Showing 3001 words to 6000 words out of 133189 words
da zai shiga, dama matarsa da bata da kirki, amman uwa akwai ciwo yanzu zai shiga damuwa sosai, wayyo Allah Kareem...”
Kuka nake sosai ina fadin haka, na dafe zuciyata ina girgiza kai, har cikin kahon zuciyata nake jin tsananin tausayin Kareem ya kamani. Daga Hafiz din har matarsa tsayawa suka yi kallona.
_______________________
Toh fa Anya akwai Uwargida mai karfin zuciya da iya danne kishi ta rike kishiya a matsayin yar'uwa kamar yadda Matar Hafiz ta yi? 🤔
Ko wane hali Kareem yake a yanzu 😪
Ya zamanta kewar Noor zata kasance a gidan Hafiz? Ga tafiyar dai mun fara... 😊
#KhadeejaCandy as always... 👌
#TKZMAPAID PAGE 2️⃣
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
“Daman kin san ta ne?”
Na juya na kalleta sai na girgiza kai har lokacin ina kuka sosai.
“Aa ni ban ma taba ganinta ba, Kareem ne ya ba ni tausayi, zai shiga damuwa sosai yanzu”
“Daman duk mai rai mamaci ne, Addu'a kawai suke bukata, amman wannan kuka haka ai ko mahaifiyarki kika rasa iyaka kenan”
Ban sake ce mata komai ba, wata kila ita din bata shaku da iyaye ba shiyasa bata san zafin rabuwa da su ba. Barrister kuma ya sauke ajiyar zuciya ya kalleta.
“Ki yi hakuri Noor kowa baya wuce lokacin, bari na tafi gurinsa yanzu”
Ya juya ya fita daga dakin, ni ma na bi bayansa, yana shiga dakina ya dauki makullinsa ya fice daga gidan. Ni kuma na kife kan gado ina wani irin kuka sosai mai ban tausayi, Kareem kawai nake hangowa irin halin da zai shiga, ni kaina da na yi rashin uwa a kusa da ni ya kasani wani kalar hali na kunci da kewarta balle kuma ace ta tafi kenan har abada, ga shi ba dadin matarsa yake ji ba, Allah kadai ya san halin da zai shiga a yanzu.
Ban wuce minti talatin da shiga dakin ba, macen dake fadar jiri na daukarta bata iya bandaki sai gashi ta kawo kanta a bangare kamar ba ita ba.
“Amarya har yanzu kukan ne? Ayi hakuri mana duk mai rai a mamaci ne”
Ta zauna kusa da ni tana fadar haka har da kai hannu ta shafa bayana alamar rarrashi.
“Hmmm ina mamakinki a haka ma kina tausayin Kareem, ina ga ace kin san abun da aka boye miki?”
Na tashi zaune ido da hawaye na kalleta.
“Kamar ya? Bata mutu ba kenan ko kuma me?”
“Aa ta rasu fa, ba akanta nake magana ba akam Kareem din kansa”
“Me kike nufi?”
“Sannu a hankali zaki san abubuwa da yawa kanwata, matukar idan muka yi sirri zamu haka rame mu bunne babu wanda ya ji, yanzu ma din ma zuwa na yi na roki wata alfarma a gurinki”
Na goge hancina ina kallonta.
“Ta me?”
“Dan Allah ko da yan'uwanki ko yan'uwan Barrister sun shigo karki fadawa kowa cewar ba ni da lafiya, irin wannan rashin lafiyar ta aljannu ba abar yayata ba ce, kuma ba kowa zai fahimta ba, duk abun da aka yi a gidan nan ko tsakanina da ke ko da mijinmu karki bari kowa ya ji, ko a musulumcin ana son rike sirri, shi ne yarda kuma namiji yana son mace mai tsanannin rikon sirri, tsakaninki da shi dabam, haka kuma sirrin dake tsakanina da ke dabam”
Na daga mata kai cike da gamsuwa.
