Showing 15001 words to 18000 words out of 122700 words
Sajida suka nufi Hayin bankin cikin jagorancin Habib, lokacin Inna Bata Nan taje MIYA gurin wata aminiyar ta da sukayi aikin Haji shekara daya.
Duk cikinsu ba wadda Bata kadu da ganin gidan ba domin ba karaya an narka mahaukatan kudi a gidan bazaka tab'a cewa renovation akayi Masa ba, bedroom's ne guda uku biyu suna kallon juna dayan Kuma daga gefe da alama yafi sauran girma Kuma shi kadai ne a rufe, sun zagaya ko Ina sai santin gidan Sajida tace tana ta daukar video, falon kadai abin kallo ne duk da ba komai a cikinsa sai fitilu da aka kunna sai Kuma AC da aka ware.
Hajiya mama ce ta kasa hakuri ta leka ta Kira Habib Nan falon ya shigo Yana fadin "gani Mama"
Yana Dan rankwafawa.
Aunty Hasana mama ta kalla "Hasana Dan Allah ki tayani tambayar yaron Nan tunda shi namu ne na gida baze cucemu ba, Wai wannan yaron sana'ar me yake daya iya Kama hayar wannan uban gidan"?"
Kara risinawa yayi Yana fadar "ba haya ya Kama ba Baba malam ne ya bashi kyauta, sai Kuma kungiyar yake yiwa aiki suka kawo masu aiki suka yiwa gidan 'yan gyare -gyare harda kayan daki ma suka zuba masa, Bismillah Bari na bude muku ku gani yanzu ba dadewa zuka Gama hadawa da kitchen din suka tafi".
Dakin ya bude musu ba Hajiya mama da take ta kwana biyu ba, ko Aunty Hasana da Sajida Saida suka Zama 'yan kauye Dan tunda suke Basu taba ganin irin wanna gadon a zahiri ba, ita kanta aunty Hasana lamarin Yana neman ya gagari tunaninta fa ance Almajirin Baba malam to Amma idan aka saka mizanin hankali abin yafi karfin yanda aka fada to wane irin NGO's ne da suke irin wannan aikin akan daidaikun ma'aikatan su haka?" Gaskiya abin akwai abin dubawa.
Lokacin da suka fito harabar gidan ne wata Hilux ta shigo da kaya a bayan motar mutane uku ne a motar bakar fata biyu fari daya Kamar balarabe Kamar kwara.
Kameme Hajiya mama ta hanasu tafiya sai da aka sauke kayan ta gani abinda da suka Gane irin katuwar plasima din Nan Mai cin Rabin bangon Nan ne kawai amman sauran tarkacen Basu Gane komai ba, haka suka kada suka tafi mama nata mitar "A'a da sake Alhaji ya titsiya yaron Nan saiya nuna Iyayen shi kafin a Kai Masa yarinyar Nan haka kawai aje ayi kitso da kwarkawata mutanen yanzu ba abin yarda bane sai kaga mutum har mutum Amman a Baki malam a ciki Kuma Fir'auna".
Maganar data Basu Aunty dariya kenan.
πβ€οΈ
πβ€οΈ
πβ€οΈ
AUREN HUCE HAUSHI
πβ€οΈ
πβ€οΈ
πβ€οΈ
STORY
AND
. WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE EIGHT
Lokacin da suka shigo gidan ana ta kokarin daura alwalar sallar magariba.
Sai bayan sallar insha'i ne Mama ta shigo dakin Ammah suka hadu da Aunty Hasana suna fadawa Ammah yanda suka gano gidan da Kuma yanda abin ya daure musu kai.
Nisawa Ammar tayi tana fadar "Mama ki Sami Abban kiyi Masa bayani yanda ze fahimta kinsan yanda suke da malam bana tunanin wannan abun ze saka ya canza ra'ayinsa duba da yanda ya yanke hukuncinsa Bai nemi shawarar kowa ba".
"Aiko dai ya kamata ayi wani Abu gaskiya Nima lamarin ya tsaya mini a cikin zuciya".
Aunty Hasana ta fada.
Sun jima suna tattaunawar kafin Mama ta koma daki tabar Autty Hasanar da Ammah.
