana biyu ban yi ba. Hakan kuma ya karantar da ni cewar Kareem yana da kirki ta wani bangaren, domin gashi ya danne kudirin mahaifina kuma yana kokarin nemawa dan'uwana karatu alhalin be hada komai da mu ba. Farinciki a gurin Yaya Nabil ba a magana kamar zai zuba ruwa kasa ya sha domin murna, daman abun da yake nema ne yana son karatu shi da Hana ba kamar ni ba.
Washe gari da safe Kanen Hafiz ya sake kawo min ziyara sai dai wannan karon ba, maganar gado ce ta kawo shi ba, ya zo min ne da tsaraba ta atamfa biyu da kuma turare sai sabulu da talkami da kudi 10k wai yana taya ni murna fita waka, kuma na yi hakuri da yadda yan'uwansa suka nuna min halin ko'ina kula. Na karba na yi masa godiya muka yi sallama na shiga ciki, bana tunanin ina da wata bukata ta kudi a yanzu wannan ya saka na dauki kudin na bawa Hana na ce ta kaiwa Mama idan ta tafi gidan, domin ita ce mai yawan zuwa ni ban taba zuwa ba domin an yi auren ne a lokacin da ba ni da halin yawo.
Abu kamar wasa, shiryen shiryen tafiyar Yaya Nabil Sudan ya fara, duk wani abu da za'ayi Kareem ne yake ba shi kudi yayi, har aka kammala komai within three months. Ranar da zai je yi ma Mama bankwana na bi shi muka tafi tare, ni da shi sai a ranar muka fara zuwa gidan.
Babba gida ne mai bangare kusan hudu, gida ne mai kyau da tsari Mama da kanta na san ba ta taba mafarkin aure irin wannan gidan ba.
Da muka shiga ciki sai ta zame mana kamar wata bakuwarmu saboda yadda rayuwa ta canja mata, ta yi kiba ta kara haske ga tufafi masu tsada kayan kallo kai har da dinning da ac kamar daman can Mama bata taba auren talaka ba, duk inda ta wulga kallonta nake kamar wata bakauya.
“Noor na zame miki sabuwa yanzu ko?”
Na yi dariya ina kallon plate din taliyar da ta aje min nama batsa batsa kamar wanke.
“Mama ina ta mamaki ne, ina kika hadu da wannan mutumen ne?”
Ta dan hade rai.
“Mutume? Toh idan ba zaki iya kiransa da Baba ba, ki kirashi da suna Alhaji kamar yadda kowa yake kiransa a gidan nan, wato ke dai sakarcin ki ba zai canja ba ko?”
Na yi shiru ina kallon Yaya dake cin taliyar, sannan na soma cin tawa. Rabin abincin kawai Yaya ya ci ya sha ruwa yace zai tafi.
“Da wuri Nabil na yi zaton sai dare, saboda Alhaji ya dawo ku gaisa, yana ta fadar ban taba gabatar masa da sauran yarana ba, be san kowa a cikinku ba sai Hana da ke yawana zuwa”
“Bana son na kai dare Mama, akwai guraren da ya kamata na tafi kamin ba bar garin nan, kuma kin ga kwana biyu ya rage min”
“To sai dai kai ka tafi Noor kuma zata tsaya sai ya dawo kun gaisa tukuna ta wuce”
Mama ta shiga dakinta ta dauko masa babbar leda cike da kaya sannan ta danka masa 20k tana ta sakawa Kareem albarka wai daman a yanzu tana ta tunanin wace makaranta zata nemawa tarin kudin da take shi take yi ma, amman gashi ya dauke mata nauyi. Bayan Ya Nabil ya wuce muka zauna da Mama muna hira take tambaya ko Zafeer ya ji rayuwar Mijina.
“Zai iya ji tun da iyayensa suna cikin unguwar, ko basa nan ma ai yan gulma suna nan, fitowar nan ma cewa suke ta yi hakkinsa ne”
“Zafeer yana sonki sosai, zai iya dawowa yanzu ma, wata kila kuma iyayensa su hana shi, ko da yake a can baya ma sun yi ta kokarin hana amman ya nace sai ke, gashi kuma an watsa masa a ido, Wallahi mahaifinku be kyauta ba”
“Baba ma da yace be yafe ba idan na sake masa magana, shi ne abun da ya fi damuna”
“Wai har yanzu? Toh ai Hafiz din baya raye kuma, yanzu idan Zafeer ya dawo ba zai bari ya aureki ba?”
“Ban sani ba, amman da kamar wahala saboda yana ganin Zafeer talaka ne”
“Haka ne, ubanki be ji wani yare sai na kudi, gashi babu mai iya ja masa liyi a dangi komai yayi daidai ne a idonsu”
Na daga kai ina kallon POP din falon.