“In Shaa Allah Madam ba zan fadawa kowa sirrina dake ba, kuma ba zan fadawa kowa baki da lafiya ba”
Ta yi murmushi
“Madan kuma?”
“Haka na ji Barrister yana fada, ban san sunanki ba”
“Sunana Aisha, sunan Madam suna ne da Barrister ya saba min da shi, ni kuma nake masa lakani da Barrister, amman ke zaki iya kiransa da sunansa kai tsaye daman ba son shi kike ba balle na ce ki yi masa sunan soyayya, ni kuma ki kira ni da Sunana Aisha bana son wani Anty ko Yaya ko Maman wani balle Madam”
Me yasa Hafiz ya fada mata bana sonsa? Gashi sai yawan nanatawa take ina jin wani iri, ko da yake gaskiya ta fada bana son sa dole ce aka yi da kuma kaddarowar Ubangiji.
“Tohm In Shaa Allah”
“Yauwa, bari na shiga ciki na yi wanka na ji jikina ya dan saki”
“OK”
Ta tashi ta fice daga dakin, ni kuma na shiga bandaki na wanke fuskata ina jin cikina na kukan yuwan.
Misalin Goma mutane suka fara shigowa yan ganin amarya daga yan'uwansa daga bisani kuma nawa yan'uwa suka fara zuwa. Babu wanda na jidadin zuwansa irin Hana domin jiya ba da ita aka zo ba, a yau kuma ita kadai ce zan iya fadawa damuwa. Domin na kasa sakewa kowa ya kalli fuskata ya san na sha kuka sosai idona ya nuna haka. Wata kila wasu daga yan'uwa mahaifina da suka san bana maraba da auren za su yi zaton wannan kukan na kiyayyar auren ne na yi, yan'uwan Barrister ma sai na ga jikinsu yayi sanyi sosai sai kallona suke kasa kasa ba su wani dade ba suka tafi bayan Zainab da Yar Fulani da Hana sun girka abincin rana. Haka Aisha ta shigo aka yi ta hira da ita sai kusan karfe hudu sannan Hafiz ya dawo gidan ba tare da ya shigo bangarena ba ya dauketa suka tafi gidan mutuwar.
Sai da mutane suka fara ragewa sannan Hana ta saka ni a daki muka zauna ta ce.
“Noor ina dalilinka na kuka uwar abokin mijinki ya mutu? Uwar mijinki ce balle hakan ya dame ki? Ina ruwanki?”
“Hana akwai tausayi fa, Wallahi Kareem yana da kirki kawai dai raba ni da Zafeer da zama sila ne nake jin na tsane shi, kuma ki duba yadda muka ji da Mama ta tafi balle kuma ace uwarta ta mutu fa”
“Akwai tausayi amman be kamata ki rika kuka haka ba, ke dai kina kukan auren ne ko? In ba haka ba ban ga ta inda mutuwar uwar wani ta shafe ki ba, Noor ki natsu dan Allah kin ga auren nan an riga an daura ki yi hakuri ki zauna ki bar wa marar da kunya, gashi kin samu kishiya ta kwai inda har ba munafurci take ba to tana da halin kirki, yanzu idan wani abu ya faru kin san Baba ke zai dorawa laifi, kuma Mama zata shiga tashin hankali, gidanki yayi kyau sosai, kowa sai magana yake, kuma mutumen yayi miki hallacci sosai be kamata ki bijiro masa da wani abun na rashin dadi ba, ki duba yadda kika bar gidanmu yanzu ke mai yanci ce sai abun da kike so kike dafawa, ko ki ci haba Noor dan Allah ki natsu”
A nan kuma sai na ji kewar rayuwar gidanmu ta dawo min sabuwa, sai na ji babu dadi. Ban raina kaina ba sai da za su tafi da magariba, bayan sun gyara min gidan ko'ina fess, suka jera min lefen da suka zo da shi a cikin Wardrobe dina. Har gurin Gate na rakasu na tsaya daga jikin gate din ina kallonsu har na daina hangosu sannan na juyo na dawo cikin gidan kamar wata marainiya, ina ta jin kadaici da kewar gidanmu, gashi an kawo ni a gurin wanda bana so kamar yadda matarsa Aisha take ta yawan fada. Duk yadda ake yawa kyaun falon da dakina ni dai na runtse ido ban ga kyau a makamata ba. Wata kila saboda hankali be kwanta da auren ba ne ko kuma dai saboda kyalkyali duniya baya gabana a yanzu. Na ji kewa na ji kadaici da tsoro kamin Hafiz ya shigo bangarena domin na ji tsayawar motarsa tun bayan da aka gama sallah Isha'i sai dai be samu shigowa bangarena ba sai tara da yan mintuna.
