Showing 96001 words to 99000 words out of 133189 words
Chapter 33 - Taki Zaman Aure Book 2 Hausa Novel Complete
ba. Da zarar ya hada min na sha sai bachi yayi gaba da ni, ko motsi ba zan yi ba sai safe.
Ina tsaka da shafa face cream ya shigo dakin ya aje min cup din natural orange juice. Sannan ya nufi wardrobe ya bude ya dauko kayan bachinsa ya saka.
“Kina bukatar wani abu?”
Na kalleshi kamar na ce ina da bukatar ka, yau wata shida kenan ban hada shimfida da mijina ba, tun cikina na wata daya da yan kwanaki ya nade sha'awata ya jefar saboda kawai na ki yarda a zubar da cikin. Sai kuma wata zuciyar tace na daure mana na zuba masa ido tun da haka ya zaba.
“Aa”
“Okay to zaki yi kallo?”
“Aa bachi zan yi”
“Yanzu ai kin lalace da bachin dare, da dare yayi sai bachi kamin tara na dare ta yi har kin kai Morocco, Allah yasa ba raguwa ko rago zaki haifa ba, wannan lalaci yayi yawa”
Na yi dariya mai sauti ina masa gwalo.
“Bachin yana min dadi, da na kwanta bana sanin me duniya take ciki sai na farka”
“Asha bachi lafiya Mom Unborn”
Ya fice ya bar ni na cigaba da shafa face cream din, sai da na gama sannan na dauki lemun juice din na sha kadan sai na ji zakin zumar yayi min yawa gashi ba son zuma nake sosai ba, haka na saka dole na tashi na shiga bathroom na kunna tap na tara lemun na kara ruwa kadan, na kashe juyowar da zan yi santsin tile ya kwashe ni, aiko ba shiri na saki kofin na rike tab din sai kofin ya fadi kasa lemun ya zube.
“Allah ya tsare na auna arziki yau kai...”
Na fada ina hakki, da na fadi gurin ba karamin ciwo zan ji ba, waya sani ma ko na karye tun da jikin babu karfi. Ruwa na saka na wanke lemun da ya zube na dauke kofin da ya tsaga na fito na aje shi a inda na saba ajewa na hau gadon na yi addu'a na kwanta, nan da nan kuwa bachi yace wa yake jira ba ni ba, kamar na mutu haka na fara bachin ban san shigowar Abdull dakin ba, kashe wuta da yayi ma duk ban sani ba. Daman bana sanin komai sai safe.
Ina tunanin shan lemun yana taimaka min sosai gurin samun bachi mai dadi kuma mai nauyi da tsayi, domin yau da ban shanye shi gaba daya ba na farka sai dai ban kai ga motsawa ba na ji saukar Abdull daga kan gadon ya nufi bathroom, yana shiga na ji kararar ruwa be jima ba ya fito ina kallonsa ya rufe kofar a hankali ba tare da ya kashe ruwan ba. Mamaki ya cika kwakwalwata ashe har yanzu be daina wannan abun ba, domin tun a wacan lokacin zuciyata take raya min yana biyawa kansa bukata ne a bandakin.
Ina ganin ya dauki wayarsa sai na rufe idona, na yi zaton bandakin zai koma sai gashi ya kunna fitilar wayar ya haska fuskata. Ni kuma na yi kamar bachin nake da gaske har sai da ya kauce sannan na bude ido. Ga mamaki na sai na ga ya nufi kofar fita ya bude a hankali ya fice. Zumut na tashi zaune kamar ledar da iska ya dauka. Na zauna gurin da tsawon minti biyar ban ji ya dawo ba, sai na sauko daga kan gadon na bude bandakin na kunna guluf na duba sannan na kashe na janyo kofar na rufe a yadda take.
