Showing 36001 words to 39000 words out of 133189 words

Chapter 13 - Taki Zaman Aure Book 2 Hausa Novel Complete

13 Dec 2024

267

na yi daga gidan ina tafiya jikin ba dadi as well as zuciyata bana iya daga kai na kalli ko'ina har na isa titi, Napep din da ta faka kusa da ni na nufa. Ban tana sanin ina tsananin kaunar Zafeer sai a yau da na yi arba da shi ya fito daga Napep din da nufa zan shiga, ya rame kamar dai he is the only person da na kalla daga fitowa ta gida zuwa nan, shi ma kallona yake kamin ya dauke idonsa ya saka hannunsa aljihu ya dubu daya ya mikawa mai napep din.

“Canjin ka kai wannan inda zata je”

Wannan karon muna hada ido hawaye suka zubo min. Ya dauke kai ya matsa baya ni kuma na shiga na zauna ina kallonsa har mai napep din ya fara tafiya...

“Ina zamu je Hajiya?”

A take hankalina ya dawo jikina, kunya da damuwa da bakinciki nadama da kuma dana sani suka rufe ni. Yaushe Zafeer ya dawo garin? Ko dai be tafi ba? Har yanzu yana so na? Ko ya daina? Ya yake kallona? Wata kila ya ji labarin mutuwar aurena amanarshi ta kamani. Ina Son ka Zafeer ina sonka sosai ina son Zafeer Allah ka sani, shi ne abun da nake ta fada a zuciyata, ban hakaro da inda nake ba har sai da Mai napep din ya sake tambayar ina zai kaini. Toh ina zan je kuwa bayan restaurant din Kareem by this time na san Hafiz yana gurinsa, zan fi jindadin tunkararsa a can na bashi hakuri kuma na fada masa ba zan sake aikata kuskure ba, duk kuwa da na san ni din ba ma'asumiya ba ce. Rokonsa a can zai fi min rufin asiri fiye da rokonsa a gidansa kuma a gaban muguwar matarsa wadda ita ce silar faruwar komai.

A gaban restaurant din ya sauke ni, ina jin zuciyata kamar ba tawa ba tsananin kunnar da take min, na fito na doshi gate din sai masu gadin suka tare ni. Suna tambayar ina zan tafi, ban yi mamakin jin sabuwar dokarsu ba ta sanin wanda zai fita ko ya shiga, domin aikinsu ne bada tsaro a matsayinsu na masu kula da gate din. Sai dai abun da ya ba ni mamaki shi ne fadar sunana da suka yi, sannan suka tabbatar min da Kareem baya gurin.

“Ba gurin Kareem na zo ba, gurin Hafiz na zo”

“Shi ma Hafiz din baya nan”

“Zan iya shiga na jira?”

“Aa gaskiya Oga yace kar abarki ki shiga”

Na yi murmushi na juya na kama hanya, yanzu kuma ban san ina zan je ba, ashe abun har ya kai haka? Na zo ace is kar na shiga ciki. Dama na kama na fara tafiya a kafa domin ba ni da kudin abun hawa, idan ma na hau yanzu ban san inda zan je ba. Motar da ke fuskanto ni har ta wuce ni Sai kuma ta dawo ta faka gabana, ban san hawaye nake ba har sai da Kareem ya fito motar ya kalleni ya ce.

“Dole ne sai kin fadawa kowa kina cikin damuwa?”

Na kai hannu na share hawaye ina kallonsa.

“Na zo sun ce kace kar a bar ni na shiga ciki”

Ya dan dauke kansa.

“Wannan zuwan ba saboda kai ba ne, na zo gurin Hafiz ne, saboda bana son na tafi gurin matarsa kai tsaye, na san a irin wannan lokacin yana gurinka ne, na san na takura maka da yawa Kareem, ba zan sake ba na sani ai na ishe kuwa a yanzu”

Ajiyar zuciya na ji ya sauke.

