Showing 57001 words to 60000 words out of 133189 words
Chapter 20 - Taki Zaman Aure Book 2 Hausa Novel Complete
har na na yi sha'awar ina ma ace shi ne mahaifina ba Baba ba, zaunawa yayi a falon yana ta min nasiha akan hakuri da rayuwa na halin da na samu kaina da kananan shekaru, na yi masa godiya ya saka hannunsa aljihu ya ciro 10k ya ba ni.
“Aa na gode”
A bakin gaskiya ta ba zan karba ba, domin ko na karba ban san miye zan yi da su ba a yanzu. Sai dai na lura hakan be masa dadi ba domin rufe ni yayi da fada a dole na karba na yi masa godiya.
“Tafi bangaren Hajiya ki ce na ce cikin yaran nan duk wanda yake nan ya sauke ki gida”
“Tohm”
Na mike tsaye na yi ma Mama sallama sannan na fice daga falon yana ta kallona. Bangaren Hajiyar na dawo na sanar mata abun da Alhaji ya fada sai mutumen dake tsaye a gabanta yayinda take zaune ya juyo ya kalleni. A nan ma wani mamakin ya kara kama ni, mutumen nan da ya taba yunkurin biya min kudin siyayyar da na yi a wani dare da muka fita tare da Hafiz.
“Kamar na sanki?”
Na bude baki kamar zan yi magana sai kuma na yi shiru, ban san me zan ce ba, ni dai ina da saurin gane mutane shiyasa na gane shi.
“Noor ce Yar wajen Anty Amarya ce, ita ce wadda mijinta ya rasu”
“Ai ban sani ba, Allah ya jikanshi da Rahama”
“Ameen, ku tafi tare sai ka sauke ta ka wuce, Noor bari ga Abdull zai fita yanzu sai sai ya wuce da ke, ki jira shi a waje”
“Okay”
Na juya na fito daga ciki, ban san wacece motarsa a cikin motocin gidan ba dan haka zauna a balcony har ya fito.
“Kika zauna a kasa?”
Bance komai na na mike tsaye na bi bayansa muka isa gurin wata sabuwar mota, sai da ya fara shiga sannan na bude na shiga front seat. Ba tare da yace min komai ba yayi reverse ya fice daga gidan.
“Ina ne unguwarku?”
A lokacin da na dago sai na ga idonsa akaina suke. Na fada masa na sake maida kaina kasa kamar ba ni ba. Na ji lokacin da wayarsa ta yi kara ya amsa.
“Hello Safeena...”
Sai kuma yayi shiru, yana sauraren abun da ake fada masa.
“Yanzu na fito gida, amman zan biya ta can, sai na zo miki da shi, shi kadai kike so ko da wani abun?”
Na yi shiru ina saurarensa kamar wata Munafuka kamin na ji ya ce.
“Okay sai na dawo”
Ya aje wayar ya dago zan kalleshi idona suka fada cikin nasa da sauri na dauke kaina ina jin sautin murmushinsa. Ban sake kallon gefen da yake ba har muka isa unguwar.
“Ka sauke ni a nan unguwar bata da kyau can ciki”
Na fada.
“Karki damu, amanarki aka ba ni sai na kai ki har gida”
Yadda ya fada haka ya aiwatar har kofar gidanmu ya isa da motarsa ya faka, ni kuma na bude na fito zan rufe kofar ya ce.
“Ba godiya”
Ban ce masa komai ba na rufe motar, na gode masa sai ka ce rokonsa na yi ya kawo ni. Sai da na shiga gida sannan na ji motarsa ta bar kofar gidan.
KAREEM POV.
Yana gama sallah asuba ya shiga kitchen hadawa yaransa breakfast. Domin Yusura bata musu komai tun da ta dawo gidan, Kullum shi zai hada musu breakfast ko kuma ya saka aika musu daga restaurant dinsa kamin su tashi break.
