Showing 93001 words to 96000 words out of 133189 words

Chapter 32 - Taki Zaman Aure Book 2 Hausa Novel Complete

13 Dec 2024

278

kina nema”

Ta hade abu da karfi.

“Babu amfani Daddy zai sake sakawa ka maida ni”

“Wannan yanci ne na har abada, it mean forever...”

Ta sake dubansa kamar yadda yake kallonta.

“Ina mai baki hakuri akan duk wani abu da na yi miki, wanda kika sani da wanda baki sani ba Yusura, bankwana ne na har abada”

Her heart and body star shaking idanuwanta suka tara hawaye.

“Na gode da kika taya ni aje farinciki mahaifiyata har sai da ta bar duniya. Yanzu kam kina da yancin ki auri wanda kike so ki yi rayuwar da kike so”

Ya juya ya fara tafiya, ta juya tana kallonsa? Me yasa yau ta ji dabam? Ta dade tana jiran zuwan ranar amman ta kasa farinciki, wacam karon ta jidadi da ya sake ta amman ta kasa farinciki.

“Yaran fa?”

Ya juyo ya kalleta hawaye ya gani suna fitowa daga idonta suna zuba a fuskarta.

“Zan kula da su”

“Za su fi jindadin zama a gurina”

Ya taka zuwa inda take tsaye.

“Idan haka kike so, zan minta, but only on one condition, no matter how happen a raye ko a mace zaki fadawa yaran nan cewar mahaifinsu yana kaunarsu, duk wani abun bacin rai ko bakinciki da zai biyo baya ko ya biyo i still love them, ki fada musu mahaifinsu yayi kokari ganin ya tsare duka hakkinsu sai abun da ya fi karfinsu”

Ya juya ya nufi kofa sai ta risina kasa ta kira sunansa.

“Ka yafe min Kareem, na cutar da kai na sani, kiyayya bata bari na yi biyayya ba”

“Komai ya kare yanzu Yusura it over now”

Ya amsa mata ba tare fa ya juyo ba ya fice daga falon. Yana shiga motarsa ya murza key mai gadi ya bude masa gate ya dauki hanyar da zata sadashi da gurin aikinsa. Be yi nisa da gida ba hudu ya rufe masa ido kansa ya fara juyawa yana ta kokarin controlling motar amman ya kasa.



NOOR POV.

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”

Abun da na fada kenan a lokacin da na farka da karfi, sakamakon mummunan mafarkin da na yi. Wai muna tafiya a jirgi sai ya muka fado kasa ni har da ni ciki, na bugi icce har sai da hankalina ya gushe. Addu'a na yi na neman tsari daga mummunan mafarki. Na yi a'uzubillahi har karshe na tofar dama na sake yi na tofar hagu, sai haki nake kamar wanda ta yi yaki, hannu na kai na lalaba ban ji Abdull ba, sai na sauka daga kan gadon na kunna wuta na nufi bathroom din da nake jin motsin ruwa na tsaya jiran ya fito na shiga.

Da na lura ba shi da niyar fitowa sai na tura kofar na fara lekawa babu kowa a ciki, shiga na yi ciki da mamaki, tab din ne a kunne ruwa na zuba kadan kadan amman babu kowa a ciki. Kashewa na yi na bayan na gama fitsari wata kila ya manta ya bar shi a kunne ne. Sai da na nufo gado na zauna sai kuma wata zuciyar ta tambaye ni ina ya tafi? Bargon na sake yayewa na sauko da kafafuwana ina mikewa tsaye sai gashi ya shigo dakin.

“Ina ka tafi?”

“Ruwan na ji na hada tea, ina zaki ke?”

“Ai dai ba zan bata ba a gidana ko? Idan bana dakin nan ina falo ko kitchen”

Ya hauro saman gadon ya kwanata rai a bace kamar an masa wani abun, har ya manta be kashe wutar ba, wata kila tambaya ta ce ta bata masa rai.
Sauka na yi na kashe wutar na dawo na kwanta.


