Showing 39001 words to 42000 words out of 133189 words

Chapter 14 - Taki Zaman Aure Book 2 Hausa Novel Complete

13 Dec 2024

257

Hafiz ko an sanar da Noor.

“Aa ba a fada mata ba, jiya na tambayi Aisha ya ba su zo tare ba sai tace wai tana gidansu ta tafi kusan sati uku bata gidan”

“Ya kamata a sanar da ita, hakki ne a fitar mata da shi...”

“Aisha tace sakinta yayi, amman be fada mana ba, ko ka sani”

“Haka ne, amman tana da hakkin a sanar mata... Mama ki aika a daukota”

“Toh ko zaka tafi tare da Raliya sai ku taho da ita, tun da kai ka san gidan”

Yayi shiru kamar yace a a sai kuma ya amsa mata da kai ya ce Raliya ta tashi su tafi. Karfe 6am daidai suka faka a kofar gidan.

“Shiga ki musu magana”

“Tohm...”

Ta amsa tana kuka sannan ta bude motar ta fita.



NOOR POV.

Muna tsaka da tafiya sai na ga sun yi nisa sun bar ni, yana rike da hannun uwargidansa Aisha ita kuma tana rike da hannun yaranta. Gajiya ta saka na zauna a gurin da suka bar ni mai tsananin turbaya da jar kasa, sai dariya nake sun yi nisa sosai kamin Hafiz ya juyo ya kalleni a lokacin ne ya hankara bana tare da su sai ya rugo a ruje ya nufo inda nake yana rike da hannun Aisha ya karaso kusa da ni yana numfashi daker.

“Noor taso mu tafi...”

Ya miko min hannunsa sai na daga kai na kalleshi sannan na mika masa nawa hannun zai kama kenan kasar da yake tsaye akanta ta bude ta rusga da shi ya fada, sai ya bar mu a gurin ni da Aisha muna kallon ramen da ya fada, ita tana rike da yaransa ni kuma ina daga zaune a gurin domin be kai ga riko ni ba ya fada. Dariyar Aisha ce ta dawo da hankalina zuwa gareta kamin ni ma na fara dariyar sai na mike tsaye. Ban lura ba ashe saman wani tsaye nake tsaye mai tsananin tsawo da saka jiri. Tangal tangal na fara kamar zan fadi sai na ji wani ya rike ni ta dama, yana sakina ya fara tangal tangal wani ya rike ni daga hagu, yana sakina na sake komawa yar gidan jiya, sai kuma na ji an rike ni ta baya, kamin na ji wani dabam kuma ya rumgume ni a kirjinsa, a chest with full of hairy chest har yana shiga min baki.

.....Firrrrrrr gigit na farko daga bachin wahala da kuma mafarkin da na tabbatar ba na kwarai ne, domin mafarkin dariya yana nufin bakinciki ga mai yinsa sai dai ta inda ban fahimta me yasa ni da Aisha muke dariyar? Kuma su waye suke rike ni? Waye wanda na kwanta a kirjinsa. Tashi na yi na alwala na rama sallah sannan na gabatar da sallah asuba ina jin fuskata na min yaji saboda dukan da Yaya yayi min ya ji min ciwo a kumatu da gafen ido har ma da saman bakina. Na jingina kadan ina lazimi da hannuna na ji an buga gidanmu, Yaya ne ya bude bana jin me ake cewa amman tabbas na ji yana fadin.

“Eh tana nan”

Sannan ya kwala min kira na tashi da sauri da kuzari na fita gudun kar na yi laifi. A tsakar gidan na yi arba da kanwar Hafiz, domin Aisha ta gabatar min da su a lokacin da suka zo ina amarya haka ma a burin Walima mun hadu da juna. Hawayen da na gani a idonta ne suke min magana ba bakinta.

