Showing 57001 words to 60000 words out of 122700 words
zaro ido waje hura kata iskar bakinsa yayi a fuskarta dalilin yasa ta rufe idonta kenan a hankali yace "Ina Zaki ki barni a zaune alhalin saboda na tayaki Zama yasa naki fita ko ina".
✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨
✨✨
💎 PAGE TWENTY 💎(20)
_______"ya Salam". Zahra ta fada a hankali jin yanda yake hura mata iskar bakinsa a fuskarta, yasa hannuwansa duka biyun ya tallabo fuskarta yana kallon face din very cute da ita, shifa baya gajiya da kallonta komai nata burgeshi yake yi Dan bakinta ya kalli 'yan kyawawan lips din ta pink, gdy yake yiwa buwayi Gagara misali daya mallaka masa ita a lokacin da bai taba zato ba, tunda ya kafeta da ido Bata yarda sun hada ido ba, ba Kuma tayi gigin dogowa ba.
Qaran da door bell din tayi shiya kawo karshen 'yar tutsiyen da yayi Mata wani soft kiss ya yiwa gefen wuyanta Wanda har Sai da ta zabura tana fadin "wayyo Allah!".
A shagwabe ta janye jikinta daga rikon da yayi mata, shi Kuma ya tashi ya nufi kofa, Bata jira taga waye ba tayi wuf ta nufi ciki jikinta kamar mazari.
Tana shiga ta zube a gado tana fitar da numfashi da sauri da sauri kamar wadda tasha gudu, jin alamun bude kofar yasa tayi saurin duba gurin Sajida ta gani tsaye ta tsura Mata ido tana Mata wani kallo cikin mutukar tsantsar farin ciki zahrar ta taso tana fadin "haba bestie kin wani tsareni da ido kina min kallon qurillah irin wannan ko Kinga wani abu a jikina ne?".
Ta qarasa fada tana karasowa kusa da ita 'yar madaidaiciyar ledar hannunta tana fadar "Wai meye Kika wani yi shiru kina kallona ne Dan Allah talk to me Mana pls".
Biyo bayan zahrar tayi har gefen gadon kafin ta samu kuzarin fadin "Bestie Kinganki kuwa just one day Amma har kin Fara canzawa, Fadi min meye sirrin gaskiya, na tafi jiya da zulumin ki a Raina yau kuma nazo na sameki haka kin wani Kara Zama fresh dake".
"Bestie tsakanin mu harda 'yar zolaya zakice Wai na Kara zama fresh?"
Zama tayi gefen zahrar tana fadin "wallahi I am serious kin canza a idona gaskiya Kinga ai dole na fada ko?".
"To shikenan kin fada bazan hanaki ba, wai da gasken yau Zaki wuce?"
Kai ta gyada Mana kafin tace "In Sha Allah meya rage kuma ai gara naje na fuskanci karatun ko tunda na samu nutsuwa kin shigo gidan ki. Alhamdulillahi, ga sauran abubuwanki na wajen Baffan rimi kici baga da amfani dasu dazuma munyi waya da safe yace na bawa Ammah abinda ya Aiko dai ya Kara jardada Mata na a fada Miki kada wani ya kawo Miki abu kici Kuma yace a tura a karbo Miki sako Nan da sati daya".
Dan langabar da Kai tayi tana Kara ganin kimar Sajida ta dauki matsalar nan tata bada wasa ba.
Godiya sosai Zahra ta yiwa Sajida akan abinda suke mata, sun Dade sajidar na yiwa Zahra nasiha akan ta rike aurenta da kyau ita bataga wani abun ashsha ba gurin Mahmud idan. Nan da Nan idon Zahra ya kawo ruwa ta shiga sharewa da hannunta tana fadar "wallahi bestie na rasa dalilin da yasa nake jin wani abu a tare dashi tun ranar Dana Fara ganin shi naji abun ko kallonsa fa nayi sai naji gabana Yana faduwa heart beat Dina Yana karuwa, kinsan ma inda matsalar take?"
Kai sajidar ta girgaiza tana fadar "sai kin fada".