It's not Free pay 500 to

Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008

And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0



Washe Gari na tashi da wuri saboda zan tafi asibiti, dan haka na gyara da wuri na fito falo, ina jin motsin Hana na nufi kitchen din na dan rikawa mata aiki.
Ina tsaka da kashe socket ta yi min wata magana da ta saka na kalleta.

“Noor ina son na tafi gida”

“Me yasa Baba ya sake magana ne?”

“Aa kawai dai ina son gida yanzu, na fi jindadin zama gida sama da nan”

Na juyo da kyau na fuskance.

“Hana wani abu na yi miki ba daidai ba ko Abdull yayi miki?”

“Aa ba ko daya, kawai dai na fi sha'awar tafiya gida ne”

Na dan jimm ina mamakin dalilinta na fadar haka a yanzu, daman na lura yanayinta gaba daya ya canja.

“Hana mafarki kika yi marar kyau ko me?”

“Ba komai ni dai kawai ina son na tafi gida”

“To kije ki dawo ko kuma ki koma gidan gaba daya?”

“Gaba daya dai nake son na koma”

“Karatunkin fa?”

“Zan hakura na san idan naje can Mama zata iya sakani idan Baba ya yarda”

Na matsa kusa da ita domin babu ta yadda lafiya zata saka ya yanke karatunta ta koma gida haka nan kawai sai da dalili.

“Hana na san muma yawan samun tsabani da ke a gida, amman nan gidan aurena ne, idan kina ganin akwai abun da nake miki da baya miki dadi zaki iya fada min sai na gyara, idan kuma aiki ne kike ganin na sakar miki ragamarsa zan rika yin rabi, amman dan Allah ki zauna ina jindadin zamanki ina son yar'uwa a kusa da ni, ba ni da kowa nan zamanki a gidan nan yana rage min kewa”

“Babu wani tsabani da zamu samu har ya saka na ji bana bukarki a kusa da ni, mu na samu tsabani a gida a nan ma zamu iya samu, saboda zama tare dole wata rana zaka ji an maka ba daidai ba, amman Noor ni ba zan iya cin amanarki ba”

Ta rumgume ni tana kuka, jikina yayi sanyi sosai kalaminta na karshe ya saka min shakku a zuciya.

“Akwai abun da yake faruwa tsakaninki da Abdull ne?”

Ta dago da sauri.

“Aa Wallahi Babu, dan Allah karki zarge shi ki lalata aurenki, Wallahi Wallahi na rantse miki da Allah babu wani abu tsakanina da Abdull”

Hankali ya dan kwanta da ta yi min rantsuwa cewar ba tsakaninta da Abdull ba ne.

“To ya kawo zancen cin amana Hana?”

Ta share hawayenta.

“Ina nufin kamar na guje ki saboda kin min wani laifi, ai kamar na ci amanarki ne a matsayinki na yar'uwata”

“To me yasa kike son tafiya gida? Kina karatunki a nan, Abdull ma idan ya ji ai zai yi fada, Mama ma sai ta miki fada tace kin san ba zaki karatu ba kika saka bata kudi aka biya miki har na shekara uku”

“Kawai ina yawan mafarkin marar kyau ne, kuma ana baki tsoro a gidan nan ina tunanin akwai aljannu a gidan”

“To ki rika addu'a mana Hana, ke da kike fada min yadda zan bi da rayuwa na jidadi yau kuma ke kika rasa ya zaki yi?”

Ta yi murmushi

“Gaba daya na rikice mugun mafarkin da na yi ya daga min hankali”

Zan sake yin magana Abdull ya kirani.

“Noor kin fasa zuwa awon ne? Karki makara fa”

Na dauki ruwan zafi na fice daga kitchen, sai da ta jera mana komai a dinning sannan ta zuba nata ta dauka.

“Lafiya na ga kamar yanayinta ya canja”

Abdull ya tambaya she dai shi ma ya lura da yadda take ta hade rai bata son kallon kowa.