Takawa na yi na fita dakin, a tunanin yana falo ne, sai dai kuma ban same shi a falon ba, domin wutar falon ma a kashe take ban ga hasken wayarsa ba kuma ban ga alamar mutum ba ta dan hasken waje da yake shigowa. Na nufi ma kunnun wutar kamar zan kunna sai kuma na fasa na nufi kitchen na leka nan ma baya nan. Na juyowa na nufo dakina da mamaki domin ko kadan zuciyata ba ta raya min abun da kunnuwa za su ji ba. Daf da zan shiga dakina ne na ji karar rufe kofar dakin Hana wata kila kuma na bandakinta ne yayi kara har na ji saboda dare ne, hakan ya saka hankalina ya karkata can, to daman idan baya falo baya kitchen baya dakina ina zai je? Waje? A tsakar daren nan ba zai fita waje ba sai idan da wani babban dalili.
Na taka cikin faduwar gaba na doshi kofar dakin, na kai hannu zan murda da nufin na bude na shiga sai kuma dauke hannuna na matsa kusa na dora kunne na a kofar dakin. Shiruuuu ban ji wani motsi ba, na sauke ajiyar zuciya ina jin kamar hankali ya kwanta, ashe dan'uwansa ne ke tafe da gumurzunsa irin tafiyar da ban yi tsammani ba.
“Sai yaushe za a zubar to?”
Na ji muryarta, hakan ya sakan ni kwantar da kunne a jikin kofar sosai na natsu numfashi ma daker nake fitarwa saboda na ji me take fada.
“Kina da matsala ne ke Wallahi, na fada miki ni ai na san lokacin da ya kamata a zubar ko?”
“Tsoro nake kar ya girma, kuma ina tsoron na sha wahala”
Ta fada cikin muryar kuka.
“Ai na sani idan ban ja lokaci haka ba, ba zan samu hadin kanki ba, yanzu ana zubarwa kuma ba zaki sake yarda da ni ba”
Rarararararsssssssaaaa. Gabana ya bugawar da mai sauraren tsawa dake tafe da ruwa.
“Zan yarda, ni dai dan Allah a zubar”
“Kin yi alkawari?”
“Eh, dan Allah a zubar”
“Ki kwantar da hankalinki mana, na san abun da zan yi, kin san ina sonki sosai ai, ina son ki Hana, amman ki yi ta wahalar da ni, Wallahi da ace ke na fara gani ba zan auri yayarki ba...”
Ban sake jin komai ba sai shesshekar kukanta kadan kadan. Tashin hankali ne be bari na sake jin komai ba ko kuma dai ba su sake cewa ba din. Na dauke kunne na shafa wuyana ina lalaben sarkar da babu ita a wuyana. Jikina ya fara rawa hawaye suka yi ambaliya a idona. Na shiga na same su a ciki na nuna musu na sa komai, ko dai wai ban ji daidai ba, ko dai gizo kunnuwa suke min. Na bar kofar na fara takawa na nufi dakina na shiga na hau gadona na kwanta na rufe ido na tsawon min biyu sannan na bude.
Wai ko zan ji cewar mafarki, amman ban ga alamar haka ba. Na mari kaina sai na ji zafin na tsara kunci na, tabbas gaske ne ba mafarki nake ba. Amman taya? Kanwata ce fa uwa daya uba daya, kanwata da mijina? Kanwata ta jini mai bina, kanwata da muka kwanta a mahaifa daya ciki daya uwa daya ta kawo mu duniya? Kuma mijina mijin da nake aure auren sunna! Mijin da nake dauke da cikin dansa ko diyarsa. Tun yaushe haka take faruwa?
Na mike tsaye na nufi madubi na sai kuma na zauna a kasa. Me na yi da na cancanci haka? Why me? Why? Kanwata? Jinina?
