Showing 18001 words to 21000 words out of 75226 words

Chapter 7 - Exiled Princess Book 1 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

289

table ta na karatun ta cikin konciyar hankali

Ta na a haka wasu yan mata guda biyu su ka zo table din ta su na mata sallama

Ko dago kai ba ta yi ba ta kale su amma ta amsa musu sallamar su cen kassan makoshi

Dayar na mini skert da yar t-shirt colour din uniform din college din babu hijab a jikin ta sai wani dan karamin veil da ta nada a kan ta , ta yi simple make up

Dayar kuma ta na sanye da uniform din ta kamar na Nesrine wato wando da riga zuwa guyiwa da hijab zuwa kirji , ta na rike da hand bag guda biyu

Wadda ke sanye da mini skert din ta ja chair din da ke fuskantar ta Nesrine ta zauna sannan ta kai hannu ta karbe book din hannun ta ta na fadin " me ki ke karantawa ne haka ? "

Hararrar ta Nesrine ta yi kafin ta mike tsaye ta tatare kayan ta sannan ta mika wa yarinyar hannu ta ce " ban Boko di na dan Allah zan koma class "

Mikewa tsaye yarinyar ta yi ta ce " haba Nesi me ya yi zafi haka "

" kin ga Ramatou ki ban book di na, sannan kuma sunana Nesrine ba Nesi ba "

Dayar yarinyar da ke tsaye ta ce " tooo ! Me ya yi zafi haka ? "

Cikin fushi Nesrine ta kale ta ta ce " kin ga Halima ban sanyo da ke ba "

Dariya yarinyar da ta kira da RAMATOU ta yi kafin ta ce " yanzu wannan fushin Nesi duk dan Hafiz ya miki fada ne jiya ? "

Dawo da kallon ta kan RAMATOU ta yi sannan ta ce " kin ga ko wlh tun wuri ki ce mishi ya fita da ga harka ta , ba ni son shi , in kuma ya matsa na sa yaya na ya yi mishi dan banzan duka "

Dariya RAMATOU ta yi har da dafe ciki sannan ta ce " to sai mi in kin fada mishi me zai yi , wlh ko karar shi ya kai gaban yan sanda ba abun da za ayi mishi dan haka tun wuri gwara ki karbi soyayyar shi, ni ban ma ga abun so cikin dirty girl irin ki ba , ni ko abotar da mu ke kawai dan ki na temakamin ne ina samun good grades ba dan haka ba ko kallo ba ki ishe ni ba , ke ba ki san yan mata nawa ne ke biyar yaya na ba da sunnan soyayya amma ya ki dan ya ce ya na son ki shi ne za ki wani ja mishi aji, yar rainin sens kawai, sannan ki ji yaya Moctar ya ga kanwar ki kuma ya ce ya na son ta , na fada mishi gaskiyar sunnan ta da kuma karyar da kika yi mishi na cewa hanya ce kawai ta hada ku wlh idan ki ka matsawa Inaya ta ce ba ta son shi " ta kai karshen ta na kyasta mata dan yatsun ta saitin fuskar ta

Cike da izza ta ce " to wlh ki kuka da kan ki "

Ta na gama fadar haka ta tila mata book din ta a fuska sannan ta juya ta bar cafeteria din Halima na biye da bayan ta


Su na barin wajen Nesrine ta koma ta zauna ta daura kan ta saman table din sannan ta saki kuka kassa kassa

Sai da a ka koma cikin class sannan ta tashi ta fara shiga toilet ta wanke face din ta sannan ta wuce class