Wike na yi masa da ido ina kallonsa kamar mai jiran ya fada min wani abu, sai yayi murmushi ya tsakali hancina da keys din motar dake hannunsa.
“Wannan idon da aka sakar min fa? Babu sannu da zuwa babu komai”
Na sauke idon kasa ina jin haushi yadda ya taba min hanci.
“Amaryata, kin yi sallah”
Na daga mishi kai ba tare da na kalleshi ba, sai ya cire hular kansa ya aje ya fara kokarin cire tufafinsa, ina ganin haka na tashi na koma falo na zauna na bar masa dakin. Sai kusan goma ya fito daga dakin sanye da wata sabuwar Shadda, yana ta kamshin turare ya zauna kusa da ni.
“Me kika ci?”
Ya taba bakina sai na kauce.
“Na ci abun da aka dafa kadan”
“Ta so mu tafi Wani guri mai kyau mu siye wani abun sai mu dawo, ban samu riko komai ba saboda mun dawo gida jikin Madam sai a hankali yayi zafi sosai, amman dai na kira kanwarta zata so ta taya ta kwana”
“Ni ba sai na je ba, zaka iya tafiya ka siyo ai”
“Idan haka kike so, ba matsala”
Ya kai bakinsa zai sumbanci bakina na kauce da sauri na tashi tsaye na bar gurin na koma dayar kujera na zauna. Murmushi na ji yayi mai sauti ya girgiza kai sannan ya mike tsaye.
“Hafiz”
Na kira sunanshi sai ya juyo ya kalleni.
“Amaryata ba ki ji sunan ya miki girma ba? hafiz kai tsaye”
“Toh ai sunanka ne?”
“Haka ne to amman yanzu ni ai mijinki ne”
“To ya zan ce maka? Mijina?”
Yayi murmushi.
“Fada min abun da kike son na siya miki?”
Na sauke idona kasa ina taba hannuna.
“Daman ina son na tambaya Ya Kareem yake?”
“Da sauki?”
“Yayi kuka?”
“Wanda ya rasa uwa ai dole yayi kuka Noor, uwa ba wasa ba”
A take idona ya cika da kwalla.
“Yayi kuka sosai?”
“Namiji ne shi ai, a boye zai yi”
Na dada noce kaina kasa domin bana son ya ga alamar hawaye a idanuwan nawa. Bw sake ce min komai ba ya shiga dakina be jima ba ya fito ya fice. Misalin Sha daya ya rabi ya shigo bangaren nawa a lokacin ina kwance kan gadona na yi shiruuu ni bana tunani kuma bana kuka, babu damuwa babu kuma farinciki a tare da ni. Not too good not too bad. Ina kallonsa har ya sauke ledadin dake hannunsa sannan ya karaso inda nake kwance ya shafa bayana, hakan ya saka ni hanzarin tashi zaune na buge hannunsa.
“Ka daina taba ni bana so Hafiz”
“Hmmm zaki saba”
Ya fada yana murmushi, ni kuwa gabana sai faduwa yake ina yawan tuna labarin da Aisha ta fada min akansa. A daren mun samu aiwatar da sallah nafila da ba mu samu damar gabatarwa ba a daren da ya gabata wadda shi ne darenmu na farko. Ya cilasta min cin naman kazar da gas meat da ya siyo daga wani restaurant din, duk yadda nake da kwadayi da son dadi sai na kasa sake jiki na ci komai gaba daya komai ya fice min a kai. A gurin kwanciya ne aka fara samuwar drama domin ni ba zan yarda na kwanta gado daya da shi ba, musamman da na lura da yadda yake ta son taba a lokacin da muke cin abinci, baya ko taya abokinsa jimami kirkiri zai taba yar mutune saboda babu kunya a idonsa.
