Showing 3001 words to 6000 words out of 75226 words

Chapter 2 - Exiled Princess Book 1 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

286

ka ci gaba da tafiya a tare


Sai da su ka karaso kofar wani gida dan nesa kadan da na Abba su ka tsaya a tare sannan Abba ya kale shi ya ce " Zayd za ka zo cin abincin da dadare dai ko na ga jiya ba ka zo ba "


Girgiza mishi kai kawai ba ta tare da ya ce komai ba

Dan murmushi Abba ya yi kafin ya ce " haba Zayd wai in ka na tare da ni din ma sai ka yi min kurmancin na ka "


Dan karamin murmushi geffen fuska ya yi kafin ya yi magana cikin wata zazzakar murya cike da nitsuwa ya ce " uncle ba na jin dadin maganar ne , so ku bar matsa min ina magana please " ya fada cikin wata kwarbabiyar haoussa kamar wanda ke koyo

( WAIT ! WAIT ! WAIT ! BAN GANE BA KENAN DAMA BA KURMA BA NE KO YA NE WANNAN ZANCEN YAKE 😳😳😳😳😳 )


Jinjina kan shi Abba ya yi kafin ya ce " ba komai, amma fa mu na jiran ka yau kar ka zauna ba ka zo ba " ya na gama fadar haka ya yi gaba ya ci gaba da tafiyar shi


Ya na fara tafiya shi ma Zayd ya juya ya nufi kofar gidan ya na sa hannu shi cikin aljihu

Sai da ya karaso kofar gidan ya tsaya ya ciro wasu keys da ga cikin aljihun shi ya bude kofar sannan ya shiga ya na medo kofar


Gida ne mai kyau dai'dai me hali amma fa ya fi na Abba Girma da kyau

A hankali ya ke takowa ya nufi terrace din gaban shi ya Haye
Nan ma ya sa key ya bude kofar shiga falon


Masha Allah duk da falon karami ne amma ya hadu , an saka mike wasu sofas red colour , buyi two seaters, daya three seater sai guda one seater , a tsakiyar su kuma wata yar karamar table ce ta glass sai wasu remote da ke saman ta

Da ka shigo bangaran dama ka na fuskantar wata yar karamar dining room mai dauke da dining table karama mai kujeru guda hudu
Sai wata yar drawer da ke karshen dining room din ta na dauke da kayan breakfast kamar su madara sugar coffee da sauren su

Bangaran hagu kuma wata door ce wadda za ta sada ka kitchen din

Bayan sofa mai three seater wani corridor ne mai dauke da wasu door guda biyu wanda ina kwaytata zaton bedroom ne



Bai tsaya bin ta falon ba ya wuce kai tsaye corridor din

Door ta karshe ya nufa ya kama handle din kofar ya murda ya shiga ciki ya rufo kofar

SAI MUN HADU GOBE 🀘 KAR KU MANTA KU NA TARE DA ALKALAMIN ANISH , WANNAN SO MA TABI NE




❀⚘ EXILED PRINCE ⚘❀
(LOVE MEETS POWER ) πŸ‘‘πŸ”₯


( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )



STORY & WRITTEN BY : ANISH


Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA πŸ’–πŸ’πŸŒΊ

https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i

β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘β™‘


PAGE 2 ❀πŸ”₯


After some minutes ya fito sanye da wandon three cuter black colour da t-shirt fara mara nauyi , babu takalmi a kafar shi , ya na sanye da bakaken glass kamar kullum


Takowa ya ke cike da izza da kwarjini , hannun shi na rike da wata dankareriar waya kirar Iphone 13 pro max mai launin Gold sai shining ta ke kamar zinaryar gaske


A hankali ya shigo falon ya nufi sofa three seaters ya Haye ya konta
Bayan ya konta ya daura hannun shi daya saman forehead din shi, dayan kuma ya fara latsa wayar shi

( KENAN BA MAKAHO BA NE DUK BASAJA CE YA KE πŸ₯ΊπŸ₯Ί TOH ME YA SA SHI YIN HAKAN πŸ€”πŸ€” )


Bai fi ten minutes ba da konciyar shi wani kyakyawan matashi ya shigo falon ya na sallama hannun shi rike da ledodin restaurant


