Showing 42001 words to 45000 words out of 122700 words
bin Zahra kafa ya kafa har ta dauko kayan ta da aka gana screening suka fito, a Nan ya fada Mata sunansa Mushahu shi Dan Kano ne Yana aikin government Yana Kuma kasuwwnci yanzu ma harkar kasuwancin ta kawo shi kasar. Zahra ma ta fada Masa sunanta da inda take karatu da Dan zaman da zatayi anan kasar kafin ta wuce.
Bai bar airport din ba har Saida Mama Hanifa tazo daukar zahra, da yake Mushahun wise ne sosai ya sake da Mama Hwnifar don Basu rabu ba har Saida ya karbi address din gidanta, saida suka bacewa ganinsa sannan Shima ya nemi taxin cikin airport ya nufi hotel din da yake sauka idan yazo kasar da buri kala kala a zuciyarsa kan Zahra.
Satinta daya ata nufi syprus kafin lokacin Mushahu ya Kai Mata ziyara yafi sau hudu ba karamin samun shiga yayi a gurin Mama Hanifa ba.
Zauwanta makaranta da kwana daya Sajida da Khadijah da Fatima suka dawo Anisa ce Bata dawo ba suna Umara da Yayarta sai Kuma sukayi Dan Samu matsalar visa.
Karatu Suke ba Kama hannun yaro Koda yaushe suna busy da karatu, tunda Zahra ta rabu da Musbahu a turkey Sam ta aje batunsa a gefe duk da kusan Kullum saiya kirata sun gaisa Yana ta kafa gwamnatin sa a gurinta. Bazato ba tsammani ranar wata Saturday taje weekend gidan Uncle Haisam ya kirata da number din kasar Yana fada ya shigo kasar tayi jiransa Nan da awa daya ze shigo makarantar, ba karamin mamaki tayi ba da jin hakan, dan harga Allah batayi zaton da gaske yake ba da yace Mata Yana Nan zuwa syprus din.
Nan da Nan ta fadawa Aunty Jinan matar uncle zata koma school yau suna da wani group Assignment data manta zasuyi ta taho, Bata Hana ta ba tunda Daman uncle din baya kasar sunje wani aiki south Korea, snacks Aunty jinan ta hada Mata masu yawa ta tafi dasu. Allah ya taimaketa ta fito da card dinta na shiga bus ko train, mintina talatin masu kyau suka kawota kyrenia city.
Lokacin data shiga hostei dakinsu ta wuce ta Kara gyara jikinta.
Wani karamin basket da dauko ta zuba snacks da drinks masu sanyi, turare ta Kara fesawa har Brandy wadda Suke daki daya take tambayar ta ko zataje wani park ne ta huta yau weekend?
Eh kawai tace Mata tayi gaba ta fita daga dakin, gurin su Sajida ta nufa akayi rashin sa'a duk basa Nan sai Anisa kawai ta Samu tana sallah.
Zama tayi tana tunanin yanda lamura Suke ta juya Mata kamar a almara ko wannan din shi ya zata Kaya a kansa? Dan haka Nan taji bazata iya yi Masa rashin kirki ba Dan duk Wanda ze Bata kudinsa da lokacin sa ya biyoka har wata kasar duk da baka bashi fuska ba to kuwa Bai cancanci wulakantawa ba a gurinka.
Kafin Anisa ta idar da sallar wayar Zahrar tayi Kara alamun Kira ya shigo, number dazu ce ta daga tayi sallama, daga can ya fada Mata ya shigo ciki da inda yake.
Bayan sun gama wayar ne Anisa ta idar da sallar ta kalli Zahrar tana fadin "yaushe Kika dawo nayi zato sai Monday da safe Zaki dawo?".
"Ke dai Bari kawai wallahi guy din Nan Dana fada muku mun hadu a airport din Kano Yana kallona har ya bini gidan Mama Hanifa?"
Kai Anisa ta gyada alamar ta gane.
"To shine fa dazu ya kirani Wai gashi a kasar ya cika Alkawari zuwa anjima ze shigo Nan gurina, shine yasa na dawo yanzuma kiransa ne ya shigo Yana gurin garden din can na gurin second gate".