“Wayyo Allah na”
Na dafa zuciyata sai wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya ya zo min. Wannan abun yayi min muni ina ji a wasu gurare amman ban dauka abun zai zo kusa ni ba. Na tashi daker na koma saman gadon na kwanta jikina na rawa na takure guri daya na rumgume fillo, a wannan daren bachi be samu damar ziyarta idona ba, kunci be bar ni, kamin safe zazzabi ya rufe ni, filon da na rumgume kuma ya jike da hawaye na. Abdull be dawo dakin ba sai asuba, ina jin shigowarsa da lokacin da ya kwanta saman gadon ya lulluba...
Littafin nan ba kyauta ba ne. Biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to
Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.https://chat.whatsapp.com/Jd2OwsAcXE7EjI7NHeFQV0
Washe Gari na tashi da wuri saboda zan tafi asibiti, dan haka na gyara da wuri na fito falo, ina jin motsin Hana na nufi kitchen din na dan rikawa mata aiki.
Ina tsaka da kashe socket ta yi min wata magana da ta saka na kalleta.
“Noor ina son na tafi gida”
“Me yasa Baba ya sake magana ne?”
“Aa kawai dai ina son gida yanzu, na fi jindadin zama gida sama da nan”
Na juyo da kyau na fuskance.
“Hana wani abu na yi miki ba daidai ba ko Abdull yayi miki?”
“Aa ba ko daya, kawai dai na fi sha'awar tafiya gida ne”
Na dan jimm ina mamakin dalilinta na fadar haka a yanzu, daman na lura yanayinta gaba daya ya canja.
“Hana mafarki kika yi marar kyau ko me?”
“Ba komai ni dai kawai ina son na tafi gida”
“To kije ki dawo ko kuma ki koma gidan gaba daya?”
“Gaba daya dai nake son na koma”
“Karatunkin fa?”
“Zan hakura na san idan naje can Mama zata iya sakani idan Baba ya yarda”
Na matsa kusa da ita domin babu ta yadda lafiya zata saka ya yanke karatunta ta koma gida haka nan kawai sai da dalili.
“Hana na san muma yawan samun tsabani da ke a gida, amman nan gidan aurena ne, idan kina ganin akwai abun da nake miki da baya miki dadi zaki iya fada min sai na gyara, idan kuma aiki ne kike ganin na sakar miki ragamarsa zan rika yin rabi, amman dan Allah ki zauna ina jindadin zamanki ina son yar'uwa a kusa da ni, ba ni da kowa nan zamanki a gidan nan yana rage min kewa”
“Babu wani tsabani da zamu samu har ya saka na ji bana bukarki a kusa da ni, mu na samu tsabani a gida a nan ma zamu iya samu, saboda zama tare dole wata rana zaka ji an maka ba daidai ba, amman Noor ni ba zan iya cin amanarki ba”
Ta rumgume ni tana kuka, jikina yayi sanyi sosai kalaminta na karshe ya saka min shakku a zuciya.
“Akwai abun da yake faruwa tsakaninki da Abdull ne?”
Ta dago da sauri.
“Aa Wallahi Babu, dan Allah karki zarge shi ki lalata aurenki, Wallahi Wallahi na rantse miki da Allah babu wani abu tsakanina da Abdull”
Hankali ya dan kwanta da ta yi min rantsuwa cewar ba tsakaninta da Abdull ba ne.
“To ya kawo zancen cin amana Hana?”
Ta share hawayenta.
“Ina nufin kamar na guje ki saboda kin min wani laifi, ai kamar na ci amanarki ne a matsayinki na yar'uwata”
“To me yasa kike son tafiya gida? Kina karatunki a nan, Abdull ma idan ya ji ai zai yi fada, Mama ma sai ta miki fada tace kin san ba zaki karatu ba kika saka bata kudi aka biya miki har na shekara uku”
“Kawai ina yawan mafarkin marar kyau ne, kuma ana baki tsoro a gidan nan ina tunanin akwai aljannu a gidan”
“To ki rika addu'a mana Hana, ke da kike fada min yadda zan bi da rayuwa na jidadi yau kuma ke kika rasa ya zaki yi?”
