Showing 9001 words to 12000 words out of 75226 words
ta na murmushi
Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " malam Zayd tunanin mi ka ke haka "
Girgiza mishi kai kawai Zayd ya yi allamun ba komai sannan ya dawo da kallon shi kan Moussa ya mishi allamun su tafi
Jinjina mishi kai ya yi sannan ya kali malam ya ce " malam za mu wuce sai mun dawo "
Dan murmushi malam ya yi ya ce " shikenan Allah kiyaye hanya , Auta baza ki raka su ba " ya fada ya na medo da kallon shi kan Inaya da ke konce a jikin shi kamar baby
Cikin shagwaba ta ce " Abba yanzu fa su ka rako ni , sannan kuma na sake rakiyar su , ni gaskia babu inda zan je "
Malam na shirin magana ya ga Zayd ya kama hannun Moussa ya ja shi su ka bar wurin
Ta na kallon su ta kassan ido har su ka bar wajen sannan ta mike da ga jikin malam ta ce " Abba , yaya Zayd sunnan shi ne hakan na gaskia ko "
Jinjina mata kai malam ya yi ya na son ya ji abun da za ta cewa
" to amma Abba me ya sa yaya Moussa ke kiran shi da Amir , Amir ai ya nufin yarima " ta fada ta na kallon malam
Shi kuma malam juya kan shi ya yi ya kali su Zayd da su ka yi nisa cikin tafiyar su
Ba tare da ya juyo ba ya ce " ni ma ban sani ba, halan sunnan da ya ke kiran shi ne da shi lokacin su na kanana kin San ba dole sai dan sarki ba a ke kira da Amir "
Cikin ranshi kuma ya na tambayar kanshi shin wanene assalin Zayd din da su ka sani
( TOOOO ! MU MA DAI MU NA SON MIJI WAYE AINAHIN ZAYD DIN NAN 🙄 )
Haka ta zauna wajen malam ta na ta zuba mishi shagwaba shi kuma ya na biye mata sai da su ka ga magriba ta gaba to sannan su ka tashi su ka koma gida a tare , ta na rike da hannun shi ta na wassa da shi
( Ita dai wannan yarinyar da wuya ta zauna ba ta motsi 😑😑 )
Bayan sun koma gida , da kanta ta debo ma malam ruwa cikin buta ya yi Alwalla sannan ya tafi mosque
Bayan ya fita ita ma debo ruwa ta yi Alwalla ta koma bedroom din su dan ta yi sallat
Ta na shiga dakin ta tarda Nesrine ta na zaune saman dadduma ta daga hannayan ta sama ta na adu'a
Dauko daddumar ta Inaya ta yi ta zo ta shinfida geffen Nesrine sannan ta tada sallar ta
Ba su tashi da ga kan daddumar sai da su ka hada da sallar isha su ka yi a tare
Bayan sun ida Nesrine ta mike ta nade daddumar ta ta mayar da ita wajen ta sannan ta fito da ga dakin
Ta na fitowa ta ji sallamar Abdoul
Dum ta ji gaban ta ya buga dan ta san da wuya ya kyale ta bai mata fada ba
Kamar ko ta sani da sauri ta juya za ta koma dakin su ya kira sunan ta
Wasu yawu ta hadiye a hankali ta juyo ta ce " na'am "
Takowa ya yi ya zo gaban ta ya tsaya sannan ya ce " su waye samarin nan da na gan ku a tare "
Sunkuyar da kai ta yi , Cikin in'ina ta ce " ni ma ban san su ba kawai sun tseda mu ne saman hanya wai mu je su rage mana hanya "
Jinjina kan shi ya yi sannan ya ce " shikenan nan gaba kar ku sake tsaya wa ko sun muku magana ku kyale su "
" to yaya Abdoul " ta fada ba tare da ta dago kai ba dan tsoron ta ke ji ya wanke ta da mari
Shi kuma tsaya wa ya yi ya kare mata kallo da kyau ya ga yadda ta ke ta rawar jiki kamar ya ce zai dake ta
Sai da ya dan jima a haka sannan ya juya ba tare da ya ce komai ba ya shiga bedroom din shi