“To yanzu ya kike so ayi?”
Ya tambaye ni yana sanye da kayan bachi kalar nawa da ya saka min a lefe.
“Ka kwanta a kasa ko kuma ni na kwanta a kasan kai ka hau gadon”
“Ba wani abu zan miki ba Noor, ba zan miki komai ba”
Na ga gaskiyar hakan a muryarsa da fuskarta amman tsoro da yawan tunawa da maganar Aisha ya hana ni yarda da shi.
“Zan kwanta a karshen gado kai ka kwanta a farko?”
Sai na ga kamar ransa be yi dadi ba, sai dai hakan be hana shi amincewa ba kuma be hana shi karfafa min guiwa da murmushi ba. Yadda na fada haka aka aiwatar ni na kwanta a karshen gadon shi kuma a farko da na ji ya motsa sai na tashi zaune, gashi na hana a kashe wutar dakin. Shi kuma ya tsare ni da ido sai kallona yake ya ki ya juya ya ki yayi bachi, ni kuma da zarar na fara bachin sai na kokarin kwatar kaina kar yayi min nauyi mu hade a guri daya. Dariya na ji yayi yana shafa kansa
“Kina wahalar da kanki Noor, shureshure be hana mutuwa, kuma ni idan na ce zan yi ko ba zan yi ba, ta zauna domin magana daya nake yi, so ki matso nan ki kwanta kina bukatar hug ki yi bachi mai dadi”
Na yi kamar ban ji ba, na ki na motsa ma balle har ya ga dama ta, a haka dai har bachi barawo ya sace ni, wannan karon ban sake farkawa ba sai da ni da shi muka ji karar bugun kofar falo da karfi.
“Subhanallahi Lafiya?”
Ya fada yana tashi zaune, ni ma na tashi zaune cike da tsoro jikina har rawa yake domin na ji bugun kofar ne a cikin bachi hakan kuma ya tsorata ni sosai.
“Bari na duba”
Na sauko da kafafuwansa a kasa ya nufi kofar dakin ya bude ya fice, tsoro be bar ni na tsaya jiran tsammani ba na bi bayansa na tsaya daga jikin kujerar falon dake nesa da kofar falon. Wata matashiyar yarinya ce da ba zata wuce shekaruna ba ta shigo falon da sauri tana kuka.
“Wallahi Yaya ba zan iya da Anty Aisha ba, ihu take tana makure kanta ta ki ta yi bachi, haka ta shiga dakin su Ikram tana ta dukansu cikin daren kuma ba su mata komai ba, sai zaro ido take”
hafiz ya juyo ya kalleni sai ya miko min hannunsa.
“Zo mu je?”
Na lake kafada a bata fuska alamar ba zan je ba, ahh daman idan ba cuta ba ta ina zai ce na zo muje kuma ya ji kanwarta na fadar tana makure kanta har ta doki yaranta.
“Okay Na'ima shiga ku kwanta tare, bari na je na dubata”
Yarinyar da ya kira da Na'ima ta nufo ni shi kuma ya fadada kofar ya fice.
“Sannu an tashe ku kuna bachi ko?”
“Ba komai ai, zo mu kwanta a nan shi sai ya kwana tare da ita a can”
“Tohm”
Ta shigo har cikin dakina. Ni da ita muka kwanta a kan gadon, a nan kam na samu natsuwa ni da ita muka yi bachinmu cikin aminci da kwanciyar da hankali.
KAREEM POV.