Ta yi murmushi
“Gaba daya na rikice mugun mafarkin da na yi ya daga min hankali”
Zan sake yin magana Abdull ya kirani.
“Noor kin fasa zuwa awon ne? Karki makara fa”
Na dauki ruwan zafi na fice daga kitchen, sai da ta jera mana komai a dinning sannan ta zuba nata ta dauka.
“Lafiya na ga kamar yanayinta ya canja”
Abdull ya tambaya she dai shi ma ya lura da yadda take ta hade rai bata son kallon kowa.
“Lafiya kalau”
Ta wuce dakinta bayan ta amsa mishi, da kallo na bita sai da ta shige sannan na juyo na kalleshi, kamar na fada masa kudurinta sai kuma wata zuciyar ta hana ni, na san ba abu ne da zai masa dadi ba, saboda kudin makaranta da ya biya mata ga yawan hidima da yake mata, tafiya makaranta ma kullum sai ya bata kudin bus kuma ya rage mata hanya saboda akwai tazara daga unguwarmu zuwa makaranta kuma babu abun hawa sosai ta gurarenmu sai idan sun kawo Passenger.
“Ina jin bata da lafiya ne”
“Me yake damunta? Ko kuma dai mood swings ne”
“Yeah”
Ko da muka gama karyawa ta yi shirin makaranta da uniform dinta da suke sakawa kullum. Tare muka fita sai da ya fara sauketa sannan ya sauke ni a asibitin ya wuce gurin aikinsa.
Tun daga ranar Hana bata sake yi min maganar komawa gida ba, sai dai na lura da yanayinta gaba daya ya canja kamar zaman gidan ya daina mata dadi a yanzu, domin ko hirar da take zama muna yi tare da Abdull a da yanzu duk ta daina, ko da yake yanzu ba kamar da ba ne, da take gida kullum yanzu kuma idan ta tafi bata dawowa sai yamma idan ta dawo wani sa'in ta hau aikin gida ko da ta gama kuma sai bachi. Sai can ba a rasa ba muke zama muna hira a falo da zarar Abdull ya shigo zata masa sannu da zuwa ta shige dakinta ba zata sake fitowa sai gobe.
Ko wani abun ya siyo sai dai na kai mata nata dakinta, ko kuma shi ya kwankwasa kofar dakin ya aje mata daga bakin kofa, wani sa'in idan ina jin wahalar tashi. Wata kila ta fara haduwa da abokan banza masu hore mata kunne ne, ko kuma dai ta gaji da yin aikin gida ne, ko kuma nata gidan mijin take son tafiya ita ma.
Ko ma dai yaya ne na daure ma zuciyata na zauna da ita a haka, saboda bana son ta lakata karatunta a lokacin da take tsananin bukatarsa, kuma ana yi da kai ya fi ba'ayi, zamanta yana taimaka min ko yaya ne tun da ita take min komai a gidan kuma ina ganinta na san ina da yar'uwa a kusa ina jin sanyi a haka din ma.
KAREEM POV.
Da sauri ya maida idon ya rufe ya kai hannunsa dake sanye da drip ya murza idon sannan ya sake budewa. Hannun ya kai ya cire robar dake bakinsa yana kokarin daga hannunsa daya sai ya ji yayi masa nauyi dubawar da zai yi sai yayi arba kan dansa Areef a hannun. Yunkurawa yayi a haka ya tashi zaune ya saka dayan hannun a hankali ya cire hannunsa. Haka ya cire duk wani abu da aka laka masa sannan ya sauko da kafafuwansa yana tuna abun da ya faru.