“Me Hafiz zai miki?”

“Hakuri zan ba shi, zan roki ya maida ni gidansa...”

Gambun motar da yake rike da shi ya sake yana kallona kamar mai mamaki.

“Noor ba ayi ma namiji haka, shi ya sake ki ai let him come to his senses idan maida ke zai yi sai ya maida ke, amman be kamata ki roke shi ba”

“To ya kuke son na yi? Kun raba ni da wanda nake kauna yake so na tsakani da Allah, yanzu kuma abokinka ya sake ni na dawo gida, Baba baya min magana be amsa gaisuwa ta, Hana bata hira da ni, Yaya ko kallona baya yi, a unguwa ana ta yi da ni, Mama tana fushi da ni? So kuke na kashe kaina?”

Na karasa maganar ina fasa wani irin ihu kamar wadda ya fita daga hankalinta. Da sauri Kareem ya matso kamar zai rika ni.

“Noor... Lafiya”

“I'm alright...”

Na amsa ina kaucewa daga gabansa na cigaba da tafiya.

“Zuwan da kike gurina yana daga cikin abun da yake haddasa fitina tsakaninki da Hafiz, shiyasa na ce kar abarki ki shigo, domin na san zaki sake zuwa ne, a yadda na lura Hafiz yana kishi da hakan, saboda akwai abun da baki sani ba a tsakanina da shi”

“Ba zan sake takura muku ba Kareem, ba zan sake zuwa ba”

Na fada ba tare da na juyo ba. Sai ya kira ni

“Noor...”

Na juyo ina wani irin kuka har naman fuskata na rawa.

“Hafiz baya garin nan, ya tafi Kaduna gurin wani case tun jiya, amman yau zai dawo. Shim kina son komawa gidansa?”

Na daga mishi kai.

“Shi kenan, Hafiz zai maida ke na miki alkawari”

“Na gode”

Na furta daker sannan na juya na cigaba da tafiyar, daga restaurant din zuwa unguwarmu tafiya ce mai nisa amman haka na tako da kafa har gidanmu saboda ba ni da kudin abun hawa kuma na san babu mai ba ni a wannan karon, tufafi ma tun wanda na zo da su daga asibitin ban ni da na canjawa sai dai idan suka yi datti na wanke da ruwa na shaya idan suka bushe na saka, haka nake kamar wata matar gata...
Ina shiga gidan, Yaya Nabil ya rufe ni da kuka saboda Baba yayi masa izinin haka, wai na ki zaman aure ina son na fara yawa ina na fito? Gurin uban waye na tafi? Na kasa magana sai kuka nake, duka sosai Yaya yayi min har sai da ya sauya min kamanin fuskata. Baba kuma ya kara min da zagi yana fadin ai ya ji labarin Zafeer ya zo garin nan gurin iyayensa ba mamaki gurinsa na tafi mika hadu. Da rarrafe na shiga dakin na kwamta a kasa a lokacin da ake kiran sallah Magariba a kowane Masallaci, a gurin na kwanta ban iya tashi ba har safe...



KAREEM POV.

Tsaye yayi a gurin yana ta kallonta tsawon lokacin da ta dauka tana tafiya a kafa har ta karya kwana. Babu abun da yake bata masa rai a rayuwar Noor da Hafiz kamar kasancewa a tsakani, ya zama tsakanin ma'auratan guda biyu, duk ta inda zai motsa kura zai tayar, and the most sadness thing is sanadinsa ne auren ya kullu, ta wani bangaren yana ganin kamar har da rashin so ke wahalar da su, domin ya san yadda zafi da wahalar abun yake, da ace yana sonta da zai iya hakuri da ita a yadda ya same ta ko da kuwa na dan lokaci ne. Shiyasa Noor din ta fi ba shi tausayi domin abokinsa yana da future, yana da matar da yake so take sonsa ya aureta har suka yi zuri'a yanzu. Ita kuma ya rabata da wanda take so kuma yanzu yana wahalar da ita, at her early age lokacin da ya kamata ace tana jindadi.

