Showing 21001 words to 24000 words out of 75226 words
ta buga uban tagumi kamar ta yi kuka ita kadai cikin gidan
Ta na a haka ta ji a na sallama
A hankali ta dago kan ta, ta amsa sallamar
Zayd ne da Moussa su ka shigo gidan ko wane ya na rike da ledodi
Ta na ganin su ta saki murmushi ta ce " sannu da dawowa "
Moussa ne ya amsa mata ya na murmushi ya na takowa ya ajiye ledodin hannun shi saman sofa sannan ya zauna saman sofar da ke fuskantar ta ta
Shi ma Zayd takowa ya yi ya ajiye ledodin hannun shi saman table sannan ya zauna geffen Moussa ya jingina a bayan sofar ya daga kai ya lumshe idanu shi ta cikin glass din shi
Murmushi ta yi kafin ta mike ta nufi dining table ta bude fridge ta dauko jug na ruwa ta ajiye saman tray da glass biyu
Sannan ta dauko tray ta komo falo , ta ajiye shi saman table ta zuba ruwan cikin glass ta mika wa Moussa
Karba ya yi ya na murmushi ya yi mata godiya
Har ta dauki guda glass za ta zubama Zayd Moussa ya yi saurin cewa " bari ba sai kin zuba mishi ba azumi ya ke "
Dago kai ta yi ta kaleshi sannan ta saki dan karamin murmushi sannan ta mike ta koma saman sofar da ta tasso ta na sunkuyar da kai
Ta na zama ko , Zayd ya mike tsaye ya nufi corridor ya shiga bedroom din shi
Da kallo su ka raka shi ita da Moussa har sai da ya shiga bedroom din shi sannan ta kali Moussa ta ce " yaya Moussa ina ganin yaya Zayd ba ya so na "
Dan murmushi yayi kafin ya ce " haba babyn malam ya isa ma ya ce ba ya son ki kawai aiki ne ya yi mana yawa kwanan nan shi ya sa ki ka ga ba ma yawwan zama gida "
Jinjina mishi kai tayi sannan ta sunkuyar da kai ta fara wassa da dan yatsun ta
Dan murmushi yayi kafin ya matso bakin sofar ya kai hannu ya dauki ledodin da su ka zo da su sannan ya mike ya tako gaban ta ya ajiye mata su sannan ya ce " Ga tsarabar ki nan, sannan ki shirya gobe za ki koma school "
Da sauri ta dago kai ta kaleshi ta ce " yaya Moussa school fa ? Yaya Zayd ya yarda ? "
Jinjina mata kai ya yi kafin ya ce " yes ya yarda mana shi da kan shi ya je ya sayo miki sabon uniform , da sauran abubuwan da za ki bukata "
Da sauri ta mike tsaye ta na tsale ta na dariya kamar karamar yarinya
Shi dai Moussa ya tsaya ya na kallon ta ya na murmushi " she is si innocente " ya fada cikin ranshi dai'dai lokacin da ya ke juya wa zai shiga corridor
Har ya yi nisa ya tsinci Muryar ta ta na fadin " nagode yaya Moussa "
Ba tare da ya juyo ba ya ce " ba ni ya kamata ki yi ma godiya ba "
Ya na gama fadar haka ya ci gaba da takawa ya nufi bedroom din Zayd
Bai mishi knocking ba kawai ya wuce bedroom din kai tsaye
❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
STORY & WRITTEN BY : ANISH
Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
PAGE 9 ❤🔥
Zayd
Ya na zaune bakin gadon shi ya na rike da wayar shi amma ya cire bakin glass din shi
Geffen shi Moussa ya tako ya zauna sannan ya ce " Amir ! "
Ba tare da ya dago kan shi ba ya ce mishi " uhmm ? "
" Amir na yi tunanin maganar da na yi maka za ka saurare ni , wai me ya sa duk abun da na fada maka in dai ba ka niya ba baza ka yi shi ba , yanzu sati guda da ka je gidan su yarinyar nan ka dauko ta amma ko kalma daya ba ka taba ce mata ba , ka ce min akwai binciken da ka ke son yi a kan ta, in ba ta zauna kusa da kai ba ta ya za ka yi binciken , Zayd wlh ba na jin dadin abun da ka ke mata , shin minene laifin ta a ciki, ka na ga karama ce sosai ko ba za ka iya soyayya da ita ba ka kula da ita a matsayin kanwar ka mana "