Ya san dai yana tsaka da tuki hudu ya sauko masa daga lokacin kuma be sake sanin inda yake ba, maybe ya hadari yayi, ba ma wata kila idan be yi hadarin ba ai ba za a kawo shi nan a aje ba. But why ICU shi da be ji ciwo ko daya a jikinsa ba, domin be ga wani guri da ya ji ciwo bako ya bugu. Hannu ya mika ya janyo files dinsa ya bude ya duba. Daman ya sani zama unconscious or in a critical condition ke saka a aje mutum a gurin. Ya duba ya gani kwanansa biyu a dakin amman be sani ba sai yau da ya farka, babu wata rauni a jikinsa but hankalinsa da numfashi sun yi nisan da an dauka barin duniyar zai yi.
Ko me ua buga oho, ya san dai hakan baya rasa nasara da damuwar da yake ciki, kusan ita ce silar faruwa komai. Ya aje files din ya shafa kan dansa dake sanye da uniform din makaranta yana murmushi ko dan yaran nan yana bukatar rayuwa. Areef ya bude ido sakamakon shafa kansa da Dadynsa yayi.
“Hey young Man”
Yaron ya tashi zaune ya matsa ya rumgume mahaifinsa yana murna.
“Dady ka farka”
Kareem ya saka hannu ya shafa bayansa yana murmushi kamin wani azababben ciwo ya ratsa zuciyarsa har sai da ya ji ta motsa kamar ta bar muhallinta.
“Oh...”
Ya furta Areef ya dago ya kalleshi.
“Dady minene?”
Kareem ya murmushi.
“Ba komai ina Tine”
“Suna waje bari na kira ta har da Mama ma tana nan, kullum zai mun zo kana bachi, Hajiya tana nan ita da Uncle Aaryan nan yake kwana”
Har ya isa kofa sai kuma ya juyo ya kalleshi.
“Daddy ma kullum yana zuwa, yana yin addu'a yana tofa maka, Dady kuma Momy ta kwashe kayanta gaba daya ta koma gurin Hajiya an bata bangare daya tace tare zata zauna da mu”
Kareem ya daga mishi kai. Areef ya fita da gudunsa, Kareem kuma ya mike tsaye ya fito daga dakin da kafafuwa normal yake jin kansa kamar be yi hadari ba. Ya san yadda asibitin take fa kuma dokokinta sai ya canja ma kansa daki bayan ya gaisa da ma'aikatan dake ta masa sannu Doctor dake duty yana da tsokarsa yana fadin ya bari yayi aikinsa yanzu shi majinyaci ne ba likita ba
Files din dake dayan dakin likita ya dauko ya dawo da su sabon dakin da Kareem yake, sannan aka bawa visitors damar shiga, yan'uwa na ta shigowa suna masa sannu na nesa kuma suna kira a waya. Duk wani motsi nasa yana kan idon Yusura kallonsa take sosai kamar bata taba ganinsa ba, sau daya ta yi masa ya jiki bata sake ba sai dai duk dagowar da zai yi sai ya ga tana kallonsa. Tun daga ranar kuma bata sake zuwa ba duba shi har aka sallame shi after four day's da yayi a asibitin.
Ranar da zai bar asibitin babu yadda Hajiya bata yi ba akan ya dawo family house ya zauna har sai jikin ya kara warwarewa da kyau saboda a can gidan babu kowa a yanzu amman ya ki, domin baya son zama gidan zai fi sakewa a gida ko da kuwa ba shi da lafiyar balle baya jin ciwon komai a jikinsa. Taya zai saki matarsa ta tare a family house dinsu shi ma ya koma can ya tare kamar mace.
Ba karamin godiya yayi ma Allah ba lokacin da Aaryam ya kai shi gidan ya ga yadda gaban motarsa ya lalace, bayan ma ya bugu ba karamin accident yayi ba amman Allah ya kawo masa sauki tun da be ji rauni a ko'ina ba. Aaryam ya fada masa yadda hadarin ya afko sai da ya cika da tsananin mamaki.
“Babu wanda ya dauka zaka rayu fa, Wallahi duk mun tsorata, babba mota ka buga irin mai zube yashin tefa. Mai motar yace yana ta maka horn domin ya ga yadda ka zo da gudu amman baka