“Taso mu tafi ki gaisa da mutanen gidan, suna ta tambayar, da kika fita wanka ma sai da matarsa tace zata tafi ta duba ki kuma Allah be yi ba”
“Ita bata kishi ne Mama?”
“Ana tabawa mana ayi mace babu kishi, amman boyewa ake na ciki na ciki, ita dai tana da kirki ba kamar wasu ba”
“Ko dai irin na Aisha take miki ba, haka take nuna min ba komai ashe wayo take min”
“Ke dai da halinki Noor, na san ki ba, kuma zamanmu a nan Alhaji ya fada mace kamar riga take a wuyansa duk wanda ta daga masa hankali cire ta kawai zai yi ya aje, duk tarin yaransa babu wanda uwarsu take cikin gidan nan, sai wannan matar da yaranta uku, sauran duk iyayensu sun fita, ni ma sai bayan auren nake ji, wata kila shiyasa ta kama kanta”
Ina jin haka na san an gudu ba a tsira ba ne, kenan ita ma idan ta yi masa ba daidai ba zai iya sakinta. Daga bangaren Mama muka fito muka shiga bangaren matar da take gidan a yanzu. A cike muka samu falon da mata da maza, Mama ta yi sallama suka amsa suna gaisheta da mutunci.
“Noor Ya hakuri?”
Wata budurwar da ban waye ta ba ta fada sai na amsa da Alhamdullahi na gaishe da Hajiyar.
“Lafiya Kalau Noor, an fita wanka ko? Tohm Allah ya bada hakuri ya kawo na gari”
Mama ta amsa da Ameen.
“Alhaji ne be santa ba sai mita yake ina boye masa yara, tare da yayanta take jibi zai wuce Sudan gurin karatu, ya zo bankwana amman be tsaya ba, ita kuma ba ce ya tsaya ta gaisa da yan gida”
“Ta kyauta gaskiya, da ma dai kin maido nan kila zata fi jin sanyi kin san gidan na mu cike yake da mutane”
“Mahaifinta ne ai be yarda ba, ko takaba a nan ya so ta yi amman uban yace ba zata yi ba”
“Kin san wasu mazan akwai kishi”
Haka dai suke ta hirarsu ni dai kaina na kasa ban dago har sai da na ji an bude kofar falo alamar mutum ya shigo. Dagowar da na yi sai muka yi ido hudu da Safeena tana dauke da cikinta da be gama girma ba. Bata kallon kowa sai ni ni ma kuma bana kallon kowa sai ita muka rika kallon kallo wata kila ita ma tana mamakin ganina ne kamar yadda nake mamakin ganinta. Gidansu ne? Ko kuma zuwa ta yi? Ko kuma dai tana da wata alaka ce da mutanen gidan?
“Kin dawo Safeena?”
Hajiyar ta fada sai Safeena ta amsa mata ba tare da ta kalleni ba, har lokacin ni take kallo.
“Na dawo Hajiya, na karbo files din gobe zan tafi asibitin na kai”
“Toh Allah ya taimaka ya raba lafiya”
“Ameen”
Ta amsa sannan ta dauke idonta ta zauna a kujerar dake facing dina, sai kuma ta sake dasawa daga inda ta tsaya.
“Anty Safeena kin santa ne?”
Na kalli mai tambayar wata kila su ma sun lura da kallon da take min yayi yawa. Ga mamakina sai ta amsa da cewar
“Aa ban san ta ba, wacece hala? Ta yi min kama da wata kawata ce ta yarinya”
“Noor ce yar wajen Anty Amarya, wanda mijinta ya rasu”
“Allah sarki Allah ya masa rahama”
Ya juya tana kallon Mama dake amsawa da Ameen sannan ta sake kallona. Har muka baro bangaren babu abun da take sai kallona kamar wata bakuwarta. Ban kuma san dalilinta na boye cewar ta san ni ba. A bangaren Mama na koma na zauna har dare ina jiran dawowar mijinta saboda mu gaisa, be shigo ba sai bayan Magariba a lokacin da ake hada hadar Sallah Isha'i.
Na yi mamakin yadda yayi murna da farinciki ganina babu wata kyama, har na na yi sha'awar ina ma ace shi ne mahaifina ba Baba ba, zaunawa yayi a falon yana ta min nasiha akan hakuri da rayuwa na halin da na samu kaina da kananan shekaru, na yi masa godiya ya saka hannunsa aljihu ya ciro 10k ya ba ni.
“Aa na gode”
A bakin gaskiya ta ba zan karba ba, domin ko na karba ban san miye zan yi da su ba a yanzu. Sai dai na lura hakan be masa dadi ba domin rufe ni yayi da fada a dole na karba na yi masa godiya.