"Kinsan haduwar mu ta farko rungumeni fa yayi a cikin jirjinsa tsam kamar.wata baby amman Kamar an dinke min Baki na kasa ko fada Masa magana ne saima wani azababben kwarjini da yayi min harda fadar na ringa kula kada nayi musu asara'.
Ai Sajida Bata San lokacin da wata dariya ta kubce Mata ba tana fadar.
"Babbar magana kice da wata tsumammiya a tsakani ku tun tuni har kika dauki alhakina gurin hanani kwanciyar hankali tun jiya Allah barci ma ban samu na kirki ba Ina zulumin abinda kaje yazo, Dan ba kowa bane za'a aje masa mace kamar ke ya iya kauda Kai gaskiya"
Wani duba zahrar tayi Mata tana fadin "ban Gane ba me kike nufi da maganganunki?.
Wata dariyar tayi tana fadin "A'a ba mefa nake nufi kawai dai...... "
Sai tayi shiru.
Wani zancen ta dauko Tana fadin "Zahra ki tsaya ki nutsu a gidan aurenki ki gyale kowa duk wanda ze raina Miki miji kada ki amince ko waye kuwa Koda ni da nake Miki wannan maganar, Kuma game da Hameeda ki kula sosai Dan a jiya ta nuna Miki jiya ba yau bace, jini kuma yafi ruwa kauri, Koda ta dawo tana neman Kara shiga jikin ki da wata manufar tazo, Dan Allah kiba marada kunya duk yanda ake son ganin lapses dinki kada ki bada damar hakan".
In Sha Allah zan kula nagode Bestie Allah yabar zumunci. Zahra ta fada
"Ameen" sajidar na ta fada, suna cikin hira akayi knocking din kofar ba'a bude ba Zahra ce Mike tana fadin "ina zuwa, tana kokarin yafa gyale ta rufe gashinta Sajida ta warce ta aje gefen ta tana fadin "haba ke kamar matar liman a daki na da Bata ja ba tayi gaba saboda an Kara buga kofar, budewa tayi Mahmud ta gani Yana tsaye ya canza kaya ya saka Riga da wando na wani yadi light brown dinkin buda yana baza kanshi sa na ibada.
Matsawa tayi daga jikin kyauren ganin alamar shigowa zeyi Amma fa Saida yadan shafi fuskarta kadan sannan ya ida ahigewa ciki, tsaye tayi tana binsa da ido tana ayyana "Wai meye ne yake faman shafa mata fuska har a gaban mutane ko kunya bayaji tasan wlh sarai Sajida ta gani sai dai ta basar kawai gashi ta wani rike mata gyale ta wani barta tsurarta".
Direct gurin mirror ya nufa ya zauna a Kan stool, Yana fadin "Bestien mu zuwa nayi muyi sallama naji Abdul Hakeem yana maganar Zaki wuce yau ko".
Ya fada Yana murmushi, itama murmushin tayi masa tana fadar.
",In Sha Allah yau sai kano tunda Allah ya cika min burina Zahra ta shigo gidanta fine".
"To mun gode kwarai Allah ya saka da Alkhairi sai munzo visiting idan madam zata dauki nauyin zuwan mu Kinga Nima sai Naga duniya ko madam?" Ya zubawa Zahra narkakkun idanunsa Yana Mata wani kallon qasa qasa.
Shiru Zahra tayi tana yafa gyaren a kanta, Sajida ce tace "gaskiya Kam haka za'ayi".
Tashi yayi ya Dan tako kadan zuwa gaban Zahra kamar ze hadeta da jikinsa da sauri tayi baya tana turo Baki yi yayi kamar Bai gani ba, envelope ya Mika mata Yana fadin ki Bata sskonta ne na jiya data Bari nayi niyya bazan canza ba sai dai idan bataso ta bayar, nizan shiga gurin su malam".
A hankali tace "an gode madallah a dawo lfy".
"Amin to bestie sai munzo ko".
Bai jira abinda zata ce ba yayi ficewarsa.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana Zama kusa da Sajida Mika Mata envelope din tayi tana fadin "yaushe ya Baki kikace bakya so?".
"Jiya Mana lokacin da zamu tafi sanda wannan jikar marokan ta zubar da darajarta ta rokeshi, yanzu Dan Allah me Hameeda ke nema? wane irin rufin asiri ne Allah Bai mata ba. Amma ta lalace gurin roko? shi yasa na aje masa kudin sa nayi gaba kayan ma nace bana so su rike".