Ita kuma ta na jin ya fara takawa ta dago kai ta ga ya nufi dakin shi ta sauke ajiyar zuciya har da dafe saitin zuciyar ta ta na jan nunfashi a hankali
Sai da ta nitsu da kyau sannan ta kama hanyar kitchen
❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
STORY & WRITTEN BY : ANISH
Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
PAGE 4 ❤🔥
Da sallama a bakin ta shigo kitchen din, nan ta isko mama gaban murhu, har ta gaba girki
Dan juyo wa mama ta yi ta kali Nesrine sannan ta ce " lafya idanun duk sun kumbura haka ? "
Ta na shirin magana ta tsinci muryar Inaya ta na fadin " kuka ta yi shi ya sa "
A tare duk su ka jiyo su ka kale ta
Ta na tsaye bakin kofar kitchen din ta na sanye da doguwar riga mara nauyi ta saka dan karamin hijab zuwa kirji
Hararrar ta Nesrine ta yi kafin ta ce " tooo malama miye ruwan ki a ciki ? "
Hannayan ta duka biyu Inaya ta sa ta rike kugun ta, ta ce " da ruwana , sai dai ki yi abun da za ki yi " ta kai karshen ta na murguna mata baki
Da sauri Nesrine ta dauki wani plate ta juya za ta bugawa Inaya
Da gudu Inaya ta juya ta bar kitchen din ta na kara
Ita ma Nesrine bayan ta ta biyan ta ta na fadin " yau sai na yi maganin ki "
Inaya kuma ido a rufe ta yi da gudu za ta bar gidan
Har ta kai bakin kofa ba ta sani ba, kawai sai ji ta yi ta bugi wani abu da karfi ta yi baya za ta fadi ta na sakin kara mai karfi, wanda ya sanya shi toshe kunnuwan shi da duka hannayan shi biyu
Cak Nesrine ta tsaya ta na kallon su ta na zaro idanu
Malam ne da Zayd su ka shigo gidan sai da su ka yi sallama amma Inaya ba ta ji su ba , har sai da ta bugi kirjin Zayd da karfi
Shi kuma ya kassa taro ta dan ya na tsoron ya taro ta wani ya lura da hakan ya yi mishi wata magana da za ta bata mishi rai shi ya sa ya kyale ta ta fadi
Inaya kuma ta na faduwa kan ta ya bugu dum ga kassa har sai kassar ta dan girgiza
Da gudu Nesrine ta saki plate din hannun ta ta nufo ta da gudu ta na fadin " Inaya, Inaya , Inaya " kamar ta yi kuka
Shi ma malam da ke tsaye geffen Zayd da gudu ya yi kan ta ya talabo ta ya na kiran sunan ta
Ina ita ko jin su ba ta yi sai kuka ta ke kamar karamar yarinya
Ganin yadda su ka bi su ka rude ya sa shi kauda kan shi gefe ya saki dan siririn tsaki
A hankali ya fara takowa inda ta ke konce ta na kuka
Dukowa ya yi gaban ta, ya sanya hannayan shi duka biyu ya dauke ta cak kamar baby ya mike tsaye sannan ya nufi tabbarma da ya gani a shinfide kussan dakin Abdoul
Da sauri malam ya bi bien shi , ita kuma Nesrine ta tsaya ta na kare mishi kallo cikin ran ta, ta na tunanin ya akayi ya san tabbarma ta na cen wajen
Malam kuwa bai kawo komai a ran shi ba dan ya san akwaye makafi dayawa da su ke aiki kamar ma su idanu ba mamaki ya hadace inda su ke zama kullum shi ya sa ya nufi wajen kai tsaye
( HAKAN NA NUFIN MALAM YA SAN ZAYD BA KURMA BA NE AMMA BAI SAN SHI BA MAKAHO BA NE 🤔 )
Sai da ya karaso wajen tabbarma sannan ya kontar da ita a wajen ya koma gefe ya zauna , ita kuma har yanzu kuka ta ke kamar baby ba ta ma san an dauke ta ba
Ya na kontar da ita malam ya karaso wajen ya zauna geffen ta ya talabo kan ta ya zaunar da ita ya rungume ta ya na fadin " ya isa haka auta daina na kukan nan haka kar ki janyo wa kan ki ciwo "
