Showing 6001 words to 9000 words out of 75226 words

Chapter 3 - Exiled Princess Book 1 Hausa Novel Complete

Meerah   

13 Dec 2024

287

shi

Ganin bai ce komai ba ya sa Abdoul juyawa ya koma gida


Shi ma Zayd hanyar gidan shi ya kama
Bai fi minti biyu ba ya iso gida

Da sallama bakin shi ya shigo falon gidan nan ya isko Moussa ya na zaune saman sofa da ga shi sai short da singlet ya na latsa wayar shi


Dago kai ya yi ya na amsa mishi sallamar shi kafin ya ce " Amir wai ina ka tsaya ne haka tun dazu ni ke jira ka "

A hankali ya sa hannu ya zame glass din idanun shi
Allahuma barik ashe ba banza ba ya ke saka glass ba
Ya na da dara daran idanu Farare kal kamar madara
Launin idanun shi Hazel mai bala'in kyau, sai wani shining ya ke abun har ya ba ka tsoro kamar idanun mage cikin dare haka su ke


Karasowa ya yi cikin falon ya ajiye glass din saman table sannan ya jingina bayan shi a jikin sofar ya daga kan shi sama ya lumshe idanun shi

Duk abun da ya ke Moussa ya na kallon shi amma bai ce da shi komai ba dan ya san abokin na shi ba karamin miskili ba ne ba bazan ba a ka kassa gano shi ba kurma ba ne


Ajiye wayar shi Moussa ya yi saman table kafin ya matso bakin sofar ya kai hannu shi ya dafe cinyar Zayd

Medo kan shi ya yi a hankali sannan ya bude idanun shi ya daga mishi gera allamar minene ?


" Amir wai me ya ke damun ka ne , duk ka bi ka sauya kamar ba Al-Amir Nawfel ba magajin Malik , ko dai ka fada soyayya ne " ya kai karshen ya na kashe mishi ido guda


Dan tsaki Zayd ya ja kafin ya kauda kan shi gefe kafin ya ce " Diya dan Allah ka bar kira na da wannan su nan, wannan sunnan ya goge da ga cikin rayuwa ta tun lokacin da mu ka shigo garin nan "


" in haka ne ka daina kira na da Diya ni ma , yanzu Amir baza ka koma ka karbi mulkin ka ba "


Da sauri ya katse shi da cewa " ai Malik bai mutu ba , har yanzu ya na kan mulki kuma ko ya mutu ba ni son mulkin, a kan shi a ka nemi halaka ni dan haka su je na bar musu kayan su , na ga ai kaima yarima mai jiran gado ne me ya sa baza ka koma masarautar ku ba ka karbi mulkin "


Yar dariya Moussa ya yi ya na dauke hannun shi da ga saman cinyar Zayd sannan ya ce " haba kai ma Zayd ta ya zan karbi mulki bayan ni ne na uku babban yayan mu na raye zan ce na karbi mulki shi ya sa na baro musu kayan su , ni fa mulki sam ba ya cikin tsarin rayuwa ta ba yadda za ka yi an haifo ka cikin jinin sarauta dole ka hakura "

Mikewa tsaye Zayd ya yi ya bar falon

Har zai shiga corridor ya tsaya ba tare da ya juyo ba ya ce " ka na da labarin Amira da Malikat Al'Umu ? "

Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " kar ka damu su na cikin koshin lafya "

Jinjina kan shi kawai ya yi sannan ya fara takawa ya shiga corridor din ya shiga bedroom din shi

Ya na shiga shi ma Moussa ya mike ya koma bedroom dinshi shi ma


Washe gari

AMINU KANO COLLEGE OF EDUCATION


Nesrine


Zaune ta ke kassan wata bishiya cikin harabar college din ta na rike da wani book ta na karatu


Kamar da ga sama ta ji an zabce mata book din ta

A dubu dari ta dago kai , wata irin mumunar faduwa gaban ta ya yi lokacin da ta yi arba da wanda ya zabce mata book din ta


Wasu samari ne guda biyu su na tsaye gaban ta

Wanda ke rike da littafin ta ya fi dayan tsayi kadan ya kuma fi shi haske ya na da dogon hanci da kananan idanu ya dan tara gashin kai
Ya na sanye da crazy jeans blue da t-shirt blue ita ma