And now cooking is one of his favorite things, yana samun nishadi a girkin, musamman idan yaran suka farka suka same shi a kitchen suna hayani yana aikinsa har ya gama, ya karya tare da su wani sa'in kuma ya zuba musu na su, ya tafi da nasa a office ko kuma su su tafi da na su school shi kuma ya ci a gida. Idan ya fita sannan Yusura take saukowa ta gyara ko'ina ta dora na rana. Tun da ta dawo gidan be taba leka dakinta ba, be taba ce mata uffan ba, ita ma kuma bata bari sun hadu ba, da zarar ta ji motarsa ko ta san lokacin dawowarsa sai ta shige dakinta.
Yau ma sai da ya raka su har gurin bus sannan ya dawo ya zauna ya ci nasa breakfast. Bayan ya gama ya mike tsaye ya shiga dakinsa yayi wanka ya shirya cikin kananan kaya ya fito yana rike da lab coat dinsa da wayarsa sai kamshi yake zuba. Yayi kyau sosai ramar da yayi ta kara masa kwarjini da haifa. Sai da ya fice daga falon sannan Yusura ta sauko a zatonta ya fice gaba daya, dinning ta nufa ta tsaya tana kallon kayan karyawar da ya shirya, biredin da ya gasa ta dauka taba tabe baki ta shinshina ta aje.
Sannan ta ja kujera ta zauna ta bude flask din ruwa zafi, a daidai lokacin Kareem ya turo kofar falon ya shigo domin daukar wallet dinsa da ya manta a dakinsa. Kallo daya yayi ma gurin da take zaune ya dauke kai ya haura sama ya dauko wallet dinsa ya sake fice. Yusura bata taba jin kunya irin ranar ba, bayan amincewa da aurensa da ta yi wannan ne abu da na biyu da take bakinciki a rayuwarta, ji ta yi kamar ta fasa komai na gidan dan bakinciki.
Tuki yake a hankali har ya isa asibitin, ya faka motarsa a gurin da aka rubuta Dr Kareem sannan ya fito ya dauki kayansa ya rufe motar ya shiga cikin Babbar asibiti ana miko masa gaisuwa yana amsawa. Office dinsa ya shiga ya fara duba takardun dake gurin sannan ya fita ya fara duba marar lafiyar da aka aje da ya kamata ya duba su.
After ya gama ya dawo ya zauna a office dinsa patient din dake shigowa suka fara shigowa yana dubata. Third person da ta shigo ita ce Safeena, tana sanye da dogon Hijabinta har kasa sai dai hakan be boye cikin dake jikinta, har ta zauna ita yake kallo. Sai da ta aje jakar dake hannunta sannan ya jingina baya ya kwanta jikin kujerar yana kallonta.
“Wai ke wace irin yarinya ce Safeena?”
“Ni din wata yarinya ce, mai wuyar warke ciwo, wata yarinya ce da ka koyawa soyayyarka kuma kake kokarin guduwa bayan ka yaudareta da farko”
“Gargadin da na yi miki, da kuma tazarar da na baki daga lokacin da muka yi haduwar karshe zuwa yau bata fahimtar dake, na rumgumi kaddarata, ke ma ki rumgumi taki?”
“Ka rumgume kaddara saboda Yusura tana sonka tana kyautata maka a yanzu? Ko kuma daman can karya ka yi min kace bata kula saboda kullum ka rika samun biyan bukatarka da ni? Ka yi breaking heart dina da farko yanzu kuma bayan na saba mu'alama da kai na saba da kwanciya a kirjinka na saba da soyayyar kake tunanin sake guduwa ka bar ni?”
Ya mike tsaye daga zaunen da yake ya nufi windows dinsa ya bata baya.
“Kana da kyau, Kareem kana da kudi amman duk wannan be tabbatar min da ina sonka ba sai da mu'amala ta hada mu, all this while na kyale ka ne saboda ina dauke da cikin nan”
“Me kika zo yi yanzu? Tashi ki fice daga office din nan”
“Baka da wannan damar ba saboda da kai na zo ba, saboda cikin nan ne, na dawo da awon cikin nan a nan ne, a nan zan yi ta zuwa har zuwa lokacin da zan haihu”
Ya dafa Window ya rike kansa.