Ko motsawa Zayd bai yi ba , ko sallamar shi cen kassan makoshi ya amsa mishi ita


Dan karamin murmushi saurayin ya yi kafin ya tako ya zauna saman sofa two seaters da ke geffen wadda Zayd ke konce sannan ya ajiye ledodin hannun shi saman table


" Al-Amir Nawfel ga abinci ka nan " ya fada ya na kallon shi ta wutsiyar ido

A dubu dari Zayd ya mike zaune ya matse fuska ya nuna saurayin da dan yatsa cikin turanci ya ce " kar na sake jin ka kira ni da wannan sunnan Diya idan ba haka ba "


Dariya sosai saurayin ya yi shi ma da turanci ya ce " In haka ne ni ma ka daina kira na da Diya , ni fa yanzu suna na Moussa " ya kai karshen ya na kashe mishi ido guda


Dan tsaki Zayd ya ja kafin ya ajiye wayar shi gefe ya matso bakin sofar , ya kai hannu ya janyo table din gaban shi sannan ya bude ledodin da Diya wato Moussa ya kawo mishi


Moussa kuma kallon shi ya ke ya na murmushi har sai da ya ga ya fara cin abincin sannan ya ce " Zayd wai ka na da labarin......... "

Bai karasa maganar shi ba Zayd ya daga mishi hannu akan ya isa haka


" Haba Amir yanzu haka za mu ci gaba da zama yanzu wajen shekara hudu kenan , ba ka kewar Al-Amira Tesnim da Malikat Al'Umu ka na tunanin halin da su ke ciki , ko kuma ka manta da Malik "


Shiru Zayd ya yi bai ce komai , ya ci gaba da cin abincin shi

Sai da ya ida sannan ya mike tsaye ya nufi dining room ya bude fridge ya dauki gorar ruwa guda ya dawo ya zauna inda ya tashi sannan ya bude ta ya fara sha


Jinjina kan shi Moussa ya yi cikin ranshi ya ce " Gaskia kam jinin sarauta ba wassa ba ne , ko da ba cikin masarautar ya ke ba "


" Amir wai yanzu haka za mu ci gaba da wannan zaman , mu fa jinin mayaka ne , zama ba na mu ba ne " Moussa ya fada cikin raunin murya


Sai da Ya ida shan ruwan shi sannan ya mike ya nufi corridor ya na fadin " ai ka san hanyar komawa ni ban tare ka ba "
Ya na gama fadar haka ya shige corridor ya shiga bedroom din da ya fito


Jinjina kan shi kawai moussa ya yi ya na murmushi ya ce " ni anya ba diyar malan din nan ya fara so ba , ka san dama an ce soyayya ke meda sarki bawa " ya kai karshen ya na bushewa da dariya


Sai da ya ida dariyar shi sannan ya mike ya dauki ledodin saman table ya kai kitchen sannan ya dawo ya nufi corridor ya shiga dayan bedroom da ke kussan wanda Zayd ya shiga


Misalin karfe 8 na dare


Gidan su Inaya


Zaune su ke cikin harabar gidan saman tabbarma su na sanye da hijab dark blue har kassa ,
Malan na gaban su zaune ya na karatun kur'ani , su kuma sun sunkuyar da kai su na sauraron shi
Mama kuma ta na zaune geffen shi ita ma ta na sanye da hijab amma fari


Su na a haka wani dan matashin saurayi ya fito da ga cikin dakin da ke fuskantar na su Inaya

Ya hadu ba laifi skin din shi chocolate kamar ta Inaya amma ta Inaya ta fi dan haske
Ya na da dogon hanci da kontancen saje , ya na da dara daren idanu brown colour , ya na da dan tsayi da mudewar jiki amma ba sosai ba a shekaru ba zai wuce 26 ba amma ya tare kassunba ga kwarjini
Sanye ya ke da wando three cuter Fari da shirt red kamar jini ya na rike da waya kirar Tecno pop 6 sai latsawa ya ke


Bai bi ta kan mutanan gidan da le zaune kussan kofar dakin shi ba ya sa kai ya fice da ga gidan

Malan na kallon shi ta kassan ido amma bai ce da shi komai ba , sai da ya ida karatun shi saman ya dago kai ya kali su Inaya ya ce " Auta, ina ga za mu tsaya a nan gobe sai mu ci gaba "


Jinjina mishi kai su ka yi a tare ba su ce komai ba , su ka mike su ka shiga dakin su dan su ajiye littafan su