A gurin suka same shi Yana tsaye kusa da wani kangaroo na siminti Yana kallonsa har da kanana a kusa dashi yayi kyau sosai kamar na gaske, ya shagala da kollon har baisan sunzo gurinsa ba Saida Anisa tayi Masa sallama sannan hankalinsa ya kawo kansu. Wani irin mahaukacin kyau yaga Zahrar ta karayi a idonsa, kasa dauke idanunsa yayi daga kanta. "Masha Allah!"
Ya furta a hankali Yana fadada fara'a akan fuskarsa tare da amsa sallamarsu.
Karkashin wata bishiya Anisa ta nuna masa inda akayi kujerun sumunti masu kyau sosai, bayan sun zauna ne Anisa ta gaishe shi tana Masa ya hanya, sannan Zahra ta gaishe shi itama, duk sai taji duk wani iri saboda Sam lamarin maza gaba daya ya Gama fuce Mata daga Rai duk da bazata ce sun yaucareta ba Amman lamarin su a gurinta Mai girma ne Dan duk yanda taso ta manta abunda ya faru a baya Bata iyawa, Samun kanta tayi da wani irin Jin bazata iya watsa masa kasa a ido ba.
Sun jima suna tattaunawa da Anisa a fakaice Yana yiwa kansa campaign a gurinta, Anisar ta gabatar Masa da abubuwan da suka kawo masa, ita dai Zahra tana jinsu suna ta Hira kanta na kasa tana Dan Wasa da wani zoben white gold da Aunty Nawwara ta saya Mata lokacin da sukaje Umara.
Anisa ta jima sosai kafin tace zataje ta duba idansu Sajida sun dawo.
Bayan tafiyarta Musbahu ya yayi duk yanda zeyi ya janyo hankalin Zahrar ta sake dashi Kuma Alhamdulillahi kafin wani lokacin ta Dan sake ba kamar lokacin da suka zoba, a nan yake fada Mata shifa da gaske yakeyi yafi son kafin ta Gama makaranta a Gama komai tana gamawa kawai ayi bikin tayi service a gidansa. Saida aka dauki lokaci sosai sannan su Sajida suka karaso gurin bisa jagorancin Anisa, sun jima suna Hira sosai anan yake fada Mata Shima Dan kano ne sokoto road, ita Kuma ta fada Masa tana Jambulu Amma da suna zaune a Gwammaja ne.
Ya jima sosai kafin ya tafi,washe gari Sunday yaso su fita Amma Zahra ta nuna ba wannan maganar duk yanda yakai da naci ta Kiya har su Sajida suka saka Baki Amma ta qiya. Satinta daya ya koma inda ya sauke Mata kudaden masu yawa ya Kuma yi Alkawarin gabatar da kansa gurin iyayenta tunda bada Wasa yazo ba, itama Kuma Bata Hana ba tunda da gaske taji yes zata iya rayuwa dashi idan Allah ya amince.
Bayan barowarsa kasar da sati daya ya gabatar da kansa ga Alhaji Jafar a matsayin Mai son auren Zahra, Bai rufe Masa komai ba har zuwan da yayi syprus din,sai dai ya bashi hakuri akan zuwan daya Farayi kafin yazo gare shi, ba komai Alhajin ya nuna masa sai dai yace irin hakan bashi da kyau kodon gaba mutum yabi 'ya mace wata uwa duniyar batar da sanin magabatanta ba akwai hadarin lalacewar tarbiyya ga Wanda Allah yasa shaidan yafi karfin zuciyar su.
Alhajin yayi Masa tambayoyi sosai akan Sana'a da Kuma asalinsa, sannan ya fada Masa shima mahaifinsa ya rasu tun Yana level one hundred a jami'a, a labarinsa daya fada masa nan ya gano kanin mahaifansa sunyi makaranta tare dashi a Bauchi.
Bayan tafiyar Musbahun da Alhaji Jafar ya tada mutum takanas yaje har Kano da taimakon abokinsa Alhaji Muttaqa akayi Masa bincike kan Mushahu Kuma Alhamdulillahi ba'a Sami wani abun ashsha ba a tare dashi Dan mahaifiyar ma ta fito ne daga cikin manyan gidajen sarautar Kano.