A hankali ta fara rage sautin kukan ta ta na hadiyar zuciya
Ta na a haka ta ji an tabo mata kafar ta
Ta na konce a jikin malam din ta dago kan ta ta kale shi
Ya na ganin ta dago kan ta ya kai hannayan shi biyu ya rike kunnuwan shi ya dan sunkuyar da kai allamun ya na bata hakuri
Wata yar karamar dariya ta yi cikin kukan nata sai da dan dimple din ta na geffen dama ya banyana karan farko kenan da na gan shi kuma gashi ba karamin kyau ya na kara mata ba
A hankali ya dago kan shi ya na kallon ta ta cikin glass din shi, abun har dariya ya so ya bashi yadda ta ke dariya ta na kuka lokaci guda
" Shikenan auta ya wuce ko ? " malam ya fada ya na kai hannun shi ya goge mata hawayen ta
Jinjina mishi kai ta kafin ta kai hannun ta bayan kanta ta ce " Abba wajen zafi ya ke min " ta kai karshen cikin shagwaba
Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " babu komai auta na zai wuce tashi ki je daki, ki konta "
Da to ta amsa mishi sannan ta fara kokarin mike wa da ga jikin shi
Da sauri Nesrine da ke tsaye waje guda tun dazu ta na kallon su , ta karaso wajen ta kamosu hannun ta guda ta taimaka mata ta mike tsaye su ka nufi cikin daki
Su na shiga cikin dakin Inaya ta Haye saman gadon ta yi rub da ciki ta na sauke nunfashi a hankali ta lumshe idanun ta
Ita kuma Nesrine ta juya ta baro dakin ta tafi kitchen
Ta na shiga malam ya kali Zayd ya ce " Zayd me ya sa ba ka taro ta ba, yanzu da ta ji ciwo fa, dama ta na da tabo a kan ta na dauke shi ne ya motsa yadda na ga ta na kukan nan "
Kallon shi Zayd ya yi cikin sanyi murya ya ce " sorry uncle , amma wane tabo ne wannan ? " ya tambaya ya na son ya ji karin bayani
Ya na shirin magana Abdoul ya fito da ga dakin shi ya na sanye da jallabiya brown mai dogayen hannu ya zo geffen su ya zauna ya na musu sallama
A tare su ka amsa sallamar amma ta Abba kadai a ka ji , dan Zayd in ba kallon bakin shi ka yi ba baza ka gane ya amsa ba
Sai da ya zauna sannan ya ce "malam, na ji wani ya yi kara, cikin gidan nan ne ? "
Dan murmushi malam ya yi kafin ya ce " ba komai, auta ce ta dan fadi amma ba ta ji ciwo ba "
Jinjina kan shi kawai Abdoul ya yi ba tare da ya ce komai
Su na a haka Nesrine ta fito da ga kitchen ta na rike da plate ta shiga dakin su
Ta na shiga mama ta fito da ga kitchen din ta na rike da tray madaidaici ta karaso wajen su malam ta yi musu sallama ta ajiye tray din gaban su , sannan ta koma kitchen ta dauko musu jug na ruwa da glass biyu ta ka ta ajiye musu sannan ta wuce dakin ta
Ta na shiga dakin Abdoul ya bude musu tray din ya mika ma kowane spoon guda sannan ya ce musu bismillah
Kamar yadda su ka saba haka wannan karan ma haka su ka ci
Sai da su ka Kamala ba wanda ya ce ma wani ufan
Ya na tsaka da shan ruwa Inaya ta fito da ga dakin su ta na dafe kai da hannu guda ta na dan lumshe idanu kamar mai jin barci
A tare duka su ka dago kai su na kallon ta ba wanda ya ce da ita komai
Ta na tsaka da tafiyar ta ta ji wani jiri ya debe ta yi fuuuuu baya ta tafi za ta fadi
Da sauri Abdoul ya yi kokarin tashi dan ya taro ta amma sai dai mi ?