Nassan kowa ya na son ya ji wanene Hafiz , to nima ina son ji 😂✌

Hafiz dai babban d'a ne ga governor din Kano, Moctar na bi mishi sannan Ramatou sai autar su Nabila , a shekaru zai kai 25 , Moctar kuma 21 , Ramatou 19 years sai Nabila da baza ta wuce 15 years ba
Tun bayan mahaifin shi ya zama governor wata izza da jiji da kai su ka saukar mishi
Duk abun da ya gani ya ce ya na so to sai ya same shi ko da ta karfi ce
Ga shi ba ya da mutunci ko kadan mahaifin nashi ma in ya bata mishi rai sai ya bishi kaca'kaca dan ba raga mishi ya ke ba
Tun haifuwar Nabila mahaifiyar su ta rasu , mahaifin na su ya sake aure har wajen sau uku
Amma duk wadda ya auro ba ta one month ta ke barin gidan sakamakon Dukan tsiyar da Hafiz ke yi musu
Mahaifin shi na sane amma ya ki yi mishi magana dan ya san ba karamin aikin Hafiz ne ba shi ma ya rufe shi da duka
Shi ya sa ya ja bakin shi ya yi shirin ya zuba mishi ido dan ya fi karfin shi
Duk wata badakala sa ya ke yi mahaifin shi na sane , sannu sannu har ya fara janyo Moctar cikin badakalar ta shi
Kullum su ne tafiya nightclub, ga shan giya da kayan maye
À takaice ba abun da ba su sha, sai dai ba su taba kusantar mace ba da sunnan Zina
Karewar zancen Nesrine da Inaya su ne mata na farko da su ka gani su ka ji su na son ta
Yadda a ka yi Hafiz ya hadu da Nesrine
Wata rana ce driver din Ramatou bai zo daukar ta ba sai ta kira Moctar a kan ya zo ya dauke ta
A lokacin su na tare da Hafiz
Da su ka iso school din , su na tsaye bakin gate ita da Nesrine
Tun da Hafiz ya daura ido saman ta ya ji ya na son ta
Sai bayan sun koma gida ne ya ke tambayar RAMATOU wacece wanan yarinyar da su ke tare
Nan ta fada mishi wacece Nesrine sai dai ba ta fada mishi ba ta na da kanwa
Goben shi tun karfe 7 ya je bakin gate fin school din ya jiran ta
Amma wani ikon Allah ranar nan Nesrine ba ta zo school ba
Sai da ya gama tsayuwar shi ya gaji sannan ya koma gida ,
Goben shi ma haka ya dawo school din
Wannan karan ta zo amma ta na baya dan Inaya ta riga ta fitowa shi ya sa a bai gane Inaya kanwar ta ba ce
Babu ko sallama ya kira ta cike da girman kai
Kallo guda ta yi mishi ta gane yayan Ramatou ne dalilin da ya sa ta fara sakin mishi fuska
Sannu sannu ta fara ganin halayan shi na gaskiya
Kullum sai ya zo college din su dan ya gan ta
Wata rana har waya mai tsada ya kama ta amma ta ki karba
Haka kuma ba karamin bata mishi rai ya yi ba har ya tsinka mata mari cikin fushi sannan ya bata wayar da karfi ya ce zai kire ta
Inda ya ajiye wayar nan ta bar ta ta yi tafiyar ta ko wa ya dauke ta oho !
Washe gari bayan ta zo school ya isko ta ya ke tambayar ta ina wayar da ya bata
Nan ta mishi karyar wai Mamar ta ta gan ta kuma ta amshe ta
Bai yi mata magana ba kawai ya bar school din , sai da ya yi wajen sati bai zo ba
Nan Ramatou ta zo ta hura mata kunne a kan Hafiz tsakani da Allah ya ke son ta ta daure ta ringa kula shi ko ya ji dadi
Abotar da ke tsakanin su ya sa ta yarda da zancen ta, dan ko ba komi yayan ta ne bai kamata ta wulakan tashi haka ba
Sannu sannu ta fara kula shi har ta fada soyayyar shi
Amma shi kuma ya na nan kamar dai kullum, bai sauya ba sam dan wani lokaci in ta bata mishi har marin ta ya ke wai a haka wai ya na son ta ( ni dai na ce humm)
Babu irin gift din da bai kama ta ba amma ko wane lokaci sai dai ta yarda shi tsakar hanya ko kuma ta bar shi nan inda ya bata shi
Sannu har soyayyar da ke mishi har ta fita zuciyar ta dan a ganin ta, Hafiz ba al'heri ba ne a rayuwar ta shi ya sa yanzu ta daina kula shi, shi kuma hakan ba karamin zafi ya ke mishi ba

TO KUN DAI JI WANENE HAFIZ DA KUMA ABUN DA KE TSAKANIN SHI DA NESRINE ✌


❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥


( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )



STORY & WRITTEN BY : ANISH


Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺

https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i

♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡


PAGE 8 ❤🔥


Zayd

Zaune ya ke cikin motar su wajen mai zaman banza ya na rike da wayar shi ya na latsa wa ya na sanye da tracksuit sky blue colour ya na sanye da wadanan bakin glglass din nashi na gado

Yayin sa Moussa shi kuma ke tukin, ya na sanye da Jeans baki da t-shirt Red colour

Su na a haka Moussa ya katse shirun na su da cewa " wai Amir ka fada ma babyn ka za ka yi tafiya ne ? " ya kai karshen ya na dan satar kallon shi

Shiru bai amsa mishi ba ko dago kai bai yi ba ya ci gaba da aikin shi

Dan murmushi geffen fuska Moussa ya yi sannan ya ce " Amir wai me ya sa ba ka kula yarinyar nan "

Ba tare da ya dago kai ba ya ce " meye ruwan ka a ciki ? "

" babu kawai gani na yi bai dace abun da ka ke mata ba, ka ga fa kallon makaho da kurma ta ke maka ba ta san kai ainahin wanene ba, ba ta san kowa na ka ba, ko cikeken sunnan ka ba ta sani amma a haka ta ke son ka "

A dubu dari Zayd ya dago kai ya kali Moussa ya ce " me ka ke son cewa ? "

Yar karamar dariya Moussa ya yi kafin ya ce " lalle ma ka cika dan rainin sens, yanzu ka na son ka ce min duk soyayyar da ta ke maka ba ka ganin komai, lalle ma yau ka cika babban makaho " ya kai karshen ya na sake bushewa da dariya

" wait ! Maganar me ka ke yi haka, wannan baby har ya san minene soyayya ? na ga ai gaban ka ta ce dakwai wanda ta ke so " ya kai karshen ya na medo da kallon shi kan wayar hannun shi ya ci gaba da aikin shi

" humm wai kenan ba ka gane ba da sunnan ka ne ta so fada ba, dan ka na wajen ne ya sa ta yi shiru , kai a ganin ka duk abun nan da ta ke ma da sunnan makobtaka ne kawai, no Amir ! Wlh pure love ne ta ke yi maka, kallo guda za ka yi mata ka gane soyayyar ka a idanun ta, nassan wadanan bakin glass din ya hana ka gani, Amir kai ka ce min ka na son ka manta rayuwar ka ta baya , to wannan damar ka ce , ka karbi matar ka , and found your family "


Shiru Zayd ya yi bai ce da shi komai ba amma cikin ranshi ya na tunanin kalmomin Zayd tabass wanda ke maka kallon makaho da kurma , kuma a hakan mutumin ya so ka ya tabbata soyayyar gaskia ya ke maka

" no ! Gaskia she is to small for me , wannan ko dauko ta ba na tunanin za ta iya bare har a yi tunanin wata familyn, gaskia ban yarda da abun da Diya ke fada ba " ya fada cikin zuciyar shi

Cen kuma wata zuciyar ta ce mishi " in ta tabbata yanzu kai ma ka na son ta ? "

Da sauri ya girgiza kan shi ya ce " no ! Impossible i can't do that "

Kallon shi Moussa ya yi kafin ya ce " what you can not do ? "

Dago kai ya yi ya kali Moussa sannan ya ce " nothing ! " sannan ya meda bayan ya jingina a bayan kujerar shi ya lumshe idanun shi

Daga kafadun shi Moussa ya yi irin ban damu ba cikin ranshi ya ce " in ta yi tsami ma ji "

Haka su ka ci gaba da tafiyar su ba wanda ya ce ma wani ufan har su ka isa inda za su je


Inaya

Konce ta ke saman bed din su ta na kallon ceiling ta daura hannu daya saman ciki dayan kuma saman gashin ta, ko tunanin mi ta ke oho !