Bangaren Zahrar kuwa kusan Kullum suna tare da Musbahun a waya Dan har ya haddace lokacin agogon kasar, tun tana daridari har ta sallama tare da karfafawar su Sajida kafin su gama semester din sun shaku dashi sosai Bata rufe Masa matsalar data fuskanta a baya ba, nuna Mata ma yayi rabonsa ne ya kawo aka ringa samun akasin na bayan ya Kuma yi Mata Alkawarin ruwa da iska ba abunda ze girgaiza tarensu bare har akai ga rabuwa Koda kuwa Aljani ne ya aurata in sha Allah sai yaga bayansa, yayi Mata alkawura da dama ya nuna Mata Babu wani abu da ze girgaiza shi koya bashi tsoro akan lamarin aurenta.
Magana tayi nisa Dan har iyaye sun shiga abinda yayiwa Ammah Dadi kenan Dan wannan karon Kam Zahra tayi Dace da Dan manyan mutane sosai, dan basu bar garin ba Saida suka shaida lokacin aure idan ta gama service da wata daya duk da sunso ayi bikin kafin tayi service din sai Alhajin ya nuna musu suyi hakuri tayi idan ta gama saita zauna guri daya ba daga kaita ba ba dadewa ta Fara fita kullum, Kuma ya Hana kayan lefe Dan Alkawari yayi ankawo biyu an karbe to kuwa ko waye zata aura sai dai ya aje Mata kayan idan taje gidan ya Bata.
Lokacin dasu Zahra suka Gama karatunsu har da Ammah da Hameeda akaje bikin graduation dinsu mutanen Jordan ma sunje har Mama Hanifa.
Bayan kammala taron sun Kara kwanaki a kasar, Zahra ta raka Hameeda kuraren shakatawa da yawa tayi kallo tayi santin inama Abba ya dawo dasu Nan Suma gashi ita har ta Gama Amma su Kullum karatunsu ba cigaba ana faman strike tunda a yanzu ma shine ya dawo dasu gida har ta samu damar zuwa itama.
Ranar da zasu taho sun Sha kukan rabuwa dasu Sajida tunda su saura shekara daya su gama.
Murna gurin Zahra ba magana ji take kamar ta sauke wani abu Mai nauyi daga kanta.
Musbahu yaso zuwa graduation dinsu Zahrar Amma lokacin Yana busy yaje wani special assignment a Kenya dole sai hakuri yayi, Amma Yana dawowa ya yiwa Azare dirar mikiya a ranar Zahra taga zallar so a gurinsa Dan ji yake kamar ya dauke ta yayi gaba da ita, itama ta bashi kulawa kamar me,Hameeda tazo sun gaisa sun Dade suna Hira dashi tambakar sun shekara da sanin juna, sunan mujiba ma ta shigo suka gaisa ba shi yabar Azare ba sai kusan magariba Dan ma Zahrar nata Masa magiyar ya tafi saboda rashin tsaro irin na kasar.
Tun daga lokacin hanya ta aure shi tsakanin kano da Azare. Mushahu na mutane ne kusan duk Wanda ya kwana ya tashi a Nan kukkuken unguwarsu Zahra yasa shi Koda kuwa ba gaisawa suke ba, wata kila ya taba yiwa wani alheri a cikin yaran gidanku Dan da gaske hannunsa a sake yake gurin Alkhairi.
Sunyi sabo sosai da jama'a a Nan har gurin malam Bukar Yana zuwa sauda dama idan ya shigo garin, wasu ma daga cikin samarin gidan malam din sunyi sabo sosai.
Lokacin da results dinsu Zahra ya fita Sam bataje ba Auncle Haisam ne yayi Mata komai Allah ya taimakeka ta fito da first class degree a akan anatomy.
Allah ya taikata da taimakon Ya Hassan aka kawota bauchi service, bayan zaman camp sukayi posting dinta Dr Sulaiman Adamu memorial college of Hygiene and Environmental health science Azare.