“Lafiya kalau”

Ta wuce dakinta bayan ta amsa mishi, da kallo na bita sai da ta shige sannan na juyo na kalleshi, kamar na fada masa kudurinta sai kuma wata zuciyar ta hana ni, na san ba abu ne da zai masa dadi ba, saboda kudin makaranta da ya biya mata ga yawan hidima da yake mata, tafiya makaranta ma kullum sai ya bata kudin bus kuma ya rage mata hanya saboda akwai tazara daga unguwarmu zuwa makaranta kuma babu abun hawa sosai ta gurarenmu sai idan sun kawo Passenger.

“Ina jin bata da lafiya ne”

“Me yake damunta? Ko kuma dai mood swings ne”

“Yeah”

Ko da muka gama karyawa ta yi shirin makaranta da uniform dinta da suke sakawa kullum. Tare muka fita sai da ya fara sauketa sannan ya sauke ni a asibitin ya wuce gurin aikinsa.

Tun daga ranar Hana bata sake yi min maganar komawa gida ba, sai dai na lura da yanayinta gaba daya ya canja kamar zaman gidan ya daina mata dadi a yanzu, domin ko hirar da take zama muna yi tare da Abdull a da yanzu duk ta daina, ko da yake yanzu ba kamar da ba ne, da take gida kullum yanzu kuma idan ta tafi bata dawowa sai yamma idan ta dawo wani sa'in ta hau aikin gida ko da ta gama kuma sai bachi. Sai can ba a rasa ba muke zama muna hira a falo da zarar Abdull ya shigo zata masa sannu da zuwa ta shige dakinta ba zata sake fitowa sai gobe.

Ko wani abun ya siyo sai dai na kai mata nata dakinta, ko kuma shi ya kwankwasa kofar dakin ya aje mata daga bakin kofa, wani sa'in idan ina jin wahalar tashi. Wata kila ta fara haduwa da abokan banza masu hore mata kunne ne, ko kuma dai ta gaji da yin aikin gida ne, ko kuma nata gidan mijin take son tafiya ita ma.
Ko ma dai yaya ne na daure ma zuciyata na zauna da ita a haka, saboda bana son ta lakata karatunta a lokacin da take tsananin bukatarsa, kuma ana yi da kai ya fi ba'ayi, zamanta yana taimaka min ko yaya ne tun da ita take min komai a gidan kuma ina ganinta na san ina da yar'uwa a kusa ina jin sanyi a haka din ma.





KAREEM POV.

Da sauri ya maida idon ya rufe ya kai hannunsa dake sanye da drip ya murza idon sannan ya sake budewa. Hannun ya kai ya cire robar dake bakinsa yana kokarin daga hannunsa daya sai ya ji yayi masa nauyi dubawar da zai yi sai yayi arba kan dansa Areef a hannun. Yunkurawa yayi a haka ya tashi zaune ya saka dayan hannun a hankali ya cire hannunsa. Haka ya cire duk wani abu da aka laka masa sannan ya sauko da kafafuwansa yana tuna abun da ya faru.

Ya san dai yana tsaka da tuki hudu ya sauko masa daga lokacin kuma be sake sanin inda yake ba, maybe ya hadari yayi, ba ma wata kila idan be yi hadarin ba ai ba za a kawo shi nan a aje ba. But why ICU shi da be ji ciwo ko daya a jikinsa ba, domin be ga wani guri da ya ji ciwo bako ya bugu. Hannu ya mika ya janyo files dinsa ya bude ya duba. Daman ya sani zama unconscious or in a critical condition ke saka a aje mutum a gurin. Ya duba ya gani kwanansa biyu a dakin amman be sani ba sai yau da ya farka, babu wata rauni a jikinsa but hankalinsa da numfashi sun yi nisan da an dauka barin duniyar zai yi.

Ko me ua buga oho, ya san dai hakan baya rasa nasara da damuwar da yake ciki, kusan ita ce silar faruwa komai. Ya aje files din ya shafa kan dansa dake sanye da uniform din makaranta yana murmushi ko dan yaran nan yana bukatar rayuwa. Areef ya bude ido sakamakon shafa kansa da Dadynsa yayi.