Bayan mintina goma Inaya ta fara fitowa ta na sanye da doguwar riga irin ta barci da dan guntun kyale ta ya yafa a kan ta


Ta na fitowa ta ji ana sallama
Cak ta tsaya ta na kallon kofar gidan kafin ta amsa sallamar

Wani dan karamin murmushi ta saki ganin waye ke tare da yayan na ta
Da gudu ta je ta fada jikin yayan ta ta na fadin " yaya Abdoul kenan yaya Zayd ka je nemowa " ta fada ta na kallon Zayd ta geffen ido


Raba jikin ta ta yi da na Abdoul sannan ta ce " sannu da zuwa yaya Zayd "

Jinjina mata kai kawai ya yi bai ce komai ba

Duk abun da su ke Malan ya na kallon su amma bai ce komai ba sai ma murmushi da ya ke

" malan Zayd ku karaso mana " malam ya fada cikin zolaya

Yar dariya Inaya ta yi ta riko hannun Abdoul, shi kuma ya riko hannun Zayd su ka fara takawa a jere


Saman tabbarma sa malam ke zaune su ka karaso

Saki hannun ta Abdoul ya yi sannan ya ce ma Zayd su zauna

A tare suka zauna geffen Malam su ka sa Zayd a tsakiya

Ta na ganin sun zauna ta juya ta fara takawa ta nufi hanyar kitchen dan ta taimaka wa mama


Kamar an ce ya dago kai ya kali gaban shi
Ya na dagowa idanun shi ba su sauka ko ina ba sai saman hips din ta , gashi rigar da ta ke sanye yar shara shara ce a na ganin shape din ta


Sai da ya ji zuciyar shi ta buga a dubu dari ya sunkuyar da kan shi dan ya yi arba da abun da ya fi karfin shi


Malam sa Abdoul sarai su ka lura da shi, dan Abdoul har kumshe dariya ya ke

Dan murmushi Malam ya yi kafin ya matso cikin rada ya ce " Zayd in ka shirya ni ban da matsala ka zo ka dauki matar ka ta tare a dakin ka "


Dago kai ya yi ya kali malam ya na zaro idanu duk da su na cikin bakin glass

Yar dariya malam ya yi dan dama tsokanar shi ya ke son yi
Shi ma Abdoul yar dariya ya yi kafin ya daura hannun shi saman kafadar Zayd ya ce " Bro ka yi sauri fa dan kar ayi maka wufff da ita "


Dan tsaki Zayd ya ja ya na kauda kan shi gefe
Dai'dai lokacin da Inaya je fitowa da ga kitchen ta na rike da tray

Da sauri ya kauda kan shi dayan geffen cikin ranshi ya na fara danasanin abun da ya yi shekarun da su ka wuce


Gaban su ta zo ta ajiye tray din sannan ta mike ta juya ta koma dakin su

Ta na barin wajen Abdoul ya kai hannu ya janye tray din na sama , ya dauki spoon ya mika ma Zayd da malam sannan ya ce musu bismillah

A tare su ka fara cin abincin , har su ka Kamala ba wanda ya ce ma dan uwan shi wani abu

Sai da su ka ida mama ta zo ta gyara wajen ta kawo musu jug na ruwa da glass biyu , su ka sha sannan Zayd ya ce da Abdoul ya raka shi gida

Sai da ya tsokane shi sannan su ka tashi su ka bar gidan a tare

Ya na fita Inaya ta fito da ga dakin su
Ta na ganin malam zaune shi kadai

Da sauri ta karaso wajen shi ta ce " Abba yaya Zayd har ya tafi " ta kai karshen ta na kallon wajen kofar gidan

Dan murmushi yayi kafin ya mata nuni da gefen shi
Ba musu ta tako ta zauna geffen shi ta na sunkuyar da kai ta fara wassa da yatsun ta


Hannu shi ya daura saman kan ta kafin ya ce " Auta , fada min gaskia , ki na son Zayd "

A razane ta dago kai ta kaleshi ta na zaro idanu, ta ma rasa amsar da za ta bashi

Daga mata gera yayi kafin ya ce " ba ki ba ni amsa ba "

Da sauri ta ce " a'a Abba ba ni son shi " ta na gama fadar haka ta mike da sauri ta koma dakin su
Ya na kallon ta har ta shiga dakin su , sannan ya saki murmushi ya na girgiza kan shi