Dan murmushi Zahra tayi tana fadin "Saji danger wato halin na Nan ko? To nidai gashi nan tunda a gaban ki ya bayar saiki karba".
"Bude mu gani to"
Sajidar ta fada.
Stalling founds ne na ingila musu yawa a ciki kallon kallo sukayiwa juna kafin Sajida tace wallahi bestie akwai kukus a shinkafa zakice na fada Miki, Wai kuwa kin tsaya kin Kare guyn nan kallo kuwa?". Kinga ya Miki Kama da Wanda baida abinyi ko wanda ya tashi a cikin rashin wadataccen ilimi da mugu? Dubi muhallin daya ajeki, ance malam ya bashi gidan sai kungiyar da yakewa aiki sukayi renovation din gidan ki kiyasta nawa yaci gurin aikin kinsan da an kashe abinda yafi kudin ginin duk yi Masa akayi? Ki tuna Nan fa ba garinsu bane ance bako ne kuma yaki fadin garinsu anyi magana ance yace ya manta komai sai a hankali idan ya tuna hankali ze yarda da hakan? Kuma kina tunanin Abba ze daukeki ya bashi ba tare da yasan wani Abu a tare dashi ba? Kiyi nazarin abin Mana ni dai ina fada Miki kibi komai a hankali kuma yanda na fashimci wani Abu a maganar da Kika fada min kinfa kamu da son guyn Nan tun sanda kuka hadu ba tare da kin sani ba, Kuma Shima Naga yanda yake shige Miki ko kunya ta Bai jiba kinsan sai a hankali kawai kwanan Nan labarin ze sauya irinsu basayi da wasa fa".
Ta garasa fada tana dariya kasa-kasa.
Suna cikin tattaunawa Kira ya shigo wayar sajida "Ya Abdul Hakeem ne" ta fadawa Zahra kafin ta daga.
"To"
Kawai tace ta kashe Kiran tana fadin.
"To bestie ya Abdul Hakeem Yana jirana Wai a she shine ze Kaini nifa daya fada na dauka da Wasa yake lokacin da Ammah tace Magaji ko Malam Bala dureba zasu kaini sai kawai yace su Bari Shima Yana son yaje kanon Sai ya tafi Dani".
Dariya Zahra tayi tana fadin "idan tayi wari munji batun, yanzu ba fa Naga Ya Abdul Hakeem Yana dama dama dake ba bai fada min ba Amma zakice na fada Miki Ina ga target dinsa kenan yau yake son ya yad'a manufarsa shi yasa yayi Riga malam masallaci yace Wai daman kanon zaya".
Kin magana sajidar tayi sai murmushi kawai. Zahra tace "bestie ko dai komai ma ya kankama ne ban sani ba Ina shirme?".
Kafin sajidar ta Bata amsa wani Kiran ya shigo da sauri ta dauki jakarta tana fadin "To bestie sai gani na gaba Allah ya bada zaman lafiya ya kade fitina, sai anyi ta hakuri kafin komai ya dai daita ki kwantar da hankalin ki zakiji dadin Zama dashi in Sha Allah".
Har gate ta rakata babbar ledar dake hannunta ta Mika mata tana Mata addu'ar sauka lfy. Amsa tayi tana Mata godiya ta bude gate din ta fita, ya Abdul Hakeem Zahra ta gani a mota a zaune cikin mamaki tace.
"Ya Abdul Hakeem daman kana Nan waje Amma baka shigo ba?".
Fitowa yayi ya karaso gurinsu Zahrar ta gaishe shi, sannan ta juya ta koma ciki duk zuciyarta ba Dadi Kamar ta Hana sajidar tafiya amma ba hali.
*********
Mahmud Yana fitowa direct Famfon shanu ya nufa tunda lifan din Habib a gurinsa ya kwana, tun jiya daya karba da yamma Bai koma unguwar ba.
Lokacin daya karasa yayi arba da motar Sameer wani murmushi yayi Yana fadin. "magulmaci kawai".