“Hey young Man”

Yaron ya tashi zaune ya matsa ya rumgume mahaifinsa yana murna.

“Dady ka farka”

Kareem ya saka hannu ya shafa bayansa yana murmushi kamin wani azababben ciwo ya ratsa zuciyarsa har sai da ya ji ta motsa kamar ta bar muhallinta.

“Oh...”

Ya furta Areef ya dago ya kalleshi.

“Dady minene?”

Kareem ya murmushi.

“Ba komai ina Tine”

“Suna waje bari na kira ta har da Mama ma tana nan, kullum zai mun zo kana bachi, Hajiya tana nan ita da Uncle Aaryan nan yake kwana”

Har ya isa kofa sai kuma ya juyo ya kalleshi.

“Daddy ma kullum yana zuwa, yana yin addu'a yana tofa maka, Dady kuma Momy ta kwashe kayanta gaba daya ta koma gurin Hajiya an bata bangare daya tace tare zata zauna da mu”

Kareem ya daga mishi kai. Areef ya fita da gudunsa, Kareem kuma ya mike tsaye ya fito daga dakin da kafafuwa normal yake jin kansa kamar be yi hadari ba. Ya san yadda asibitin take fa kuma dokokinta sai ya canja ma kansa daki bayan ya gaisa da ma'aikatan dake ta masa sannu Doctor dake duty yana da tsokarsa yana fadin ya bari yayi aikinsa yanzu shi majinyaci ne ba likita ba

Files din dake dayan dakin likita ya dauko ya dawo da su sabon dakin da Kareem yake, sannan aka bawa visitors damar shiga, yan'uwa na ta shigowa suna masa sannu na nesa kuma suna kira a waya. Duk wani motsi nasa yana kan idon Yusura kallonsa take sosai kamar bata taba ganinsa ba, sau daya ta yi masa ya jiki bata sake ba sai dai duk dagowar da zai yi sai ya ga tana kallonsa. Tun daga ranar kuma bata sake zuwa ba duba shi har aka sallame shi after four day's da yayi a asibitin.

Ranar da zai bar asibitin babu yadda Hajiya bata yi ba akan ya dawo family house ya zauna har sai jikin ya kara warwarewa da kyau saboda a can gidan babu kowa a yanzu amman ya ki, domin baya son zama gidan zai fi sakewa a gida ko da kuwa ba shi da lafiyar balle baya jin ciwon komai a jikinsa. Taya zai saki matarsa ta tare a family house dinsu shi ma ya koma can ya tare kamar mace.

Ba karamin godiya yayi ma Allah ba lokacin da Aaryam ya kai shi gidan ya ga yadda gaban motarsa ya lalace, bayan ma ya bugu ba karamin accident yayi ba amman Allah ya kawo masa sauki tun da be ji rauni a ko'ina ba. Aaryam ya fada masa yadda hadarin ya afko sai da ya cika da tsananin mamaki.

“Babu wanda ya dauka zaka rayu fa, Wallahi duk mun tsorata, babba mota ka buga irin mai zube yashin tefa. Mai motar yace yana ta maka horn domin ya ga yadda ka zo da gudu amman baka tsaya ba sai da ka bugu shi, gashi ita kuma wata motar ta bugi taka a baya, daker aka fito da kai motar babu rauni amman baka numfashi hankali ya bace gaba daya, asibitin ma sai da aka yi da gaske sannan numfashinka ya dawo”

Yayi murmushi.

“Kwana ne ba su kare ba, da lokacin yayi da ba zan farka ba, Alhamdullahi”

“Gaskiya mun auna arziki, da mun rasa ka rayuwa ba zata yi dadi ba”

Kareem ya kalli falon ya mike tsaye.

“Wata rana dole za ku rasa ni Aaryan dole kuma ayi hakuri da rayuwar”

“Haka ne, amman ba ma fatan zuwanta yanzu, Allah dai ya kara maka lafiya”

“Ameen”

Aayam ya sauke ajiyar zuciya.