Sai da ya runtse ido ya girgiza kai sannan ya dan samu saukin jirin da yake gani, sai ciwon kai kam kamar an kara masa wani haka yake ji, ba wani uban nauyin da zuciyarsa ta yi. Cike da karfin hali ya taka ya karasa gurin da Yusura take zaune ya cire drip din dake lake ya saka mata wani sannan ya koma ya zauna ya dafe kansa. Can kuma ya dago kai ya kalli matarsa da har yanzu bata san inda hankalinta yake ba tun bayan da uwar da take kallo a matsayin tata ta kwanta dama, wata kila kaddarar ta mata nauyin dauka ne shiyasa kwakwalwarta ta rikice, domin mutuwa gaskiya ce mai tsananin daci, kuma nauyi ne da idan ya hau kai ba a iya saukewa. Ta rasa mutane masu muhimmanci a rayuwarta tun kamin girmanta ta saba da rashi, sai dai mutuwar Momy ya zo mana a wani ma'auni mai tsanananin nauyi da ya wuce sikelin awa, a yanzu jin take bata da kowa kuma bata da gata domin ta rasa macen da ita ce komai nata kuma ita ce gatanta.
Kallonta yake irin kallon da be taba samun damar yi mata ba, tun bayan da ya aureta, ashe ta zama babbar mace wasu abubuwa sun sauya daga hallitarta, sai dai kyaun da Allah yayi mata yana nan har yanzu ko da yake kyauta baya gabanshi sai dai ba zai iya karya ba matarsa tana da kyau. Dauke kansa yayi idonsa na tara kwalla tunawa da ranar da Momy ta fada masa ra'ayinta na son ya auri yar'uwarsa. Wannan karon ba bakinciki auren yake ba bakincikin rasa first love dinsa yake, be saka mata ran mutuwa nan kusa ba, yanzu da waye zai zauna yayi hira irin wadda ya saba yi da ita, wa zai tsokana wasa da wa zai yi shawara...? Shi kam dai be san zafin rashin rai ba, sai a wannan karon ganin yake kamar wata karya ce dake kokarin zame masa gaskiya tsakanin jiya zuwa yau saboda rashin saka mahaifiyarsa a ido da be yi ba. Wai Momynsa ta tafi kenan tafiyar da babu dawowa?
“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”
Ya furta a hankali yana saka hannunsa ya dafe kansa. Hajiya Hassana ce ta shigo dakin dauke kofin fura.
“Kareem karbi ka sha, tun jiya na lura baka ci komai ba, tun shekaranjiya ba idonka har ya fada”
Ba dabi'arsa ba ce yi ma na gaba da shi musu dan haka na karba ya sha rabi kofin ya aje yana amsa mata.
“Eh ni ma na yi wannan tunanin idan har bata samu sauki ba yau dole na kaita asibiti”
“Dole kam, Allah dai ya sauwake mutuwa ai ba ku kadai kuka ji ba, ni ma na rasa abokiyar zama mai kirki mai hali na gari”
Hajiya Hassana na fadar haka ta fashe da kuka, daman tun rasuwar Momy take ta kuka har ta bawa mutane tausayi. Kareem ya mike tsaye ya fice daga dakin, harabar gidan ya fita gurin da maza suke zama ya zauna kusa da Hafiz yana amsa gaisuwar da ake masa. Kadan daga cikin dabi'u na mutuwa shi ne bata manta gidan kowa, kuma idan ta ziyarta, sai ta bar tabon da ba zai goge ba kuma ba za'a manta da ita ba, mussaman washe garin sadakar uku a ranar kuka yake sosai, daga ranar kewa zata fara domin mutanen dake bada hakuri idan ana kuka sun watse mutum kadai za a bari da kuncinsa a zuciya.
Ranar da Momy ta cika kwana hudu da rasuwa, Yusura ta samu karfi jiki a yayinda Kareem kuma ya rasa nasa saboda garkuwar jikinsa dake yin kasa tana son kwantar da shi. Har suka dawo gida wasu ba su daina kira suna masa gaisuwa ba, wasu kuma da kansu suke zuwa su yi