“Tafi bangaren Hajiya ki ce na ce cikin yaran nan duk wanda yake nan ya sauke ki gida”
“Tohm”
Na mike tsaye na yi ma Mama sallama sannan na fice daga falon yana ta kallona. Bangaren Hajiyar na dawo na sanar mata abun da Alhaji ya fada sai mutumen dake tsaye a gabanta yayinda take zaune ya juyo ya kalleni. A nan ma wani mamakin ya kara kama ni, mutumen nan da ya taba yunkurin biya min kudin siyayyar da na yi a wani dare da muka fita tare da Hafiz.
“Kamar na sanki?”
Na bude baki kamar zan yi magana sai kuma na yi shiru, ban san me zan ce ba, ni dai ina da saurin gane mutane shiyasa na gane shi.
“Noor ce Yar wajen Anty Amarya ce, ita ce wadda mijinta ya rasu”
“Ai ban sani ba, Allah ya jikanshi da Rahama”
“Ameen, ku tafi tare sai ka sauke ta ka wuce, Noor bari ga Abdull zai fita yanzu sai sai ya wuce da ke, ki jira shi a waje”
“Okay”
Na juya na fito daga ciki, ban san wacece motarsa a cikin motocin gidan ba dan haka zauna a balcony har ya fito.
“Kika zauna a kasa?”
Bance komai na na mike tsaye na bi bayansa muka isa gurin wata sabuwar mota, sai da ya fara shiga sannan na bude na shiga front seat. Ba tare da yace min komai ba yayi reverse ya fice daga gidan.
“Ina ne unguwarku?”
A lokacin da na dago sai na ga idonsa akaina suke. Na fada masa na sake maida kaina kasa kamar ba ni ba. Na ji lokacin da wayarsa ta yi kara ya amsa.
“Hello Safeena...”
Sai kuma yayi shiru, yana sauraren abun da ake fada masa.
“Yanzu na fito gida, amman zan biya ta can, sai na zo miki da shi, shi kadai kike so ko da wani abun?”
Na yi shiru ina saurarensa kamar wata Munafuka kamin na ji ya ce.
“Okay sai na dawo”
Ya aje wayar ya dago zan kalleshi idona suka fada cikin nasa da sauri na dauke kaina ina jin sautin murmushinsa. Ban sake kallon gefen da yake ba har muka isa unguwar.
“Ka sauke ni a nan unguwar bata da kyau can ciki”
Na fada.
“Karki damu, amanarki aka ba ni sai na kai ki har gida”
Yadda ya fada haka ya aiwatar har kofar gidanmu ya isa da motarsa ya faka, ni kuma na bude na fito zan rufe kofar ya ce.
“Ba godiya”
Ban ce masa komai ba na rufe motar, na gode masa sai ka ce rokonsa na yi ya kawo ni. Sai da na shiga gida sannan na ji motarsa ta bar kofar gidan.
KAREEM POV.
Yana gama sallah asuba ya shiga kitchen hadawa yaransa breakfast. Domin Yusura bata musu komai tun da ta dawo gidan, Kullum shi zai hada musu breakfast ko kuma ya saka aika musu daga restaurant dinsa kamin su tashi break.
And now cooking is one of his favorite things, yana samun nishadi a girkin, musamman idan yaran suka farka suka same shi a kitchen suna hayani yana aikinsa har ya gama, ya karya tare da su wani sa'in kuma ya zuba musu na su, ya tafi da nasa a office ko kuma su su tafi da na su school shi kuma ya ci a gida. Idan ya fita sannan Yusura take saukowa ta gyara ko'ina ta dora na rana. Tun da ta dawo gidan be taba leka dakinta ba, be taba ce mata uffan ba, ita ma kuma bata bari sun hadu ba, da zarar ta ji motarsa ko ta san lokacin dawowarsa sai ta shige dakinta.
Yau ma sai da ya raka su har gurin bus sannan ya dawo ya zauna ya ci nasa breakfast. Bayan ya gama ya mike tsaye ya shiga dakinsa yayi wanka ya shirya cikin kananan kaya ya fito yana rike da lab coat dinsa da wayarsa sai kamshi yake zuba. Yayi kyau sosai ramar da yayi ta kara masa kwarjini da haifa. Sai da ya fice daga falon sannan Yusura ta sauko a zatonta ya fice gaba daya, dinning ta nufa ta tsaya tana kallon kayan karyawar da ya shirya, biredin da ya gasa ta dauka taba tabe baki ta shinshina ta aje.
Sannan ta ja kujera ta zauna ta bude flask din ruwa zafi, a daidai lokacin Kareem ya turo kofar falon ya shigo domin daukar wallet dinsa da ya manta a dakinsa. Kallo daya yayi ma gurin da take zaune ya dauke kai ya haura sama ya dauko wallet dinsa ya sake fice. Yusura bata taba jin kunya irin ranar ba, bayan amincewa da aurensa da ta yi wannan ne abu da na biyu da take bakinciki a rayuwarta, ji ta yi kamar ta fasa komai na gidan dan bakinciki.