“Yaya Kareem yana waje ya ce ki zo mu tafi”

Na nufi kofar babu talkami a kafata na fice daga gidan zuwa kofar waje. Kareem ya na samu jingine jikin wata bakuwar mota ya rumgume hannayena yana kofar gidanmu.

“Hafiz ya rasu...!”

Na fada domin a yanzu na gama fahimtar mafarkina.

“Ban fada mata ba”

Na ji kanwarsa ta fada daga bayana. Juyowa na yi na kalleta.

“Na sani, na gani a mafarkina na gani jiya ya saki hannuna ya zo zai kama ni sai wani rame ya bude ya fada da shi, ya saki hannuna da na Aisha, ya tafi ya bar ni ina tangal tangal, wayyo Allah na, na shiga uku wayyo Hafiz...”

Na ruka zan kai kasa sai kanwarsa ta rike ni ni da ita muka fashe da kuka mai karfi.

“Karfe 8am za ayi masa sallah, you need to be there kamin a tafi da gawarsa”

Kareem ya fada ganin kukan na mu ba mai karewa ba ne. Yaya ya leko yana ganin Kareem ya gaishe shi, sai Kareem ya ce.

“Ka fadawa Baba Allah yayi ma Hafiz rasuwa jiya da dare, sakamakon hatsarin da yayi a hanyarsa ta dawowa daga Kano”

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”

Yaya ya fada ya juya ya koma cikin gidan, Kareem kuma ya bude mana mota ni da ita muka shiga baya. Yanzu ta ina zan roki gafararsa ya tafi be fahimce ni ba, ina jiran tsammanin zuwa ko aikowa a dauke ni sai labarin mutuwarsa ya riske ni a yanzu.

“Ni ma tawa rayuwar ta kare...!”

Wannan kawai na iya furtawa ina kuka bayan haka ban sake fadar komai ba har muka isa gidan. Gidan ya cika tam da mutane amman ba cikar farinciki ba domin kowa kuka yake da jimami. Haka na fito motar babu talkami a kafata kanwarsa ta ja ni ta shiga da ni har gurin da gawar take. Sai ta ja ta tsaya daga bakin kofa ta ni kuma na kwance, yana kwance cikin kagara an masa sutura amman likkafaninsa yana jike da jini. Ban taba arba da gawa ba sai a ranar domin ban taba rasa kowa ba, ban rasa uwa ba ban rasa uba na ban rasa yaya ko kanwa ba. Ban san ya zafin abun yake ba, ban taba zauna a daki daga ni sai gawa ba sai yau. Ashe mijina ne farkon abun da zan fara rasawa a kananan shekaruna... Ban taba sanin idan mutum ya mutu abubuwan da kake masa marar dadi ne suke zuwa su tsaya maka a rai ba sai yau.

Yadda yayi ta kokarin kaiwa ga jikina ina hana shi da ihu da kokawa ne ya tsaya min a rai, ya saka ni fasa ihu ya saka ni rawar jiki, me yasa ban bari ya kai ga abun da yake halalinsa ba? Me yasa na biyewa Aisha da tsoro har abubuwa suka zo mana a haka? Ashe zaman ba mai tsawo ba ne ko da na zauna a gidansa ne. Wasu matane ne suka shigo suka fitar da ni, ina wani irin kuka da ban san ina yi ba, sai hakuri suke ba ni suna rarrashina amman ji nake kamar suna cewa bude baki ki yi kuka sosai Noor yau ranar kukanki ce.

Ni dai na san bana son Hafiz amman kuma ba kinsa nake ba, amman a ranar na ji tausayinsa kuma na ji tausayin kaina, ban gane haka ba sai da aka fito da gawarsa za a fita da ita domin yi masa sallah. Ban san ya aka yi ba na isa gurin na ratsa cikin maza na rike makara, ina kiran sunansa kamar ance zai iya amsa min. Daker aka banbare hannuna daga jikin makarar su kuka ni kuka ana rike ni aka fita da gawar mijina wanda shi ne duniyata a yanzu.