Ammah taji dadin hakan sosai haka shima Mushahun yaso hakan kwarai da gaske.
Zahrar najin dadin aikin sosai da sosai domin teaching Yana cikin hobbies dinta.
Bayan sun Gama ne da wata daya kamar yanda akayi Alkawari aka Fara kokarin Fara shidimar bikin ta dai dai lokacin Kuma akayiwa su Ummee rasuwa a saudiyya abinda ya Hana su zuwa kenan da har Ammah tace a daga bikin tunda rasuwar ta jikinsu ce kanin Baban Ummeen ne ya rasu,Amman sai sukace Dan me ayi idan komai ya lafa zasuzo suga daki kawaii.
A satin da za'a Fara bikin kusan Kullum Mushahu da Abokansa shakikai su Deeni da Aliyu Wanda Suke cussings suke ta zirga-zirgar ganin abubuwa sunyi yanda ake so duk wasu programs a nan za'ayi dinner ce kawai zasuyi a Kano, sun Kama dakuna uku a hotel idan zasu zauna har zuwa Daurin aure.
Saura kwana biyar Daurin auren ne wani abun al'ajabi ya faru da Hajiya Nafisa Maman Mushahu wadda suke Kira da Ammi.
Cikin dare tana barci ta farka a matukar razane saboda wani mugun mafarkin da tayi da Musbahun akan auren, addu'a tayi ta koma ta kwanta ai kamar jira ake barcin ya dauketa sai abunda ta gani a wannan mafarkin yafi wancen muni, wasa-wasa barci ya gagareta a wannan Daren kafin safe duk ta wani hargize ga wasu irin tunane tunane sun cika Mata zuciya na rashin kwanciyar hankali kafin yamma gaba daya ta Zama wata marar nutsuwa ba shiri ta Nemo kanwarta Aunty Jamila a waya Nan da Nan tazo tunda ba aure gareta ba, duk ta kwashe komai ta fada Mata akan Bata son auren Musbahun kwata kwata ita fa ko a cikin ranta ta tuna da zeyi aure ji take kamar zata zauce, da farko Aunty Jamilar ta dauki abun Wasa Amma ganin da gaske abin yake yasa ta Kira Babban yayansu Alhaji sulaiman da kanin Baban su Musbahun Alhaji isma'il, Suma da farko sunyi zaton na Wasa ne Amma da suka matsa akan ta Fadi dalilinta na Hana yuwuwar auren sai abun ya ta'azzara ya Zama kamar Mai tabin hankali, ganin abun Yana neman ya Zama wani iri ne yasa Alhaji sulaiman ya kirawo Aliyu tare da tambayar suna ina?.
Aliyun yace gasu Nan a hanya sunje Azare ne Amma har sun wuce wudil sun kusa kano ya fada Masa lallai direct su nufo sokoto road su duka.
Haka suka shigo suka tarar da wannan dambarwar ana ta fama da Ammi.
Ai tana arba da Mushahu ta Kara tuburewa tana fama fadar wallahi matukar ya kafe sai auri Zahra Bata yafe Masa nononta da yasha.
Su dai Basu ankara ba sai ganin Mushahu sukayi ya sulale ya zube a sume, da sauri Aliyu ya kawo ruwa aka zuba Masa Amma a banza ganin haka yasa suka nufi Asibitin Nasarawa dashi. Haka aka dunga juyawa da Ammi Amma ta kafe kamar kafiran farko duk Wanda ake tunanin ze kawo gyara a lamarin an fada Masa Kuma yayi bakin iyawarsa Amma ba wani ci gaba da aka nemi a Zafafa sai lamarin yaso ya koma Mata tabin hankali abinda daya tada hankalin Babarsu kenan Hajiya Yaya tace dole a hakura da auren tunda abin yazo da irin wannan lamarin marar Dadi daman tun farko ita bataso lamarin ba sai dai yaran yanzu ne baka hanasu abinda suke so, tunda Daman fa ance shine na uku a Wanda zasu auri yarinyar ana fasawa to shima gashi tun ba'aje ko Ina ba lamarin ya Zama haka.