Daya kuma ya na da dan duhu kadan amma kamanin su daya sai dai wannan bai tara gashin kai ba, idanun shi brown colour ne , kuma ya na da saje lips din shi kuma sun dan yi pink kadan
Shi kuma ya na sanye da jeans baki da t-shirt fara


Wanda ke rike da book din ta ya fara magana ya ce " baby wai ba na ce da ke ba ki ringa samu na a wajen parking space lokacin break ba "

Wasu yawu Nesrine ta hadiye murya na kerma ta ce " yi hakuri Hafiz bazan sake ba "

Geffen ta ya zo ya zauna ya na mika mata book din ta ya ce " ba komai baby nan din ma ya na da dadin zama sai dai da mutane dayawa shi ya sa na ce ki ringa tarda ni parking space "


Ta na shirin magana ta ji Muryar Inaya ta na yi musu sallama

A tsorace ta dago kai ta kale ta

Inaya kuma ta yi zaton classmate din nesrine ne sai ba ta ka komai a ran ta ba ta kali yar uwarta ta ce " Nesrine dan Allah in kin tashi tafya gida ki jira ni "
Ta na gama fadar haka ta juya da gudu ta bar wajen kamar ta ga wani abun tsoro


Tun da ta iso wajen saurayin da ke tsaye ya tsare ta da idanu sai kallon ta ya ke ya na hadiye yawu


Sai da ta bar wajen ya na kallon ta har ta kure wa kallon shi sannan ya dawo da kallon shi kan hafiz ya ce " bro wacece wacen yarinyar ta hadu fa, she look so innocent "

Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san in Moctar ya lakewa Inaya ta shi ga uku cikin college din nan dan sai ya azabtar da ita shi ma ba karamin mugu ba ne ga son mata


Ta yi nisa cikin tunanin ta sai ji ta yi an daura hannu saman cinyar ta

A razane ta dawo cikin hayacin ta, ta na kallon hannun hafiz da ke saman cinyar ta

" lfy baby ina tambayar ki kin yi shiru " ya fada ya na leko face din ta

" minene ? " ta fada cen kassan makoshi

Dan murmushi yayi kafin ya ce " who is she , ko sister din ki ce "

Da sauri ta ce " a'a kawai saman hanya na hadu da ita "

" okay meye sunnan ta " ya tambayeta ya na tsare ta da ido

Wasu yawu ta hadiye kafin ta ce " ban sani ba "

Tass ta ji saukar mari a face din ta

Da sauri ta kai hannu ta saman kumatun ta ta na dafe wajen wasu hawaye na zubo mata

Mike wa tsaye ya yi cikin bacin rai ya daga mata murya ya ce " ni za ki raina wa hankali ke har kin isa ki min karya "

Ya na gama fadar haka ya kai hannu ya shake ta ya hada kan ta da bishiyar cikin tsawa ya ce " meye sunnan ta na ce miki "


Cikin kuka ta ce mishi " Maryam sunnan ta Maryam " da kyair kalmar ta karshe ta fito dan ba karamar shaga ya yi mata ba

Ganin ya na neman ya kashe ta ya sa Moctar kai hannun shi ya dafa kafadar shi ya ce " bro sake ta kar ta mutu "

Da sauri ya janye hannun shi da ga wuyan ta , ya ja baya kadan kafin ya ce " nan gaba ki san irin amsar da za ki ba ni in na tambaye ki " ya na gama fadar haka ya juya ya bar wajen

Bin bayan shi Moctar ya yi su ka bar wajen


Su na barin wajen ta fadi kassa ta konta ta na sauke kuka mai cin rai

Sai da ta share wajen good 30 minutes ta na kukan sannan ta mike a hankali ta na jan kafa ta nufi toilet din mata ta wanke face din ta sannan ta dawo ta dauki school bag din ta ta tafi class



❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥


( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )



STORY & WRITTEN BY : ANISH


Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺

https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i

♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡


PAGE 3 ❤🔥


After some hours


Tafiya su ke saman titi a jere , Nesrine ta yi nisa cikin tunanin ta , ita kuma Inaya sai wassan nin ta ta ke kamar karamar yarinya