Shi dai Zayd ko dago kai bai yi bare ya ce mishi wani abu
Sai da ya gaji da zubar shi sannan ya ce " Amir ina son in san dalilin da ya sa aka aura maka ita "
Wannan karan sai da ya dago kai slowly ya kale shi kafin ya ce " a kan hakan ni ke bincike "
Dan zaro idanu Moussa ya yi kafin ya ce " ban gane ba kawai malam zowa ya yi ya ce ka aure ta kai kuma ka yarda ? In da ba ka son ta na minene za ka yarda "
Ajiye wayar hannun shi ya yi saman bedside drawer sannan ya juyo da kyau ya kali Moussa sannan ya ce mishi " ba haka ba ne , shekara biyu baya , lokacin ka tafi Abuja dibo company , dai'dai na fito da ga cikin gida na hadu da malam ya na tafiya da sauri ko kallon gaban shi ba ya yi, a haka har ya kai min karo ya yi baya zai fadi , bayan na taro shi ya na yi min godiya kuka ya kubce mishi har da hawaye, na yi matukar mamaki ya babban mutun na kuka haka kamar karamin yaro , na so na ki dalilin kukan na shi , sai na ja hannun shi mu ka shigo gidan nan na zaunar da shi sannan da hannu na tambaye shi minene ya ke kuka nan ya ke ce min " Zayd kashe min auta ta za su yi yanzu shekara biyu ina boye ta amma ina ji a jiki na wannan karan sai sun gano mu ban San ya zan yi ba " ni sam ban gane abun da ya ke nufi, sai na tsaya ina kallon shi ina son in karanci abun da ya ke nufi, sai da ya ida kukan shi sannan ya riko hannu na ya ce min " don Allah Zayd ina son in roke ka wata Alfarma " jinjina mishi kai na yi , ina kallon shi ya mike tsaye ya dawo gaba na ya zube saman guyiwowin shi ya ce min " don Allah Zayd ina son ka auri Inaya " a rude na mike tsaye ina fadin " what aure ? " mikewa malam ya yi ya na zaro idanu ya na kallo na ya ce " Zayd, dama ka na magana ? " ban amsa mishi tambayar shi ba na ce " uncle yi hakuri gaskia babu aure a sha'anin rayuwa ta bare kuma wannan yarinya ta yi min kannan ta " komawa ya yi ya zube saman guyiwowin shi ya riko kafafuna ya roke ni da na yarda na aure in ba haka ba komai zai iya faruwa da ita kuma duk abun da ya faru da ita da hannu na a ciki tun da na samu damar ceton rayuwar ta amma na ki duk ya bi ya kashe min jiki ba yadda zan yi na yarda , a ranar a ka aure na da ita, limamin massalaci ya zama waliyi na, shi kuma malam na ta na biya sadaki a ka aura mana aure , duk lokacin da na tambayi malam dalilin da ya sa a ka aura min ita sai ya ce min in bari in lokacin ya yi zan sani , dalilin da ya sa na ce yanzu ta dawo gaba na na dinga ganin ta ko zan gano dalilin da ya sa malam ya aura min ita " ya kai karshen ya sauke ajiyar zuciya ya dan lumshe idanun shi dan ba karamar wuya ya sha ba wajen yin wannan maganar duka
Jinjina kan shi Moussa ya yi kafin ya ce " yanzu me ka ke tunani a kai ? "
" duk yadda a ka yi akwai wanda ke bibiyar rayuwar ta , ka manta ranar nan ta na zaune ta fara sakin kara kamar wadda a ka dauke da karfi , wai ba ka lura da wasu abubuwa da ta ke kamar mara hankali "
Dariya Moussa ya yi kafin ya ce " O'O kenan ka na lure da duk wane abu da ta ke "
" of course ba matata ba ce " ya fada a takaice ya na mike wa ya wuce toilet