Cikin motar ya koma ya dauki wayarsa sai ya tararda miss calls din Hafiz har biyu, ya dade yana kallon wayar kamar mai tunanin abin yi, har ga Allah be so ya sake yi masa magana akan aurensu ba, domin sakin da Hafiz yayi mata ya bata masa rai, saboda me zai saketa a lokacin da ya same shi ya ba shi shawarar yadda zai zauna da matarsa. Be gama yanke shawarar ba kiran abokinsa ya sake shigowa a karo na uku he pick the call ya kara a kunnensa yayi shiru har sai da Hafiz din ya fara magana cikin farinciki da murna kana jinsa zaka san yana cikin jindadi, daman kuma idan dayansu ya samu wani abun jindadi ko farinciki kamin kowa ya sani sai sun fara labartawa junansu.

“I win the case Doctor, we won it...”

Kareem yayi murmushi jindadi ya rufe even though dai baya cikin farinciki a yanzu.

“Congratulations to us, daman na san zaka yi winning ai, bana da shakkun akanka congrats”

“Thank you, ba karamin dadi na ji ba nasarar nan da na samu, domin babban case ne wannan zai kara min martaba sosai zai daga darajar aikina”

“Haka ne, ko da yaushe kana nasara Hafiz, kai mutumen mai tsananin jajirce da hikima da wayo tun muna yara, sai dai abun da yake ba ni mamaki shi ne yadda ka gagara fahimtar matanka ka gagara saita gidanka, kuma ka gagara fahimtar wacece ne? Wane irin zama ya dace ka yi da ita, kuma ya kamata ka tafiyar da rayuwarta”

“Na fahimci gidana Kareem, na san waye Noor, akwai abun da na fahimta a game ita da zai hanata kuma ni ma ya hana ni jindadin zaman aure da junanmu”

“Ka jefa yarinyar a cikin matsala Hafiz, ka rabata da masoyinta mutumen da she can dia for him, ka siye mahaifinta ka aureta yanzu kuma ka sake ta a wace hujja?”

Yayi shiru be ce komai ba sai tukin motar yake.

“Hafiz, zan roke wannan alfarmar a gareka, zan saka ka aikata saboda ina jin na isa da kai, bayan wannan ba zan sake rokon komai ba, ina son ka maida aurenka da Noor yau... Yarinyar tana wahala ka jefa rayuwarta a masifa, wani abun bakinciki kuma duk saboda ni ne, ka san baka sonta you don't have to married her What kind of wickedness is this? Na taina wayonka Hafiz”

“Wait... What....”

“Ka mai da aurenka da ita a yau Hafiz...”

“Amman kansan bana gari ina hanyar dawowa, na maka alkawari Kareem ina dawowa gidansu zan sauka zan daukota mu tafi gida tare, hakan ya maka..?”

“Yayi, thank you my friend”

“Ka fi karfin haka, amman ban taba jin ranka ya bace irin haka ba, baka taba bani umarni ko rokona wata alfarma irin wannan ba”

Kareem ya sauke ajiyar zuciya shi kanshi ya san he's too harsh for his friend, abun da be saba ba.

“ABun ne naka ya daure min kai Hafiz, na rasa gane ma kake nufi fa yarinyar nan, kuma a rasa wanda zai fada maka abun da ka aikata ba daidai ba ne ko Mama ko Baba”

“Babu wanda ya san ya sake ta sai Aisha ita kuma na gargadeta kar ta fadawa kowa, Mahaifinta kuma na fada masa zan waiwaye shi, tun daga lokacin ban sake amsa wayarsa ba”