Su na tsaka da tafiyar su wata mota fara kirar Mercedes ta tsaya a gaban su ta tare musu hanyar wuce

Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san ko wanene
Inaya kuma ta yi tsaye ta na kallon motar dan ita ba ta san ko su waye ba

Su na tsaye a hakan su ka ga an bude kofofin gaban na motar Hafiz da Moctar su ka fito

Gaban su ka zo su tsaye sannan Moctar ya ce " yan mata ku zo mu rage muku hanya mana "

Dan murmushi Inaya ta yi sannan ta riko hannun Nesrine ta ce " mun gode amma mun iso gidan ai " ta kai karshen ta na rabawa ta geffen su za ta wuce


Da sauri Moctar ya sha gaban su ya ce " haba yan mata taimako ne fa "

" babu komai mun gode gidan mu fa cen karshen layin ne , ka ga kuma ba ni son Abban mu ya kan ki zai mana fada "

Ba ta gama rufe bakin ta ba ta tsinci Muryar Hafiz ya na fadin " ke Nesi wuce cikin motar nan na kai ku gida "


Wasu yawu Nesrine ta hadiye ta na tsoron ta shiga motar in malam ya gan ta zai yi mata fada, in kuma ta ki ta san halin Hafiz yanzu zai yi mata Dukan mutuwa kuma ba izinin ramawa, kawai sai ta tsaya ta na faman muzurai

Ta yi nisa cikin tunanin ta sai tsintar Muryar Abdoul su ka yi ya na fadin " Nesrine me ku ke yi a nan ? "

A razane ta juyo ta na kallon shi zuciya na duka uku uku
Ya ko tsare da wadanan dara daren idanun shi


" yaya Abdoul dama classmate din su Nesrine ne su ka ce wai su rage mana hanya shi ne na ce musu mun ma iso gida amma su ka ki yarda " Inaya ta fada babu ko tsoro


" shikenan ba komai wuce ko tafi gida yanzu "

Tun bai rufe bakin shi ba Nesrine ta kamo hannun Inaya ta raba ta geffen Moctar da sauri ta bar wajen

Su na barin wajen Abdoul ya juyawar shi shi ma ya yi tafiyar shi su ka bar Hafiz da Moctar tsaye a wajen


Bayan Abdoul ya bar wajen Moctar ya kali Hafiz da ke ta hura hanci ya ce " kai dan malam rage wannan fushin na ka, ga shi yanzu sun tafiyar su ba tare da mun ga gidan su ba "


Dan tsaki Hafiz ya ja sannan ya juya ya fara takawa ya na fadin " ai mun hadu school "

" kai malam kar ka manta ba college din ba mu ke , yawwan zuwan mu cen ya janyo mana matsala "

Geffen driver Hafiz ya bude ya shiga
Ya na ganin ya shiga motar shi ma ya bude geffen mai zaman banza ya shiga

Bayan ya shiga Hafiz ya tada motar su ka bar wajen da mugun gudu


Duk abun da ya faru a kan idon Zayd , dan ya na biye da su Inaya amma su ba su gan shi ba , ya na shirin ya je ya yi ma su Hafiz Dukan tsiya ya ga Abdoul ya shawo kwanar ya nufi su Inaya kawai sai ya yi tsayiwar shi sai da ya ga tafiyar su sannan ya juya ya kama hanyar komawa gidan shi


Bangaran Inaya kuma , sai da su ka isa cikin gidan babu wanda ta ce da yar uwarta wani abu

Sai da suka shiga cikin bedroom din su sannan Inaya ta kwace hannun ta da karfi ta dan ja baya ta na kallon Nesrine ta ce " wai me ya same ki Nesrine kin ga yadda saurayin cen ya yi miki tsawa kuma ki ka kassa ce mishi wani abu "


Cire hijabin ta Nesrine ta yi ta ajiye saman sannan ta zauna geffen gadon ta dago kai ta kali Inaya ta ce " Inaya ke karama ce baza ki gane ba amma wlh ki raba hanya da samarin nan ko cikin school in ki ka gan su ki tsere ki buya dan wlh ba mutanan kirki ba ne " ta na gama fadar haka ta tashi ta fice da ga dakin