Ta na a haka malam ya shigo dakin ya na sallama

Ba tare da ta motsa ba ta amsa mishi sallamar mishi

Bakin ya karaso ya zauna sannan ya kai shi ya daura saman nata ke saman cikin ta ya ce " auta, wai me ya ke damun ki ne tun shekaran jiya na lura yanayin duk ya sauya ko waje na da ki ke zuwa kin daina ko laifi na yi miki ? "

A hankali ta janye hannun ta , sannan ta juya ta bashi baya sai ta ce " Abba me ya za ku min aure ba tare da na sani ba, nassan ku na ikon yin hakan amma Abba ni ba ni son wanda a ka aura min , gaskia Abba a raba auren nan "

" dalilin da ya sa wacen ranar na tambaye ki in kina son shi , amma ba ki ba ni amsa ba ki ka tashi ki ka tafiyar ki "

" ni Abba ba ku tambaye ni in ina son shi ba , "

" to shikenan yanzu bara na sake tambayar ki , ki na son Zayd ? "

Da sauri ta ce " ina son shi , duk da ban san meye so ba amma har cikin raina na ke jin shi , amma gashi yanzu kun rabu har abada Abba ya zan yi na cire son shi a cikin raina " ta kai karshen kamar ta yi kuka

Dan murmushi yayi kafin ya ce " to ai ba sai kin cire son shi ba a ran ki ba "

" Abba ya zan je gidan wani ina son wani kuma, ni gaskia Abba ba ni son wanda a ka aura min , ko da ba za ku yarda na auri yaya Zayd dan Allah Abba kar ku aura min wanda ba ni so "

" na ga yanzu ki ka ce ki na son ya kuma za ki juya zancen "

Kuka ta saki ta fara harba kafafun ta kamar karamar yarinya ta ce " ni Abba ba shi ba na ce na ke so "

Yar dariya ya yi dan da gangan ya ke jan mata rai

Sai da ya ida dariyar shi sannan ya ce " to shikenan wanene ki ka ce ki na so ? "

" yaya Zayd " ta fada cikin kukan nata

Hannun shi ya kai saman kafadar ta sannan ya ce " yo ai ni ma shi ni ke cewa, shi ne wanda na aura miki , amma tunda ba ki so zan kira shi in ce ba ki son auren " ya kai karshen ya na janye hannun shi da ga saman kafadar ta ya mike ya zai bar dakin

Har ya kai bakin kofar ya jiyo Muryar ta ta na fadin " sa gaske Abba yaya Zayd ku ka aura min ? "

A hankali ya juyo ya na kallon ta
Ta na zaune tsakiyar gadon ta na kallon shi idanun cike da hawaye

Jinjina mata kai ya yi sannan ya sa kai ya fice dakin

Wani irin sanyi ne ta ji cikin zuciyar ta lokaci guda ba ta san lokacin da wani kyakyawan murmushi ya kubce mata ba har da wata yar karamar dariya
Ta dauko pillow ta boye fuskar ta, ta na dariya ta koma ta konta


After one week


Kwana biyar bayan Malam ya fada mata cewa Zayd ne mijin na ta, ya dawo da ga tafiyar da ya yi, a ranar nan kuma a ka kai Inaya dakin mijin ta , tun bayan ta koma gidan shi har yanzu ba ta daura ido saman shi ba, kullum a falo ta ke kwana saman sofa sai in ta na bukatar yin wanka ko alwalla sannan ta ke tashi ta shiga bedroom din shi ta wuce toilet ta yi
Duk kayan ta su na cikin trolley din ta dama ba wasu kaya dayawa ba gare ta gashi ko lefe ba a yi mata ba

Bangaran Nesrine kuma kullum in ta je school sai Hafiz da Moctar sun saka ta gaba a kan ina Inaya amma sai ta ce musu ta koma gidan mijin ta
Nan Moctar ya tada tarzoma a kan karya ta ke ya bar college din cikin fushi shi da Hafiz
Tun ranar ba su sake dawowa college din ba
Abun da ba ta sani ba kullum sai sun zo , sun buya sai in an sauka su ke bibiyar ta amma kullum ita kadai ke tafiya gida har Hafiz ya fara gajiya ya kyale Moctar ya ci gaba da bibiyar ta shi kadai dan shi ya kwalafa rai sosai a kan Inaya


Misalin karfe 5 na yamma


Inaya

Zaune ta cikin falon gidan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login