Tashin hankali iya tashin hankali Musbahu ya shiga Dan dakyar aka Sami nutsuwarsa dan kwata kwata ya daina magana da kowa ya rufe duka wayoyinsa shima Deeni ganin kiran Zahra yasa ya rufe layin da suke wayar da ita, Aliyu ne kawai Bai rufe wayar ba Amma baya picking idan ta Kira a halin hake ne su Alhaji sulaiman sukaje Azaren da labari marar Dadi Wanda ya kawo karshen 'yar Wala walar da akeyi da Zahra akan aure ta kawo karshen duk wani makirci da bita da kulli da ake Mata na rushe aurenta idan ya taso abinda ya girgaiza duniyar Wanda suke fake suna tsula ta'addanci ta karkashin kasa.
✨
✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨
✨
MAMAN FATIMAH
Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu. Dan Allah ayi hakuri da matsalar da aka samu gurin turo page fourteen sau biyu hakan ya faru ne saboda wasu dalilai Amma na karshen Wanda na turo shine cikakken fourteen din yanzu kuma na hade fifteen & sixteen guri daya na gode.
Page
Fifteen
&
Sixteen
📖🖋️
BACK TO STORY.
________ Gurin Zahra su Sajida suka shiga tana kwance a gado idanunta a rufe tayi zurfi cikin tunanin, Sam bataji shigowar su Sajida ba Saida mujiba ta Dan zungure ta bude ido ta yunkura ta tashi zaune tana dafe kanta dake Sara Mata.
Sajida ce ta zauna kusa da ita ta Kama hannun Zahrar tana fadin "bestie Dan Allah ki rage tunani kada wani ciwon ya kamaki, ki yawaita addu'a komai yayi zafi maganinsa Allah. Kuma wani hanin ga Allah baiwa ne, ke kanki Baki taba tunanin abun ze Zama haka ba, Kuma Allah ya juya lamarin yanda yaso, to saiki gode Masa bisa ni'imar da yayi miki, Kuma nifa mujiba Ina doubting akan wannan da aka daura musu aure, Kuma ki rubuta ki aje zakice na fada Miki kije kiga gidan da za'a Kai bestie, Kuma ki duba kiga irin kayan da aka kawo yanzu kinsan duk Wanda ya hadasu first class ne a gurin gayu wallahi komai bana banza Amma Kuma Wai almajiran malam ne gaskiya I doubt much".
Ta fada tana kallon mujibar.
Ita dai Zahra ta rasa inda zata Kama komai ya kwance Mata, su damuwarsu kaya da gida, ita Kuma tata damuwar ta yanda za'ayi zaman ne, har yanzu gani take kamar a mafarki Wai wannan karon ma Saida aka samu akasi,ta rasa daga Ina matsalar take, shi kuma auren da aka daura meye ze biyo baya tasan idan ba wani nufi ba na Allah shima sai an Sami wani kalubalen a cikinsa.
A hankali ta furta "Ya Salam! Allah ka shiga cikin lamarina, wallahi bestie komai ya kwance min bani da sauran dabara,kwakwalwata ta daina aiki yanda ya kamata kinsan Allah nifa kamar ma tsoronsa nakiyi Dan tunda na Fara ganinsa naji wani irin Abu a jikina wanda ban tabaji ba a kan ko wane namiji sai shi, Kuma yayi min abinda ya kamata na dauki mataki Mai karfi amman wallahi ko magana kasayi Masa nayi, yanzu kuma a haka zan rayu dashi? Ni wallahi bana sonsa Sam Kuma fa Shima yace baya son abin yake ba kawai dai baze iya watsawa su Abba kasa a ido bane". Ta karasa fada hawaye na zubo Mata a fauska.
Lallashinta sukayi da kyar tayi shiru kafin mujiba tace "haba Zahrar ki daina kuka idan kina daga hankalin ki na Ammah ma baze kwanta ba, Kinga irin haka ba Dadi duk da an aura miki Wanda babu soyayya da shakuwa a tsaninku, ita a hakan ma yayi Mata da ace wannan karon ma an fasa aure gara hakan tunda naga alama da ita ake fadan ke