Zama Aunty Hasanar ta kyara ta fuskanci Ammar ta Kira sunanta "Anya wannan Mahmud din ba abinda yake boyewa kuwa Ammah Kinga gidan kuwa ga wannan uwar wayar daya canza Mata kinsan kudinta kuwa ? gaskiya I doubt much, ni dai kiyiwa Abban magana da kanki Kamar zefi daukar abun serious akan na Mama".
Can Kuma sajida ce tasa Zahra a gaba tana ta faman zuba.
"Innalillahi! Kinga gidanki kuwa? Allah ya bamu ya taku wallahi Zahra ki godewa Allah. Wallahi Allah ya Gama miki duk wata ni'ima ta ko Ina kinyi gaban da Nan kurkusa dai kafin a fiki za'a Dade ana lalube. Zahra Naga mijinki har mun gaisa ada Ina adawa da auren Amma tunda na ganshi Naga Yana yinsa nasan yanzu ne kikayi aure da mijin daya Dace ke.Kawai dai matsalar za'ace ba Mai kudi bane,amma a yanda gidan da zaya ajeki yake wallahi ko minister ne sai hakan, akwai abinda na gani a gidanki wallahi ban taba gani a gidanki kowa ba duk yawona sai dai a film amma dai a zahiri A'a ban taba gani ba Allah Bai kaini gurin ba".
Tunda ta Fara zuba Zahrar ke bin sajida da idon lokaci daya duk ta wani rude sai zuba take Kamar 'ya 'yan kanya.
"Kin Gama?"
zahrar ta tambayi sajidar.
"Eh na Gama aini an ma yanka ta tashi na fasa tafiyar zanyi waya da Mom taje can Rimin sumailar gurin Baffan kawai, tunda Daman zatazo nan din ba suna kwantagora".
"Ke Kika sani dai tunda Naga kina nema ki Zama wata daban ko dai an canza min ke da wata ne ko Kuma wani abun ya fada Miki ya goge Miki hadda ne?".
"Eh da alama Kam Dan ya fiki iya lafazi gaskiya inaga na Zama 'yar team dinsa fa tunda Naga ke Baki da wayo".
Ta fada tana dariya.
Washe gari tun safe Abba yasa aka Kai furniture's din Zahra gidan Daman Aunty Hasana sunyi magana da Wanda zasu hada musu kayan, kayan kitchen da sauran kayayyakin duk suna gidan Aunty Hasana daga can aka ringa daukowa, masu aikin su suka hada komai na gidan hatta kitchen su suka gyara komai, gidan ba karamin kyau yayi ba, ba karya duk Wanda yaga gidan yasan na 'yar gata ne.Dan wasu irin mahaukatan Turkish furniture's ne wanda kakanninta ta gurin uwa sukayi Mata duk wani abun more rayuwa akwai shi a gidan Nan, bangaren electronics ma sai a cikin lockers aka zuba wasu, komai yayi.
Lokacin da aka Gama gyaran Aunty Hasana da sajida ne sukazo gani ba karamin burgesu gidan yayi ba Dan sai yanzu ne ya fito a asalinsa na kyau da kayatar da Mai gani, komai na gidan unique ne Masha Allah.
A waya sajida ta daukowa Ammah komai. Ita kanta Ammah Kai Kawai take jinjinawa Dan ba karamin burgeta abin yayi ba, sai dai can kasan ranta rudani ne kala-kala domin abin ne duk yazo a hagunce.
Tana tsoron lamarin sosai sai da har abada baza iya jayayya da Alhajin ba Dan da gaske ubane tsayayye Wanda baya nuna banbanci tsakanin abinda ya Haifa da Wanda yake bashi ya Haifa ba, amma harga Allah tana zulumin wannan AUREN HUCE HAUSHIN da Alhajin yayiwa 'yar marainiyar Allah, mazan yanzu sunce suna sonka ma ya kukan kare idan Zama yayi Zama ballantana matar cushe ta San komai Daren dadewa ranar da yaga irin matar da yake so Sai dai zahra tayi hakurin zama Kawai, duk da tasan Bata da haufi akan yarinyar Tata Dan macece har mace abin alfaharin kowa ne namiji ace ya mallaki Kamar ta, to Amma shi lamarin so daban yake duk kyan mutum da asalinsa ba lallai ne ace yana burge kowa ba domin shi dai so makaho ne.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali duk jikinta yayi Mata wani irin Sanya ta kalli Aunty Hasana tace "Hasana Ina jin wani irin rauni a zuciya ta game da lamarin nan Ina tausayin yarinyar nan rayuwa tana ta walagigi da ita sai nake ganin Kamar laifi nane Dana kafe a barmin yarinyar Nan na hana kakanninta ita ni Kuma nayi sakacin da aka maida rayuwar ta Kamar kwallo ana ta dokata daga Nan zuwa nan".