Inaya dai ta na tsaye ta na kallon ta har ta ida maganar ta ta tashi ta bar dakin ba ta ce mata komai ba


Nesrine kuma bayan ta fita kai tsaye toilet ta shiga

Maimakon ta yi wanka sai ta jingina a jikin bangon toilet din ta aza kuka

Cikin kukan nata ta ke fadin " ya Allah na roke ka raba ni da Hafiz , ya Allah ko ba ka raba ni da shi ba kar ka bari ya kusan ci yar uwata , ban San me na yi mishi a duniya ba ya ke neman ya cutar da ni , na shiga uku ni Nesrine , RAMATOU kin cuce ni kin hada ni da bala'i da na sani bazan taba yarda da abotar ki ba, Allah ya isa tsakani na da ke "

Haka ta yi ta dimimuwan ta har ta gaji ta yi shiru sannan ta yi wanka ta fito ta koma bedroom din su

Ta na shiga ta tarda Inaya har ta yi barci dan gajiya


Misalin karfe 5 na yamma

Inaya

Zaune ta ke bakin kofar gidan su saman wasu duwatsu ta na faman wassa ita kadai kamar karamar yarinya


Tun da ga nesa ya hango ta zaune ta cikin bakin glass din shi
Ya na tare shi da Moussa, ya na sanye da wandon jeans baki da t-shirt dark blue , shi kuma Moussa jallabiya ce fara ya ke sanye da


Lokacin da Moussa ya gan ta ya saki murmushi ya kali Zayd ya ce " Amir ga fa babyn ka cen ta na wassa "

" ina ga yarinyar nan ta na da matsala a kwakwolwar ta " ya fada mishi cen kassa kassa ta yadda shi da Moussa kawai su ka ji abun da ya fada


Jinjina mishi kai Moussa ya yi dan ya lura yanayin ta bai yi kama da masu cikakiyar lafya ba a shekarun ta


Haka su ka ci gaba da tafiyar su har su ka karaso inda ta ke zaune su ka yi mata sallama

A hankali ta dago kan ta, ta na amsa musu sallamar su kafin ta ce " ina wuni yaya Moussa "


Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " lafya lau babyn malam , ko dai in ce babyn Zayd "

Dan zaro idanu ta yi ta na kallon Moussa sannan ta kali Zayd da ya tsareta da ido

Turo dan bakin nan nata ta yi gaba ta shagwabe fuska sannan ta ce " a'a ni babyn malam ce ni na ma tafiya ta wajen Abba " ta kai karshen ta na mikewa ta fara tafiya


Da sauri Moussa ya ce " to tsaya mu raka ki mu ma cen za mu je "
Da sauri Zayd ya kale shi dan ya lura Moussa na neman ya kwabo mishi ruwa

Jinjina mishi kai kawai ta yi ta ci gaba da tafiyar ta

Su kuma juya su ka bi bayan ta, ba yadda Zayd ya iya dole ya hakura ya bi bayan shi su ka tafi


Tun da su ka kamo hanya ya ke kallon ta ta cikin glass

Ita kuma sai wasu juye'juye ta ke ta na halba kafa ta na wassa yadda kassan me shekara biyar haka ta ke

Shi kuma Zayd wannan abun da ta ke ya na yawwan tuno mishi da kanwar shi dan ita ma haka ta ke da rawan kai

Kawai sai ya tsinci kan shi ya na jin wani bakon yanayi , cikin zuciyar shi ya ce " she is so cute and innocente why malam zai aura min ita da karancin shekarun ta haka , ya kamata na tambaye shi dalilin shi na yin hakan "

Sai magana ya ke cikin zuciyar shi har su ka karaso sangayar Malam bai sani ba, sai da Moussa ya kai hannu ya taba shi ya na fadin " Amir ba ka ji ne malam na gaida ka ? "


A dan razane ya juyo ya kali Moussa sannan ya meda kallon shi kan Malam da ke zaune saman tabbarma sanye da manyan kaya ga Inaya geffen shi ta rungume shi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login