Kafin ya shiga Saida suka dinga gaisawa da jama'a anata Allah sanya Alkhairi, Binya ya tambaya Ina Habib yace yaje Kai wani sako da malam ya tura shi ya Kai gidan sarki.
Gurin Malam din ya shiga shi dasu Sameer ya samu suna magana da malam din Yana shigowa da sallama mlm din yace.
"Yauwa Dan halak yanzu nake cewa bazaka jima ba zaka shigo, mutanen ku ne sukazo da wasu ayyuka gasu nan dai zasuyi maka bayani. Ya wajen iyalin naka!?"
Dan sosa kansa yayi Yana Dan sadda shi qasa yace "Lafiya kalau tace a gaisheka" .
"Masha Allah. Allah yayi Albarka"
Gurin su Sameer ya juya suka gaisa, kafin suka fita zuwa inda suke meeting.
Stepdown training zasuyi da school base management committee Basu tunda tsarinsu ya koma sun bin tsarin makarantun government ne sai kuma officially da suka gayyaci Mahmud zuwa gurin taron da zasuyi a Lagos nan da kwanaki biyar masu zuwa. Bayan Gama taron Sameer ya dauki Mahmud a mota suka fita hotel din suka nufa a hanya Sameer ya kalli Mahmud Yana fadin "yallabai meye labari naga text dinka komai an sawo zuwa anjima motar zata karaso amma sai nake ganin kamar kayi tafiyar nan da ita tunda zaka jima a can Kuma kaga duka kwanan ta nawa zaka tafin baka ganin abin ze iya Zama na surutu ko ace ma guduwa kayi amma dai ya kake gani?".
Dan Jim yayi kafin yace.
Tafiya da ita ba shine solution ba na dauketa na kaita Ina ko Kuma nace Mata wanene ni Nan nace Lagos zani can Kuma taga sabanin hakan ya kake tunani ka tuna fa she's educated, zatayi saurin gane komai ni kuma nafi son na Gina soyayya ta a zuciyarta ba tare da tasan who I am ba, I hope you understand?".
Kai ya gyada Masa alamar eh.
Sun Dade suna tsaya yanda program din ze kasance da abinda za'a batar da abinda za'a kashe a makarantar zuwa lokacin da zasu dawo suna cikin aikin direban daya dauko kayan ya Kira Sameer ya fada Masa ya shigo Azaren ya fada Masa inda yake tattara komai sukayi suka wuce gurin da direban yake, Sameer din ne ya shiga gaba direban na binsa a baya har zuwa gidan Mahmud din.
Mai gadi ya taya direban sauke kayan, kayan abinci ne da sauran tarkacen girki hatta nama da kifi daga can aka kawo kayane masu matukar yawa.
Ciki Mahmud din ya shiga tararwa ya yi tayi Baki har su zulai da sahura, a tsaitsaye suka gaisa yayi gaba zuwa bedroom dinsa.
Ganin idon su zilan yasa zahra mikewa tabi bayansa dai dai lokacin Kuma Yara suka Fara shigon kayan masarufin da aka kawo, ganin zahrar Bata Nan yasa su sahura shiga dasu store din kayan abincin suka hada da wanda Abba yasa suka kawo dazu da kayan gara su gireba dasu dublan da alkaki.
Sunyi mamakin yanda yara ke shigo da kayan abincin basu Kara Shan mamaki ba Saida aka Fara shigo dasu Nama da kifi ga drinks Nan ko ba'a fada ba Wai ance ido ba mudu ba amma yasan kima sun San kayan na manyan kudi ne, ko wacce da magana a bakinta Amma bata furta ba.
Zahrar na shiga corridorn ta waske zuwa nata dakin.
✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨
✨✨
💎 PAGE TWENTY ONE 💎 (21)
...............…... Sai da su zulai suka gyara Mata komai yanda ya kamata sannan suka gyara parlourn,lokacin da Mahmud ya fito bedroom dinta ya nufa baiyi wani knocking ba ya tura kofar a gaban gado ya ganta ta cire bedsheet din ta zubo da pillows din da alama wani Abu take nema sallama yayi mata cikin muryarsa Mai nutsuwa yana kallon ta, cikin takunsa na cikakken namiji ya karaso Yana tambayarta "lfy me kike nema ne haka Kika birkita gurin haka?".