Ta karasa maganar hawaye na zubo mata.
Abinda tunda Allah ya kawo Aunty Hasana duniya Bata taba gani ba a zahiri gurin Ammah Nan da Nan hankalinta ya tashi sajida ma kukan ta Fara duk da batasas takamaimai man abinda ya saka Ammah kukan ba, tashi tayi ta fice daga dakin jin an Fara Kiran sallar magariba.
Aunty Hasana ce tace "Haba Ammah duk yanda Kika jure bakin cikin baya na abubuwan da suka faru Baki taba zubar da hawaye ba sai yanzu da Allah ya nufa akayi ai godiya Zaki yiwa Allah daya kawo karshen wahalar ba kuka ba".
Gefen zani tasa tana goge hawayen.
"Hasana Ina hango abinda ke bakya hangowa ne,masu iya magana suna cewa matar shige Bata daraja ba irin wannan rayuwar na sowa Zahra ba to sai dai kana naka Allah Yana nasa Kuma nasan ne gaskiya. Ba komai haka Allah ya tsara komai mukaddari ne daga gare shi, naji Alhaji Yana maganar zuwa juma'a za'a kaita".
*******Tun bayan kammala karatunsu na bayan insha'i da suke na littafin iziyya yake zaune a kusa da Baba malam har kowa ya watse ya rage saura su biyu tunda malam yaga haka yasan da magana a bakin Mahmud ne.
"Ya ya akayi ne Mahmuda?"
Malam ya jefo Masa tambayar, Kara dukar da Kai yayi kafin yace "Daman maganar kayan lefe ne dazu Oga Sameer ya kirani yace ya hado tasa gudunmawar kenan, shine nace Bari na fada maka Dan kasan da zuwansu".
"Ikon Allah shi wannan yaron baya gajiya ne Kamar baisan ciwon nema ba tunda yazo ya riski maganar Nan yake Yi kan jiki kan karfi. Allah ya saka Masa da Alkhairi yabar muku zumunci".
"Ameen" ya amsa.
Harya Mike ze tafi sai malam din ya dakatar dashi, dawowa yayi zauna.
Gyaran murya malam din yafa kafin ta jefo Masa tambayar.
"Sai zuwa yaushe ne kake ganin zamuje ga mahaifan naka kaga dole muje musu tunda wannan lamarin ya faru".
Kai ya sadda kasa Yana fadin "zamuje in Sha Allah Amma Dan Allah a Kara min lokaci da kaina zanyi maganar ayi hakuri".
"To ba laifi Allah ya iya Mana kaje ka Samu su Habibu kuje acan gidan ku kwana kaga sun zuba dukiyar kasan yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba".
"To in Sha Allah za'ayi hakan amma ni Ina Nan sai dai su Habib din suje".
"To ai hakan ma yayi Allah yayi Albarka".
Saida ya dudduba dakunan yaran ya tabbatar da komai lafiya lokacin sha biyu ta wuce, dakinsu ya nufa wanka yayi ya saka kayan barci sannan ya hau gado ya bude laptop dinsa. Email dinsa ya shiga Yana duba sakknnin daya samu sakon daya shigo ne ya dauki hankalinsa.
"Ya Salam!".
Abinda ya iya ambata kenan sai Kuma sautin daddad'an ringtone dinsa ya karade dakin.
"Sameer!" Ya fada a hankali yasan za'ayi haka, ya haga wayar Yana fadin "Ta Yaya hakan ya faru?"
Daga can bangaren Sameer din yadan furzar huci Mai zafi Yana fadar "wallahi nayi duk yanda zanyi Amma abun yaki yuwuwa dole ka daura ka kawar da komai muje gaskiya Dan kasan tunda akaje Nan zuwan nake ne Kawai mafita".