“Ka bar abun da ya wuce ya wuce, a fuskanci gaba ita kanta a yanzu na san ta yi sanyi ba zata yi maka laifi ba, sai dai hakan ba zai saka na kasa fada maka ka yi hakuri da Noor ba, ba zan ce ka daina bawa matarka yarda 100% ba, na san maya suna sa wuyar fahimta wuyar sha'ani, but still ka rika bincike kamin ka aiwatar da abu, ka daina compare Noor da AISHA Noor yarinyar kuma bata san komai ba akan aure, Aisha kuma ta waye ta san komai ka tuna ba kai ne first husband dinta ba, kuma Aisha ta yi karatu har degree ba zaka hada ta da Noor da bata ma son zuwa makaranta ba, bawa ta irin wannan wayewar da duniyancin da yan matan yanzu suke da shi, and kishiyace ta koro Aisha daga gidan mijinta na farko, abu ne da ka san shi na san shi, har abada na zata taba son kishiya ba, babu ma macen da zata so kishiya you should think about it Hafiz”


“Hmmm...”

Kawai Hafiz yace, hango soyayyar Noor da yake a zuciyar abokinsa ne ya hana shi walwala da bude mata nata shafin soyayyar a zuciyarsa, yana rayuwa da matar da ba shi ya kamata ya aureta ba, kuma matar da abokinsa amininsa wanda ya zama dan'uwansa yake sonta, kuma a haka ita kuma a zuciyarta tana son wani dabam ba shi ba.

“Sai na dawo...”

Ya fada sannan ya kashe wayar. Kareem ya sauke ajiyar zuciya ya yi ma motarsa key ya karasa restaurant. Yana shiga office dinsa Cashier ya shigo suka fara lissafin abubuwa da suka kamata. Be fita ba sai 6pm Kareem ya saka aka kawo masa coffee ya sha saboda ya samu sauki stressed, domin jin yake jikinsa ya mutu gaba daya har wani abu yake ji kamar bachi kamar ba bachi ba.
Be bar office din ba sai da aka fara kiran sallah magariba. Yana fitowa sallah kira ya shigo wayarsa, yana ciro wayar ya duba. Number Hafiz ce ba tare da wani dalili ba gabansa ya fadi, babu tsoro ko fargaba amman haka zuciyarsa ta rika bugawa da mugun karfi yana ta kallon wayar tana ringing har ta katse ya kasa amsawa. A karo na biyu da aka sake kiran sai hannunsa da zuciyarsa suka hau rawa.

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”

Ya furta domin be taba jin yanayi irin wannan ba, haka kuma Hafiz be taba kiransa ya gagara amsa wayar ba a yayinda take rike a hannunsa sai yau. Sai da aka sake kira a karo na uku sannan ya iya amsa wayar.

“Hello”

“Assalamu Alaikum... Barka dai”

“Barka ina mai wayar?”

Ya tambaya yana jin kirjinsa na masa wani irin nauyi.

“Wayar ya samu hatsari a hanyarsa ta shigowa garin Kano, mun samu wayarsa a motarsa sai muka bude da fingerprint dinsa, da muka shiga log calls na sa sai muka samu number ka ne da yayi waya da ita last”

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un... Yana ina?”

“Mu sami'an kula da hadarukka ne, yanzu haka muna hanyar asibitin Malam Aminu Kano ne tare da shi”

Kareem ya yanke wayar da sauri ya nufi motarsa da gudu ya hau motar ya taka titi kamar wanda baya son rayuwarsa. Kamin su isa asibitin har ya rigasu ya fitowa motarsa ana fitowa da shi daga motar Road safety. Da gudu ya nufi abokinsa dake numfashi daker jini na fita ta cikin kansa.

“Hafiz... Hafiz...”

Haka ya bi gadonsa da aka dora shi akai aka wuce da shi ICU, Kareem ya dora hannu saman kai kamin ya sauke ya nufi motarsa, wayarsa ya dauko ya kira mahaifin Hafiz, yana dagawa ya ce.

“Hafiz din ya rasu ne?”