Tun kafin ya mike ya ga Zayd ya mike a dubu dari ya nufe ta , taku biyu kawai ya yi ya riko hannun ta ya janyo ta, ta fado saman fafadar kirjin shi
Baki sake Abdoul da malam ke kallon shi sannan su juyo su kali juna su na son su yi magana amma baki ya ki buduwa
Basu Ankara ba sai kawai ganin su ka ya dauke ta cak ya komo inda ya tashi ya kontar da ita, sannan ya kai hannu ya dauki glass din ruwa ya zuba kadan ya yarfa mata a fuska
A hankali ta ware idanun ta ta na karanto kalmar shahada
Ajiyar zuciya malam ya sauke ya na lumshe idanun shi a hankali sannan ya bude ya kali Abdoul ya ce " Abdoul meda ta dakin su "
Da to ya amsa mishi sannan ya mike tsaye ya kai hannu ya dauke ta cak kamar baby ya nufi bedroom din su da ita
Ya na barin wajen malam ya kali Zayd ya ce " Zayd na san kai ba kurma ba ne amma yau abun da na gani makaho bazai iya yin haka "
Shiru Zayd ya yi ya na sauraron shi amma ya kassa bude baki ya yi magana
Dafa kafadar shi malam ya yi kafin ya ce " Zayd ni fa na yarda da kai, dalilin da ya sa na aura maka Inaya nassan ka na da kyakyawar zuciya amma ban San assalin ka ba kuma bazan ce ka fada min har sai randa ka yi ninya amma zan so in sani meyassa ka ke karyar wadanan nakassa al'halin ka na cikin koshin lafya ? "
Malam na gama fadar haka Abdoul ya fito da ga cikin dakin su Inaya ya dawo inda ya tashi ya zauna
Ya na zama Zayd ya ce " Ni ban taba ce muku ni kurma ne ko kuma makaho ku ne ku ka yi hassashen ku a haka "
Dan zaro idanu malam ya yi dan fa maganar Zayd ba karya ba ce dan tun lokacin da su ka shigo garin kano su ka hadu da Zayd kullum shiru da shi ko an mishi magana sai dai ya girgiza kai ko ya jingina da haka har su ka yi tunanin ko shi kurma ne , gashi kullum ya na sanye da bakin glass wani lokaci ya na rike da sanda kamar makaho dalilin da ya sa su ke tunanin shi kurma ne kuma makaho
Kallon shi da kyau Abdoul ya yi kafin ya ce " Zayd ka na nufin yanzu ka na iya gani na "
Sai da ya dauki lokaci kafin ya ce " of cours ina iya ganin ka, ka na sanye da jallabiya brown mai dogayen hannu , ni fa ba ni son yawwan magana dan Allah ku daina saka ni dole sai na bude baki na yi magana zan iya fadar abun da zai bata muku baki daya " ya fada kai a sunkuye
Jinjina kan shi Abdoul ya yi kafin ya ce " don Allah Zayd zan so na ga idanun ka ko da so guda ne ka ga yanzu four years kullum ina ganin ka da glass wannan karan na so na gan su "
Dago kan shi ya yi a hankali ya na kallon Abdoul ta cikin glass din shi kafin ya sa hannu a hankali ya zame glass din shi
A tare zuciyar malam da Abdoul su ka buga da su ka ci karo da wadanan hazel eyes na Zayd ga shi ko ya na fuskantar lamps din wajen sai idanun shi su ka yi reflecting hasken lamps din sai su ka yi wani kyali na musaman su ka zama kamar idanun mage
Da sauri Abdoul ya ce " don Allah meda glass din ka wlh sai da na ji tsoro "
A hankali ya sunkuyar da kai ya Meda glass din shi sannan ya dago kai ya kali Abdoul ya ce " yanzu dai baza ka ce ba ka taba ganin idanu na ba "
" ni ko na gan so , ai wadanan ko a mafarki na gan su sai na gane su " ya kai karshen ya na yar karamar dariya
Malam dai ya yi sumar zaune ya rasa wane irin mutun ne Zayd , sam bai yi kama da mutanan Nigeria ba karewar zancen bai ma yi kama da mutanan Africa ba ki daya
Haka su ka ci gaba da hirar su wadda yawancin Abdoul da malam ke yin ta shi Zayd ya na zaune kamar gunki
Sai wajen karfe 10 na dare sannan ya mike zai koma gida, Abdoul ya dan raka shi