Jiki sanyaye tace Masa "wayata nake nema tun safe banganta".
Dan matsowa yayi kamar ze tayata dubawar Yana fadin "Kuma tun safe Baki ganta ba Kuma Baki nema ba sai yanzu, to su waye suka shigo dakin ne?".
"Shiru tayi kawai tunda tasan daga ita sai sajida ne a dakin Kuma tun bayan tafiyar ta ko Baki ne 'yan ganin daki Bata ahigo dasu Nan Dan gani take yaushe za'a dinga shigo da jama'a har dakin barcin mutum su dai dayan tunda ba a ciki take ba.
Dagowa tayi ta Dan kalli gefen shi da gani wanka yayi ya canza kananun Kaya tana mamakin sa ita tunda take ganinsa Bata taba ganinsa da shiga irin wannan ba Kullum manyan kaya ne Amma daga jiya zuwa yau ya zamar Mata wani daban, Sam ba wancen bane take gani.
Kamar ze wuce ta bayanta sai Jin Hannun Mutum tayi ya zagayo ta cikinta ya manna bayanta a kirjinsa ya kwanto da kansa dai dai saitin kunnenta iska yadan hura Mata kadan tare da hucin numfashinsa kafin yace.
"Ki daina wahalar da kanki tana gurina tun safe na dauka, nayi mamakin da baki nemeta ba sai yanzu? Na cire sim din saboda Naga wani sakarai ya kiraki da number din to nasan ze iya bibiyarki tunda naga bashi da taushidi ko kankani Bai hakura ba da hukuncin Allah so yake da karfi saiya kwato abinda ya kubce masa".
Kasa ko kwakwkwaran motsi tayi sanda yake jero Mata maganganun. Amma jin ya Kira Musbahu da sakarai marar taushidi yasa taji Zuciyarta ta wani baci, idan beji tausayinsa na abinda ya faru ba ai baze Masa bita da kullin irin wannan maganar ba, shida ya tsunci dami a kala har ya samu bakin magana irin haka. Nan da Nan taji ta samu wani courage wanda Bata San tana da shi ba, cikin muna bacin rai ta fara kokowar raba jikinta da nasa tana fadin.
"Wallahi Musbahu ba sakarai bane, ba Kuma marar tauhidi bane,dan ya biyo abinda yake halalinsa amma kasan dai Banda qaddara ba abinda ze rabani dashi, dashi muka tsara planning na rayuwarmu Amma lokaci daya ka rusa Mana budget din mu ka yarda da aurena da aka baka Kuma wallahi tunda nake dashi bai ko taba rike ko hannuna ba, amma Kai kuwa fa ranar Dana fara ganinka a duniya dame ka Fara min bada rugumata ba?" Kai kenan baka da aikin yi sai tabawa mutane jiki ......
Bata karasa fadar abinda tayi niyya ba taji ya hade bakinsa da nata cikin zafin nama Yana ladabtar da bakin nata da harshensa, dayan hannun Kuma yayi Mata wani irin riko bana Wasa ba dayan Kuma yana yawo dashi a ilahirin jikinta cikin wani irin sarrafawa Mai zafi.
Wata irin tsuma jikinta ya kama ga hawaye kamar na lalataccen famfo sai zuba suke ba bakin kuka sai mutsu mutsu take Amma ko a jikinsa wajen sau uku ana Kiran wayarsa tana tsinkewa, yayi biris da Kiran Kumar baya ji, sai da ya tabbatar da ya ladabtar da ita yanda yake so ya saketa, kan bed ta fada tana shashhshekar kuka hannunta daya yana Kan lebenta dake Mata zafi haka ma kirjinta zafi yake Mata ga gaban rigar ya farke Mata ita.
Kafarsa daya ya doro Kan gadon dayar tana kasa ya Fara fadar maganarsa hankali kwance kamar bashi bane ya Gama yamutsa Mata jam'iyya yanzu ba cikin mugunta.
"Wallahi na Kara Jin wannan sunan a bakinki ko magana makamanciyar irinta saina shayar dake ruwan mamakina, an fada Miki ni lusari ne da har Zaki tasani gaba kina fada min rubbish ne? an