Ban kara raina kaina ba sai da aka kai shi gidansa na gaskiya aka dawo, maza suka shigo cikin gidan domin yi mana gaisuwa, ashe wata kalar azaba ake ji idan aka yi maka gaisuwar wanda ya rasu. Allah ya jikansa yayi masa rahama ya raya abun da ya bari haka kowa yake ta fada. Cikin taron masu yi mana gaisuwa Mama ta kutso ta shigo ta iso inda nake ta zauna sai ta saka hannunta biyu ta rika fuska.

“Yi hakuri Noor yi hakuri”

Ta fara karanta ayatul kursiyu ta tofa min a kai ta busa ido. Ban sani ba ashe ba daidai nake kallon mutane ba, idanuwan nawa juyewa suka yi ina kallon mutane a baibai. Ta rumgume ni tana kuka, sannan yan'uwanta da na Baba suka shigo suka zauna suna gaisuwar kamar yadda yan'uwan Aisha ma suke cike a gidan, ita ma kuka take tana gurnani ko'ina ana jinta sai hakuri ake bata wasu na addu'ar Allah ya sauke ta lafiya. Ni kuwa a zuciyata ba ni da makiyiya irin Aisha domin ita ce silar duk wata fitina a gidan Hafiz, ashe ma ba dadewa zai yi tare da ni ba, me yasa ta zuge min kunne bata bar ni na yi zaman aure kamar ita ba? Amman laifin ba nata ba ne nawa ne miyasa na dauki zugarta? Why?

Har aka yi addu'a uku ban daina ganin laifin kaina ba, kuma ban daina fargabar yadda rayuwa zame min ba bayan tafiyar Hafiz, na san kowa zai dora min laifi ne a gidanmu, kuma na cancanci haka ya kamata ayi min kowane kalar hukunci a yanzu. Na gane ba laifin kowa ba ne nawa, ni ce wawuyar da ban fahimci duniya ba.
Wani irin nauyi na ji an dora min ashe haka ko wace mace take ji idan ta rasa abokin rayuwa, ni kenan da ban dade da shi ba kuma ban haihu da shi ba ina ga wandanda suke da yaya kuma suka dade a tare? Wani abun da zan iya cewa tsana ce ko tashin jindadi na ga ganina fuskar iyayen Hafiz bayan sadakan ukun ita ce ta mutuwar auren.

Ina da tabbacin a cikinsu babu mai iya bada shaidar abun da ya faru indai ba Aisha ta fada ba, domin sun ce ba su san da sakin ba har sai da ta fada, amman sai na ga nuna min wani kallo, mahaifiyarsa na tambayar me ya hada mu har tana fadan danta mutumen kwarai ne mai mutunci mai rike amana, domin tun da ya auri Aisha ba su taba jin wani abu ba, yana zaune lafiya da matarsa.

“Waya sani ma ko bakincikinki ne ya saka shi sakin motar har yaje yayi hatsarin, kin saka na rasa mijina uban Yayana mai so na tsakani da Allah”

Na kalli Aisha dake maganar ina hawaye.

“Allah ya isa tsakanina dake, ke ce silar da Hafiz ya sake ni, Allah ya isa ban yafe miki ba”

“Mijina be san tashin hankali ba sai da ya aureki, daga sunan taimako, Wallahi Hafiz baya sonki shi be taba sonki ba daga ya taimaka ya auroki sai kika zo cikin gidan suna son cin amanarsa”

Mahaifinsa ya daka mata tsawa.

“Aisha ya isa haka, ko dai minene ya riga ya faru, Allah ya masa rahama, babu amfanin maido baya”

“Ai amana bata barin kowa, Allah ya masa rahama, ni dai ina son na tafi da Noor can gidana idan kun yi min izini, yarinya ce ba zata iya wanka ita kadai a gidan ba”

“Ai wanka be hau kanta ba domin ya sake ta tun kamin ya rasu, da wanka da gado duk basa kanta”

Mahaifinsa ya fada. Sai Aisha ta karba.