Tuki yake a hankali har ya isa asibitin, ya faka motarsa a gurin da aka rubuta Dr Kareem sannan ya fito ya dauki kayansa ya rufe motar ya shiga cikin Babbar asibiti ana miko masa gaisuwa yana amsawa. Office dinsa ya shiga ya fara duba takardun dake gurin sannan ya fita ya fara duba marar lafiyar da aka aje da ya kamata ya duba su.
After ya gama ya dawo ya zauna a office dinsa patient din dake shigowa suka fara shigowa yana dubata. Third person da ta shigo ita ce Safeena, tana sanye da dogon Hijabinta har kasa sai dai hakan be boye cikin dake jikinta, har ta zauna ita yake kallo. Sai da ta aje jakar dake hannunta sannan ya jingina baya ya kwanta jikin kujerar yana kallonta.
“Wai ke wace irin yarinya ce Safeena?”
“Ni din wata yarinya ce, mai wuyar warke ciwo, wata yarinya ce da ka koyawa soyayyarka kuma kake kokarin guduwa bayan ka yaudareta da farko”
“Gargadin da na yi miki, da kuma tazarar da na baki daga lokacin da muka yi haduwar karshe zuwa yau bata fahimtar dake, na rumgumi kaddarata, ke ma ki rumgumi taki?”
“Ka rumgume kaddara saboda Yusura tana sonka tana kyautata maka a yanzu? Ko kuma daman can karya ka yi min kace bata kula saboda kullum ka rika samun biyan bukatarka da ni? Ka yi breaking heart dina da farko yanzu kuma bayan na saba mu'alama da kai na saba da kwanciya a kirjinka na saba da soyayyar kake tunanin sake guduwa ka bar ni?”
Ya mike tsaye daga zaunen da yake ya nufi windows dinsa ya bata baya.
“Kana da kyau, Kareem kana da kudi amman duk wannan be tabbatar min da ina sonka ba sai da mu'amala ta hada mu, all this while na kyale ka ne saboda ina dauke da cikin nan”
“Me kika zo yi yanzu? Tashi ki fice daga office din nan”
“Baka da wannan damar ba saboda da kai na zo ba, saboda cikin nan ne, na dawo da awon cikin nan a nan ne, a nan zan yi ta zuwa har zuwa lokacin da zan haihu”
Ya dafa Window ya rike kansa.
“Namiji zan haifa suka ce, kuma ina alfahari da haka”
Kareem ya dauki lokaci a haka kamin wani tunanin ya zo masa sai ya juyo da sauri ya kalli cikin na ta sannan ya kalli fuskarta, sai ta yi masa murmushi.
“Fita ki bar office din nan”
Ya nuna mata kofar, zata sake magana da daka mata tsawa har sai da ta zabura.
“Fita ki bar office din nan na ce”
Ta mike tsaye da sauri ta dauki jakarta tana kallon yadda ya hade fuska kamar be taba ganinta ba, ta fice daga Office din. Dawowar yayi ya zauna kan kujerar ya dafe kansa ya runtse ido yana numfashi da karfi, ya girgiza kai kamin ya daga hannunsa ya buga a tebur din yana jin wani irin bakinciki marar misaltuwa...
It could be a joke maybe tana gwada shi ne, if not ai tana da hankali matukar ba wata manufa take da ita akansa ba ba zata taba sha'awar haihuwa da shi alhalin tana da aure ba, ta dauki dawainiyar cikin da ba na mijinta ba ta kai masa yayi komai, ba zata fara ba. Abun da zuciyarsa ta raya masa kenan har ya ji ya samu saussaucin cigaba da aikin da yake. Sai da lokacin tashi aikinsa yayi ya tuna da ba shi da abokin hira ko shawara a yanzu domin Hafiz is no more balle ya fada masa hasashensa ko damuwarsa.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0
PAID PAGE 2️⃣0️⃣
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
Rumgume hannayena na yi ina kallonsa with my innocent face.
“Besty how are you?”
Ya tambaya yana daga kai ya kalli harabar unguwar.
“I'm good and you?”
Ya daga gira not happy not sad.
“I'm not fine”
Na dan matsa kusa da shi.
“Me ya same ka?”
Sauke kai yayi kasa sannan ya ce.
“Bestyna kamar kin taba fada min sunan wanda zaki aura ko?”
“Eh Abdull”
Ya dago ya kalleni.
“Yana da mata kika ce idan ban mata ba”
“Eh da yara uku matarsa ya haihu na hudu”
Ina