“Namiji zan haifa suka ce, kuma ina alfahari da haka”
Kareem ya dauki lokaci a haka kamin wani tunanin ya zo masa sai ya juyo da sauri ya kalli cikin na ta sannan ya kalli fuskarta, sai ta yi masa murmushi.
“Fita ki bar office din nan”
Ya nuna mata kofar, zata sake magana da daka mata tsawa har sai da ta zabura.
“Fita ki bar office din nan na ce”
Ta mike tsaye da sauri ta dauki jakarta tana kallon yadda ya hade fuska kamar be taba ganinta ba, ta fice daga Office din. Dawowar yayi ya zauna kan kujerar ya dafe kansa ya runtse ido yana numfashi da karfi, ya girgiza kai kamin ya daga hannunsa ya buga a tebur din yana jin wani irin bakinciki marar misaltuwa...
It could be a joke maybe tana gwada shi ne, if not ai tana da hankali matukar ba wata manufa take da ita akansa ba ba zata taba sha'awar haihuwa da shi alhalin tana da aure ba, ta dauki dawainiyar cikin da ba na mijinta ba ta kai masa yayi komai, ba zata fara ba. Abun da zuciyarsa ta raya masa kenan har ya ji ya samu saussaucin cigaba da aikin da yake. Sai da lokacin tashi aikinsa yayi ya tuna da ba shi da abokin hira ko shawara a yanzu domin Hafiz is no more balle ya fada masa hasashensa ko damuwarsa.Tafiyar Ya Nabil karatu ta zame ta bude min wani gurbi a gidan. Domin ruwan da yake debo mana da safe yanzu nauyin ya koma kaina, ni nake cika gidan da ruwa ga jikin nawa ba mai son wahala ba ne amman haka nake daurewa ina yi saboda gujewa hayaniyar Baba bana son ya jefe ni da wata kalmar marar dadi a yanzu. Haka ma ba fita nake son yi ba, saboda idanuwan mutane yana kaina, idan na hadu da kanen Zafeer har jefa min magana suke kamar ni na so mutuwar auren ko kuma zaman gidan.
A haka dai na daure na danne zuciyata ina cigaba da rayuwa a gidan ubana. Ranar wata labara Anty Larai ta kawo mana ziyara har da tsarabarta domin ta dade rabonta da gidan. Rabon da na saka a ido kuma tun a gurin gaisuwar Hafiz. Na yi murna sosai da ganin tana cikin Gwagganina masu hankali da kamanta adalci daidai gwargwado. Ina zaune kusa da ita nabban danta Ridwan Wanda ya kasance cousin ne a gareni sai tsokana ta yake, ni kam baki ya mutu bana cewa komai, Hana ce take ramawa sai Umma dake dan jefo magana sama sama.
Gwaggo ta shafa kaina zuwa bayana tana murmushi ta ce.
“Ka bi ka saka min yarinya a gaba, saboda yanzu ka samu ta yi lafiya ko? Da ada ne ai ba zaka iya da ita ba”
“In ji waye ko a da ne zan iya, kawai ina daga mata kafa ne”
Anty Larai ta bude jakarta ta dauko goro ta gutsira tana fadin.
“Nabil an tafi ko? Ya zo min bankwana ai, Allah yasa ayi karatu cikin nasara”
“Ameen”
Na amsa ina daga kai na kalli Ridwan dake shirin tafiya.
“Zaki dare nan?”
“Aa idan dai ka yawato ka samu abun da zaka samu sai ka dawo ka dauke ni mu tafi gida”
“Yaya Ridwan har yanzu Napep din kake ja?”
“Toh ya za'ayi abincin a nan yake”
Ya amsawa Hana dake tambayarsa domin tun tashinmun, Yaya Ridwan ba shi da wata sana'a da ta wuce jan Napep, da ita ya rike gidansa ya yaransa da matansa biyu har ma da mahaifiyarsa.