“Balle ma bata taba yarda da shi ba, kullum addabarsa take da fitina bata taba yarda ya taba ta har ya rasu”

Na kalleta ban ce komai ba na dauke kai. Yayan mahaifin Hafiz ne ya ce.

“Ko ma dai minene ba mu yanke hukunci ba, sai mun bincike malamai mun ji me ake ciki tukuna, ki tafi da ita din idan mun bincika duk abun da yake nan za mu sanar miki”

Yana maganar yana kallon Mama sai ta amsa da tohm. A bisa wannan muka fito daga gidan, wani abun da ban yi tsammani ba shi ne direba ne da mota ya daukemu daga gidansu Iyayen Hafiz zuwa family house din su Mama. Muna shiga kowa sai tausaya min yake suna ta shawarar inda zan zauna a gidan, domin sun ce zaman wanka wai sai da mai kulawa da mace, domin gidan Baba babu mata Hana kuma karamar yarinya ce bata san komai ba.

“Ki barta gurin Kawu Garba, matarsa bata da matsala zata kula mata”

“Na fa yi magana da Alhaji, shi da kansa ya ce ta zo ta zauna ba wani matsala”

Yayanta ya girgiza kai.

“Amman Hajara baki yi tunani ba, saure sati daya ki yi masa maganar kawo yarki a gida? Haba dan Allah”

“Wallahi Yaya ba ni na yi masa magana ba, tun da aka yi rasuwar na fada masa yace na shirya na zo matarsa ma sau biyu tana zuwa, to kuma jiya da aka yi sadakan uku yake min maganar cewa na maidota a gidan ta zauna tare da ni zata fi sanyi, saman da zaman gidan ubanta domin babu mai kula mata a can din, babu yadda ban yi amman yace na kawota ai kowa ya san lalura ce bata wuce kowa ba, kuma gidan gida ne babba mai yalwa zata iya yin sha'aninta har ya shigo ya fita bata sani ba, domin bangarena dabam bangaren matarsa dabam kuma bangaren nawa ma babba ne sosai”

“Aa ni dai ban aminta da hakan ba, kawai dai ya fada ne saboda kawaici, da dai kin hakura ki barta a nan din ta zauna idan ta gama wanka idan ya sake magana sai ta koma amman a yanzu ki barta a nan”

Cewar wata yayarta. Sai Mama ta ce

“Toh ai na ji suna fadar wai ba zata yi wanka ba, saboda ya sake ta”

Yayanta ya kalleni.

“Sakinta yayi? Yaushe?”

Mama ta fada musu komai sai dai ita ma ba zata iya fadar dalilin sakin ba. Ni kuma na gagara fadar abun da ya gani a jakata har ya zama silar lalacewarki komai.

“Ni fa yadda ba lura wannan matar tasa kamar ba ta Allah ba ce, duba yadda yake son kunyata Noor cikin danginsa”

“Na lura Wallahi Yaya, ai gata ga su idan wani za su kara aura mata sai mu gani, na san Noor bata jin magana amman a yanzu na lura wannan matar ta fi ta wayo, wata kila da zaman ya dade Allah kadai ya san me zai kasance”

Mama ta fada.

“Aa laifin duk na wannan yarinyar ne, ba mamaki taje tana masa hauka da nuna masa ita wacan take ba kin san halinta da shirme da shashanci to ya bar miki duniyar kin huta”

Cewar Yayanta, haka dai suka ci suka cinye ni dai bana iya cewa komai idona sai ciwo suke saboda kuka da na sha. Daman na san laifin a kaina zai dawo duk juyin da za'ayi ba zan taba wankuwa a idonsu ba. Daga karshe dai aka yanke shawarar bari a gidan Baba domin ya tsaya kai da fata ba zan zauna ko'ina ba sai a gidan, bayan har Kawu Garba ya ce zan zauna a gidansa.