Bangaran Inaya kuma ta na shiga dakin su ta fada saman gadon su ta yi rub da ciki

Bugun ta a baya Nesrine ta yi kafin ta ce " ke dan Allah malama yi a hankali kar ki kare mana gado "

Dago kai Inaya ta yi ta zauna ta na kallon ta
Dan turo baki tayi cikin shagwaba ta ce " kin ga ko ku daina bugu na ko in fada ma Abba "

" ina ruwa na tashi muje na raka ki ma " ta fada ta na meda kallon ta saman book din hannun ta

Marairaice fuska Inaya ta yi kafin ta ce " Nesrine, wai Abba tambaya ta ya yi in ina son yaya Zayd " ta kai karshen kamar ta yi kuka


Dago kai Nesrine ta yi ta kale ta da kyau kafin ta bushe da dariya har da dafe ciki


Marairaice fuska Inaya ta yi kamar ta yi kuka ta ce " haba Nesrine ya zan yi miki magana ki yi zaune ki na yi min dariya "


Dan tsagaita dariyar ta Nesrine ta yi kafin ta ce " Yau ni tambayar Abba ce ta bani dariya , yo mi ne abun so cikin wannan abun , mutumin da ba ya magana , ba ya gani wa zai iya zama da shi ai ni ko sadaka a ke bani shi wlh ba ni so " ta kai karshen ta na sake bushewa da dariya


Hararrar Inaya ta yi kafin ta ce " kin ga matsala ta da ke wlh ba a iya magana da ke "

" yo ai wannan ba magana ba ce zancen gaskia wa zai iya son Zayd, ba dan kyawon shi ba ai ko kallo bai isa wani ba "

" wai ke me ya sa ki ke yawwan cin zarafin mutane, me ya yi miki, kullum sai kin kaskantar da shi , ko dan kin ga ba ya da kowa ba ya da idon gani , ba ya da bakin magana ko dan bashi da kudi , kin je makaranta ki yi karatun kur'ani ki san Allah ba ya son mai kaskantar na kassa da shi , yanzu in kin wayi gari kin koma kurma ko makafniya ki na tunanin wani zai so ki ne , wlh Nesrine ki ji tsoron duniya wannan jiji da kai da ki ka dauko ba na familyn mu ba ne , ba mu gado wannan ba gwara tun wuri ki tambayi kan ki ina ki ka dauko su "

" ke dan Allah malama ya isa dan kawai na tabo wani banza cen shi ne za ki yi zaune ki na min fada kamar wata uwa ta , ai ba karya na yi ba dan ko ke da kan ki da ki ke kare shi ba son shi ki ke ba dan haka ki bani lfy sakara kawai , kamata ya yi ki tafi massalaci ki dauki speaker ki ringa yi musu wa'azi ko ba komi kin samu lada no sens " ta kai karshen ta na saukowa da ga saman gadon ta fice da ga dakin


Ta kallo Inaya ta rakata har sai da ta fita sannan ta ce a fili " wlh karya ki ke, duk abun da zai sa mace ta so namiji yaya Zayd ya malake shi , dan ya ma fi sauran mazan wlh ko cikin dubu za ki duba da wuya ki samu kamar yaya Zayd " ta kai karshen hawaye na zubo mata

Da sauri ta koma ta yi rub da ciki ta fara kuka kassa kassa


Zayd


Tafiya su ke saman hanya shi da Abdoul, sai zuba ya ke mishi amma shi kuma ko kalma daya bai ce da shi ba

" Zayd wai mi ne sunan ka na gaskiya " Abdoul ya tambaye shi

Cak ya tsaya da tafya ya na kallon gaban shi kamar ya ga wani abu ya kassa gaba ya kassa baya


A hankali ya medo da kallon shi kan Abdoul ya zuba mishi ido mai ce komai

Ganin ya yi shiru kuma ya tsaya ya na kallon shi ya sa Abdoul cewa " ko sunnan na ka ma ka manta "

Jinjina mishi kai Zayd kafin ya fara takawa ya yi gaba

Dan murmushi Abdoul ya yi kafin ya ce " to tun da ka san hanya ni zan koma gida " ya fada ya na daga mishi murya

Bai ce mishi komai ya ci gaba da tafiyar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login