Da kallo Moussa ya raka shi har sai da shiga toilet sannan ya ce " matar ka ko , to za ka ga yadda zan yi wufff da ita dan rainin hankali "
Sai da ya ida sambatun shi sannan ya mike ya fice ya koma bedroom din shi
Bai jima da fita ba Zayd ya fito da ga cikin toilet ya yi Alwalla sannan ya fito dakin kai tsaye corridor ya baro ya shigo falo ta na nan zaune saman sofa ta na kallon Tv
Har ya yi gaba zai wuce ya tsaya cak a hankali ya juyo ya zuba mata ido
Ta na zaune waje guda kamar kungi ko kifta ido ba ta yi
Slowly ya tako ya tsaya gaban ta ya dan sunkuyo ya na kallon face din ta
Ko motsi ba ta yi kamar wanda ya suma
Yatsun shi biyu ya kai saitin face din ta ya kyasta mata
Da karfi zuciyar ta ta buga ta yi baya ta fadi konce saman sofar ta na nunfashi sama sama idanu a lumshe
Shi duk ya bi ya rude ya rasa mai zaiyi ya tsaya kawai ya zuba mata idanu
Sannu sannu nunfashin ta ya fara dawowa dai'dai
A hankali ta bude idanun ta ta na kallon ceiling din falon
A haka Moussa ya fito ya same su
Ya na ganin su a haka ya saki murmushi cikin ranshi ya ce " me kuma ka yi ma y'ar mutane ? "
Ya na gama fadar haka ya karaso geffen Zayd ya tsaya ya kale shi ya ce " Amir lafya wani abu ka yi mata ? "
Girgiza mishi kai Zayd ya yi ba tare da ya ce komai
Medo da kallon shi kan Inaya ya yi kafin ya kira sunan ta
" Na'am " ta amsa mishi ta na kallon ceiling din
" me ya faru ne ? " ya tambayeta ya na lekon face din ta
A hankali ta fara kokarin dagowa ta gyara zaman ta sannan ta ce " yaya Moussa yi na yi kamar an danne min zuciya, duk ta yi min nauyi "
Murmushi kadan Moussa ya yi kafin ya ce " shikenan ba komai har yanzu ki na jin hakan ? "
Girgiza mishi kai ta yi kafin ta dago kai a hankali
Idanun ta ba su sauka ko ina ba sai cikin nashi, shi ma ita ya ke kallon ta cikin bakin glass din shi
Da sauri ta sunkuyar da kan ta ta takure waje guda
Kai a sunkuye ta ga ya miko mata hannu
Da sauri ta dago kai ta kaleshi ta na son ta yi magana amma ta ki fitowa
A hankali ta medo da kallon ta kan hannun shi kafin ta dago nata slowly ta daura a saman na shi
Dum zuciyoyin su su ka buga lokacin guda , dalilin mi ? Oho su kadai su ka sani
Ta na daura hannun ta, ya janyo ta ta mike tsaye sannan ya juya su ka fara tafiya a hankali ya na rike da hannun ta
Sai da su ka shiga bedroom din shi sannan ya saki hannun da hannu ya mata allamun " ki shiga ki yi Alwalla ki yi sallat sai ki konta "
( WAI DAMA ANA MAGANA DA HANNU 🤔🤔 )
Jinjina mishi kai tayi ba tare da ta ce komai ba
Juya wa ya yi ya fara takawa har ya kai bakin kofar dakin ya tsinci Muryar ta, ta na fadin " a dawo lafya yaya Zayd ! "
Jinjina mata kai kawai ya yi ba tare da ya juyo ba ya ci gaba da tafiyar shi
Ya na fita ita ma ta juya ta shiga toilet din
Shi kuma ya na fitowa ya tardo Moussa zaune saman sofa ya na latsa wayar shi
Ya na ganin shi ya saki murmushi ya ce " na dauka , ka na cen ka cin angoncin ka ka kyale ni nan "
Dan tsaki ya ja ya ci gaba da takawar shi zai bar falon
Dariya Moussa ya yi kafin ya mike ya bi bayan shi da sauri
Su na fitowa harabar gidan Moussa ya kaleshi ya ce " Amir ka gano abun da ke damun ta ne ? "
Sai da su ka fita gidan sannan ya ce " na gano nan gaba "
Jinjina mishi kai kawai Moussa ya yi su ka ci gaba da tafiyar su har su ka isa mosque