“Yusura da Khadija sun sha kuka, Hajiya har sai da aka zuba mata ruwa, ban taba ganinta cikin tashin hankali irin na ranar ba, babu wanda be yi kuka ba sai ni”

Kareem ya juyo ya kalleshi.

“Eh kai mai zuciyar fir'auna ko?”

Aaryam yayi dariya.

“Ai duk abun da zai saka namiji kuka ba karamin abu ba ne, Allah dai ya tsare faruwar hakan”

Dinning Kareem ya dafa.

“Yusura bata fada muku abun da ya faru ba?”

“Ta fada mana, har ta kwashe kayanta ai Hajiya ta bata bangare daya ta zauna saboda ta samu sakewa ita da yaranta, Khadija da Nana sun koma bangarenta, na yi mamakin kukanta wata kila ita ma ta dauka mutuwa zaka yi”

“Daddy be ce komai ba a game da rabuwarmu?”

“Ba ka da matsala da shi, tun a lokacin da aka fada min halin da kake ciki sai na same shi na yi masa bayanin komai, saboda mu samu goyon bayansa idan zaka kara aure, ashe Allah da kai ba, amman dai ya sani kuma ya daga maka kafa. Kawai addu'a yayi Allah yasa hakan shi ne mafi alheri”

Dogon numfashi Kareem yaja ya sauke ya daga kansa sama.

“Ameen”

A gidan Aaryam ya wuni saboda ya ragewa dan'uwansa Zango har sai da yamma ta yi sannan ya tafi bayan sun sha hira sosai. Kareem ya juyo kenan daga rakiyar da yayi ma Aaryan bakin kofar falon sako ya shigo wayarsa.

“Wata kila ni ce silar hadarinka? Shin ka aikata hakan ne da nufin kashe kanka? Ka ji zafin gaskiyar da ka sani ne Kareem? Ni ma daga baya na gane ban kyauta ba na yi kuskure, amman na maka alkwari babu wanda zai ji wannan, ina zuwa dubaka asibiti a kullum amman bana samun damar shiga na ganka saboda yan'uwanka da matarka suna gurin. Yau kuma na tafi aka ce an sallame ka na jidadin haka kuma na ji tausayinka na yi bakinciki abun da ua faru da kai, ina kaunarka Kareem Wallahi ina kaunarka”

Ya goge sakon bayan ya gama karantawa, ko ya fada mata yayi hadarin ma oho, falon ya shiga ya kwanta akan kujera ya rufe ido yana maida numfashi a hankali.





NOOR POV.


A lokacin da cikina ya shiga wata bakwai na samu sauki abubuwa da yawa na daina amai da kwadayin sosai, ko zabar abinci. Har ta kai ni nake shirya abun karyawa da safe da kaina. Domin yanzu Hana ce mai tsananin bachin safe idan ta gama sallah ta koma ta kwana sai kace ba yar makaranta ba. Kullum sai ta buga latti saboda bachi, har tausayi take ba ni domin na san wahala ce ta yi mata yawa, na aikin gida da take ga kuma karatu da basa daga kafa.

Abun sai ya zame mana kamar duty ni ce mai saurin bachin dare ita kuma ta yi rankon na safe. Domin da zarar na gama sallah Isha'i Abdull ya kawo lemun juice da yake hada min a kullum, domin likita yace na rika cin yayan itatuwa sosai a yanzu fiye da kayan zafi ko kwadayi irin su madara da danginsu. Saboda kina yana ta girma ne a yanzu, ban yi kasa a guiwa ba na rumgumi kayan marmari, kullum sai na ci da dare kuma sai Abdull ya hada min lemun juice da juicer da ya siya gurin Khadeeja Candy Store, zallar ruwan fruit take matsewa sai dan sukari kadan da yake kasa min ko kuma abar da bana so wato zuma, wani lokacin saboda bakin nawa ya saba da zaki idan babu ba zan sha

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login