“Aa yanzu suka shigo da shi, Baba kar a fadawa Mama dan Allah”

“Tohm ni ma ai sun kira ni, gani nan hanyar asibitin”

Ya sauke wayar ya kira mahaifinsa ya fada masa. Yana sauke wayar wani likitan da ya san shi ya fito ya dafa Kareem.

“Doctor Kareem, Mutumen yana son magana da kai, ka shiga ka ganshi ka yi abun da ya dace...”

Kareem na jin haka gabansa ya tsinke ya fadi, domin shi ma likita ne ya gama fahimtar yaren na su. Cikin rashin kwarin guiwa ya shiga sai ya samu likita uku da Nurses suna kokarin tsayar da jini dake ta zuba amman sun kasa, not because of ba su iya ba, sai dan lokacin tafiya yayi mai ajiya zai karbi abarsa, dabara bata tare damuwa.

“Kareem... Allah yayi ba zan samu cika maka burinka ba, ba zan samu dawowa na tafi da Noor ba, ka gyara inda kake ganin na bata, ka san son yarinyar nan Kareem na ga haka a idonta da aikinka, na so ka da farinciki ne shiyasa na so ka aureta, ko yanzu lokaci be kure ba, dan Allah ka auri Noor Kareem ka samawa kanka farinciki, ga Iyeyena nan na bar mana amanarsu, ga Yayana ka ce a kula min da su, na yafewa kowa ka ce kowa ya yafe min, ba zan tashi ba, na san me nake ji na san me nake gani lokacin yayi babu tsayawa...”

Magana kawai yake ba dan yana ganin kowa ba domin an yanke ganin, ana saka masa oxygen yana cirewa yana magana daker. Kareem ya rike hannunsa yana kuka.

“Yaushe Momy ta tafi, ban gama warkewa daga ciwonta ba zaka tafi ka bar ni Hafiz?”

Hafiz ya cire Oxygen din zai yi magana bakinsa ya cika da jini. Sai ya fara kalmar shahada yana tari jinin yana koma masa yana sake fitowa. Mahaifinsa na shigowa wa'adin yana cika rai yayi halinsa Hafiz ya amsa kira...








#KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣3️⃣


©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024

Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar

And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....


You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153


_______•••_______


Wani abun da Kareem be sake yi ba shi ne hawaye. A gaban idonsa ran abokinsa amininsa abokin shawararsa ya fita. Ya saba ganin mutuwa ya saba sanar da ita ya saba jinta but this one is different mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a different way, na farko a lokacin da be yi tsammani ba, kuma a gurin wanda be sakawa ba, mutuwar Momy ta zo masa da sauki domin ta yi ciwo kamin ta rasu, and ko da yaushe tana yawan fadar zata mutu zata mutu tana kan tunatar da su idan sun manta. Amman abokinsa da yake lafiya kalau suka yi waya a hanyarsa ta dawowa har yayi masa alkawarin dawowa da Noor, ta yi hitting dinsa so so so bad. A hanyar da be yi tsammani ba, what a lost, this is a great lost to him ya rasa RAI BIYU within a year...
Ya rasa uwa ya rasa babban amininsa.

Har kara ma mutuwar Momy ya samu zubar da hawaye yayi kuka a lokacin da ya kebe kansa amman mutuwar Hafiz ta yi hitting dinsa in a way da ta tare hawayensa ta tare zuciyarsa daga kuka tun daga asibitin da mahaifinsa yake kuka har aka dauko gawarsa aka dawo da ita gida gurin iyayensa yan'uwa da matarsa suka rufe gawar da kuka shi kam ko kadan hawaye be kusanci idonsa ba. Kuma ta hana idanuwansa runtsawa a lokacin da ya kwana tare da gawar abokinsa domin yin masa sallama ta karshe.. Da kansa ya wanke abokinsa yayi masa sutura sannan aka jira wayewar gari domin kai shi gidansa na gaskiya.
Suna fitowa daga sallah azuba ya shiga cikin gidan ya tambayi mahaifiyar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login