“Allah ya taimaka”
Cewar Umma, dukanmu muka amsa da Ameen sannan ya fice. Shimkafa da miya Umma ta girka saboda zuwan Anty Larai, bayan mun ci mun yi sallah Hana ta dauki awara ta fice gurin sana'ar da ta zame mata dole, ni kuma na zauna da Anty Larai muna ta hira, a cikin hirar nake gutsura mata irin zaman da muka yi da Aisha da yadda yan'uwansa suka jajirce ba za su ba nu gado ba.
“Daman can Allah ya gani, zuciyarta bata natsu fa yarinyar nan dari bisa dari ba, mata makircinsu yana da yawa, ke kuma ba wayo ne da ke ba kuma babu mai tsawata a tare da ku, dama ace irin gidanmu ne da muke hade kin ga wani abun ko dan ganin idon uwar miji dole a bar shi”
“Ni kadai nake zaune kuma kowa da bangarensa, amman hakan be hana ta cutar da ni, gashi ya yarda da ita, komai aka fada masa akanta baya yarda”
“Ki barta da Allah, yanzu ai mai rabawa ta raba, Allah ya ba ki na gari ita kuma sai ta je can ta karata”
Na yi shiru ina zane a hannuna da karen tsintsiya, kamin na kira sunan Gwaggo.
“Anty Larai”
“Na'am Khadijatu”
“Anty Larai, alfarma nake nema a gurinki, na san Baba yana jin maganarki, dan Allah ki roka min shi yayi hakuri yace ya yafe min na yi magana da Zafeer”
Na kora bukatar tawa ne ba tare da na kalleta ba, domin ina jin nauyin kallon idonta a yanzu.
“Zafeer din ya dawo ne? Aiko ya kai masoyi kuma lallai yana sonki da gaskiya bawan Allah nan”
“Be dawo ba, yana da zuciya sosai wata kila ba zai sake sona ba har abada, amman ni ina son a duk lokacin da na ganshi ko kuma na samu dama na masa bayanin da zai gamsar da shi cewar ba wai na ki aurensa saboda ba shi da kudi ba ne, na lura yan'uwansa har yanzu ganin suke kudi na bi na bar Zafeer”
“Idan har yana sonki da gaske zai dawo, ai mai sonka be ganin ramar ka, be ganin tsufanka, kuma shi ma mahaifinku ai be dace ya shata muku layi mai kauri irin wannan ba, saboda zuciya bata da kashi”
“Dan Allah ki masa magana, yace ya yafe min”
“Zan mishi magana idan ya shigo, noor har yanzu kina son yaron nan ko?”
Na daga mata kai ba tare da boye ko jin kunya ba, zan iya fadar ina son Zafeer a gaban, duk kuwa da na san a yanzu yayi min nisa. Sai na ji ta yi dariya tana buga bayana.
“Aiko da har ina cewa Ridwanu ya shigo ko Allah zai ba shi sa'arki, sai ayi tuwona maina tankaden bakin gado?”
Murmushi ne kadai abun da zan iya yi na kwanci kaina a wannan lokacin kuma shi na yi, sai dai ko kadan manufar da take son isarwa a gareni ba mai yiyuwa ba, sai idan cilasta Baba zata yi yayi min auren dole. Baba be shigo gidan ba, sai da yamma liss ya dawo a gajiya. Na debi ruwan wanka na kai masa yayi wanka ya fito ya zauna kusa da yar'uwansa yana cin abinci suna gaisawa.
Ina alwalar magariba na ji tana yi nasa maganar Zafeer.