A dole na dawo gidan da zama sai wani sabon kunci ya bude min kofa. Hana ta min magana ta kan ja ni da hira Yaya ya kan min magana amman Baba har lokacin fushi yake da ni, yar karamar rayuwar da na yi a gidan Hafiz ta dawo min sabuwa, ina tuna lokacin da ya siya min waya ko kuma yake rarrashina idan kuma na tuna abun da na yi masa na bacin rai sai na ji kamar zan runtse ido na mutu na huta, ina ma ace zai dawo na kyautata masa? Ina ma ace zai dawo ya fahimci ba ni na saka robar nan da magani a jakana ba. But the part da na tuna Aisha tace shi ma haya so na ya kan saka na ji wani iri, be so kuma ya aure ne? Saboda me? Ya san be so ya raba ni da mai so na kuma ya aure ni....




KAREEM POV.

Yana zaune a kan tool holding his best friend picture yana kallo, har lokacin baya iya kukan rashin abokinsa zuciyarsa tana nan da nauyinsa pain din ya fi karfin kuka, har gobe he can't believe abokinsa ya tafi ya barshi.

“Sun ce mutanen kirki ne suke tafiya da wuri, ka fini kirki har a gurin Allah domin baka aikata abun da nake aikatawa ba, kana kokarin tsare dokokin Allah, kullum burinka na daina abun da nake marar kyau, a lokacin da ka fahimci bana cikin farinciki sai ka fara gina tubalin matso min da shi kusa, maganar mu ta karshe ma umanine kake kokarin cikawa saboda ka faranta min, ba zan taba barin iyalinka su shiga kuncin rashinka ba Hafiz”

Yana maganar idonsa suka fara tara hawaye, at the same time Yusura ta turo kofar dakin ta shigo. Kusa da shi ta karaso ta tsaya sai da ta kalli hoton dake hannunsa sannan ta kalli Kareem ta ce

“Kyautatawa abokin zama, makoci ko aboki wajibi ne gudun kar ya tafi a dawo nadamar da bata da amfani”

Ya aje hoton ya rufe drawer madubin.

“A iya sanina Noor bata son Hafiz ko kadan, saboda ya raba ta da wanda take so kuma ya aurenta alhalin shi ma kansa ya san baya sonta kamar dai ke, banbancin mu da su, ba iyaye ne suka cilasta ba, duk wani yunkuri da yake saboda ni ne, daga karshe kuma sai abun ya fada kansa, ashe saboda ya tafi ya bar ni da bakinciki kasa cika masa burinsa ne da ban yi ba...”

Ya dago ya kalleta yana murmushi.

“Kin san banbancinki da Noor? Ta fi ki wayo ta fi ki imani da yardar da kaddara, ta fi ki tsoron duniya, yarinyar nan bata iya munafurci da pretending ba, tsabar saka shi da ta yi a zuciya na nesan da ta yi na kwana biyu sai da ta yi mafarkin mutuwarsa tun kamin a fada mata ya rasu, a ranar da za a binne Hafiz na ga wani abun da ban yi zato ba gurin yarinyar nan, ta rike karagarsa tana kuka, na tabbatar da ni aka sanar miki na mutu murna zaki yi...”

Ta yi murmushi.

“Kasan da hakan kuma kake zaune da ni har yanzu? Idan zaka kwatanta Noor da misalta ta da Safeena mana, ka ce ta fi Safeena wayo, amman ba ni ba, ni din na san abun da nake so da wanda bana so. Ko da yake dole ka yaba Noor ai, saboda kana sonta shiyasa ka cilastawa abokinka aurenta, yanzu kuma ya tafi ya barku sai ku cigaba daga inda kuka tsay....”

Tana kai aya yana wanke mata fuska da wani zazzafan mari, har sai da ta ja baya

“Ka mare ni Kareem? How dare you...!!”

“Saki kike

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login