Basu dawo gidan ba sai bayan sallar isha, nan su ka isko ta gyara gidan tsab sai kamshin turare ya ke , har da abinci ta girka musu ta jera komai saman dining table
Kallon Zayd Moussa ya na murmushi ya ce " kai da ka cewa mu wuce restaurant mu sayo abinci, madam har ta shirya mana ashe "
Kauda kan shi gefe Zayd ya yi sannan ya ci gaba da takawa ya shiga corridor ya wuce bedroom din shi
Nan ma wajen a gyare ya ke sai tashin turare ya ke , ta share ko ina ta goge ta canja mishi bedsheet
Sai da ta gyara komai sannan ta yi wanka ta sauya kaya ta Haye bed din ta konta
Dan karamin murmushin geffen fuska ya yi sannan ya juya ya bar mata dakin dan ba ya son tada ta
Falo ya fito nan ya ga Moussa saman dining table sai cin abincin ya ke
Chair din da ke fuskantar tashi ya ja ya zauna sannan ya fara serving din kan shi dan shi ma fa yunwar ya ke ji , ya na iya jure komai a duniya amma banda yunwa shi ya sa duk irin fushin da zai yi bazai yi fushi da abinci ba
Bayan ya yi serving din kan shi ya deba a spoon ya kai baki
Sai da ya dan zaro idanu lokacin da ya ji taste din abincin, ba karamin dadi ya yi mishi ba
Duk abun da ya ke Moussa na kallon shi ta kassan ido, cikin ranshi ya ce " tukunna ma sannu sannu sai ta mamaye wannan zuciyar ta ka ta dutse "
Haka su ka ci gaba da cin abincin ba wanda ya ce ma wani kala har sai da su ka ida su ka sha ruwa su ka daura da juice sannan Moussa ya riga shi cewa " Amir gaskia da ga yau na daina cin abincin restaurant baby na zai dinga girka min "
Kallon shi da kyau Zayd ya yi kafin ya ce " wane baby kuma ? "
Dariya sosai ya yi sannan ya mike tsaye ya tatare dishes din ya gyara wajen ya meda su kitchen sannan ya dawo ya wuce falo
Sai da ya zauna sannan shi ma Zayd ya taso ya shigo falon ya zauna ba wanda ya ce ma wani ufan har sai da Moussa ya koma bedroom din shi ya bar Zayd nan a falon
Misalin karfe 12 na dare
Ya na konce saman doguwar sofa ya daura hannun shi guda saman goshin dayan kuma saman ciki ya lumshe idanun shi
Ya na a haka ya jiyo takun mutun, a hankali ya ware idanun shi dan dama ba barci ya ke ba kawai ya lumshe idanun shi ne
A hankali ya dago kai ya kali saitin da ya ke jin takun mutun din
Sai da ya dan zaro idanu ganin ta , ta na tafiya a hankali idanu a rufe
Ya na kallon ta har ta shiga kitchen
Da sauri ya mike ya bi bayan ta , ya na shiga kitchen din ya gan ta rike da wuka ta na shirin caka ma kan ta
Dan zaro idanu yayi a dubu dari ya yi kan ta ya karbe wukar har sai da ta dan yanke shi , dan rumtse idanun kadan ya yi ya sake budewa a kan ta
Ta na tsaye waje guda sai tangal tangal ta ke ido rufe
" wai me ya ke damun yarinyar nan ' ya fada cikin zuciyar shi
A hankali ya kai hannu ya dauke ta cak kamar baby ya juya ya baro kitchen din, kai tsaye bedroom din shi ya meda ta ya kontar da ita saman gadon sannan shi ma ya Haye ya konta ya na kallon ta , a haka har barci ya dauke shi
Washe gari
Misalin karfe 4 na safe ya farka da ga barcin shi
Ya na bude idanu su ka sauka a kan ta , ta juyo su na fuskantar juna ta na sauke nunfashi a hankali
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya juya a hankali ya sauko kafafun shi kassa sannan ya mike tsaye ya nufi closet din kayan shi ya bude ya dauki kayan shi wandon