“Ai wannan duk da ne, yanzu kam komai ya wuce, ko lokacin da na yi mata wannan furucin ta fusata ni ne shiyasa kuma na lura a wacan lokacin tana son ta biyewa zugarsa ne ta bijirewa umarnina, amman yanzu komai ya wuce”
“Duk da haka dai ka ce ka yafe ka san bakin iyaye lalle ne”
“Haka ne, toh na yafe Yaya Larai kina shagwaba Noor”
Ta yi murmushi ni ma murmushin na yi ina jindadin janye takukun da Baba yayi tsakanina da Zafeer. Daki na shiga na yi sallah bayan na gama na fito na yi ma Anty Larai godiya a lokacin Baba yana masallaci. Shigowar Ridwan da mintuna kadan Baba ya dawo daga masallaci suka gaisa Ridwan yayi masa alheri sannan ya fita waje jiranta. Ni kuma na yi mata bankwana Baba ya rakata har waje suna tafe suna hira har suka fice daga gidan.
Hana na shigowa na labarta mata cewar Baba ya daga min kafa a yanzu, yace ya yafe min na yi magana da Zafeer, na yi zaton zata taya ni farinciki ne kawai sai na ji ta fashe da kuka marar sauti. Hankali ya tashi da sauri na dafata na dago kanta.
“Hana lafiya?”
“Na gaji da rayuwar gidan nan Noor tun da Mama ta tafi ba mu da jindadi babu walwala, zuwan Umma ya kara mana matsuwa kuma ban mu isa mu yi magana ba, ni ban taba talla ba, sai wannan karon idan na fita da la'asar ba zan dawo ba sai bayan Isha'i dole sai na siyar da komai idan ba haka ba idan na dawo sai ta fara fada tace keta nake son mata. Baba kuma ba zai shigar mana ba sai ita, kawayena a yanzu babu mai talla sai ni, maganar nan har ya kai makarantar mu na boko, gashi yanzu mun fara jawaba, muna karewa zata oya kirkiro wani abun da zai hana ni zaman gida da safe, yanzu kina gani yadda karatun addini na bar shi saboda tallar nan, gaba daya rayuwar gidan nan ta isheni Noor ji nake kamar na gudu”
Tausayinta da kuma na kaina ya kamani, idan har ita zata fadi haka to ni nace me, kashi uku na ukuncin rayuwarta data gidan Hana bata shiga daya ba, domin ita har yanzu bata kula kowa ba balle a rabata da wanda take so kamar yadda Baba yayi min. Bata yi aure ba balle ta hadu da kishiya irin Aisha wani abun na rayuwar har yanzu bata san ya zafinsa yake ba.
“Ya muka iya? Tun Mama tana gidan nan muna cikin takurawar Baba balle kuma yanzu da bata nan, ni ina ganin idan kin kare karatunki kawai ki koma gurin Mama ki zauna, za ki jidadi kuma mijinta da take aure a yanzu yana son mutane ba kamar Baba ba”
Ta kalleni hawaye na mata zuba.
“Amman kina ganin Baba zai yarda? Ba zai yarda?”
“Me zai hana idan ma be yarda ba ki yi ma Anty Larai magana zata saka baki, kin san kuma Baba yana jin maganarta”
Ta fara share hawayenta.
“Allah yasa”
Ta mike tsaye ta cire hijabinta ni kuma na tashi na fita waje gurin aikin gyaran wake da nake kullum da dare. Tiya uku na zuba a tray na shimfida matacciyar tabarmarmu na zauna kamin na saka hannuna a waken wani yaron unguwarmu ya shigo wai ana sallama da Noor.
“Je ka ce waye?”
Umma ta ba shi umarni yaron ya juya ya fita.
“Gashi Malam baya nan balle na ce a nemi izini gurinsa, yaran yanzu kuma ba natsuwa ce da su ba, musamman zaurawa”
Tana maganar tana kallo, wata kila so take na yi mata ba daidai ba ta fada min ba dadi ko kuma ta hada ni da Baba, idan ba haka me miye na cin fuskar, ita ba zarwacin ta yi ba kamin ta auri Baba, su zaurawan dabam suke da sauran mata.?
“Sallamu Alaikum, ya ce wai wanda ya saba zuwa”
Ina jin amsar yaron zuciyata ta raya min Kareem ne, wata