"Amman ai kasan halin da ake ciki so kake ace na gudu nabar 'yar mutane Eyeh?".
"Cool down Mana my man abin Bai Kai nan ba aikin daine ya taso na gaggawa Kuma dole sai da Kai za'ayi Dan haka suyi hakuri su aje maka ita zuwa sanda ka dawo ko Kuma ka dauko abarka ku tafi, kaga ai tafiyar tafi yi maka armashi ko?"
Ya fada cikin zolaya.
"Dan Allah ka Zama serious mana, kayi duk abinda ya kamata a Nan goben ka hakura da zuwan ka turo wannan friend din naka tunda yasan gurin ya kawo kayan kawai, Kai Kuma ka Kira Baba malam ka fada Masa daga can sun nemi ganin wakilansu na kasa da jahoshi da kananan hukumomi nasan dai kome ake ciki baze wuce kwana buying zuwa uku ba kaga lokacin na tare a gidana nafi son na barta a Nan gidana akan na tafi Bata tare ba".
"Ko dai.......?"
Sameer ya fada Yana dariya.
"Allah ya shiryeka ko dai me? kasan ni salihn ne ba ruwana da wannan sabgar sai ku".
Kit ya kashe wayar sannan yayi switch off dinta.
Misalin karfe Sha biyun Rana wata tamfatsetsiyar mota Parker a kofar gidan malam.
Akwatuna Yara suka dunga saukewa suna shiga falon malam saida suka Gama sannan baki nufi falon malam din bisa jagorancin Habib sun gaisa sosai da malam suka gabatar Masa da kayan daga Sameer.
Malam yayi godiya ya saka Albarka ba adadi.
Falon malam ya bar musu sukaci abinci suka huta sannan Habib ya rakasu can gidan suka gaisa da Mahmud din.
Sai bayan Azahar suka tafi malam yayi musu Sha Tara ta arziki.
Kayan malam yace suje su duba su gani saboda da an jima za'a Mika musu can gidan Alhajin.
Kaya ne na gani na fada an zubasu Kamar ba gobe, an shigarwa da iya Abu ciki ta gani malam yace ta turawa makotanta na kusa suzo su gani anjima za'a Mika musu.
Bayan fitowa daga sallar la'asar ne Malam Bukar ya fadawa Alhaji yanzu su malam Mudi da Alaramma malam Haruna zasu kawo kayan Zahara'u.
Fada Alhajin yayi akan kayan da za'a kawo Yana fadar "Haba malam Dan me za'ayi min haka ko wancen da aka fasa auren Kai sheda ne ban karbi lefe ba da suka matsa cewa nayi suje da kayan idan tazo saiya ba matarsa".
Kai malam yanjinjina Yana fadin "Anyi hakan Kam amma wannan shima bamu muka hada ba wannan yaron Sameeru ne ya turo dasu dazu yace gudunmawarsa ce aba Amarya"
"Ikon Allah shi baya gajiya da dawainya haka daga wannan sai wance Allah ya saka da Alkhairi ya bar.zumunci na jima banga yaro mai karqmcinsa ba abin duniya Bai rufe Masa ido ba".
Da yamma su sajida suna zaune suna Shira ita da Zahra da wata kawar Zahra Mujiba Nan take makotansu suna dasawa da Zahra sosai sun Kuma yi sabo sosai da Sajida tun lokacin da sake zuwa hutu da Sajidar lokacin suna makaranta.
Ba zato ba tsammani Yara suka shigo da manyan jakunkuna dasu cylinder din gas, ai Zahra na ganin haka ta tashi da sauri ta nufi hanyar shigowa gidan da gudu ta karasa Kamar karamar yarinya suka rungume juna da Hameeda Kamar zasu fadi. Suna rike da hannun suka shigo ciki su Mujiba suna ta faman yi Mata sannu da zuwa, sai daga baya Salma ta shigo tana wani shankanshi Bata kula su Zahra ba Suma ba Wanda ya kula ta, directly dakin Mama ta nufa.
Kamar jira ake Salma ta wuce saiga su Magaji da manyan Akwatunan lefe suna shigowa da sauri Zilai Mai aiki ta warto Babbar tabarma ta baza tana rabsa guda tana fadin "Masha Allah! Alherin Allah ya sauka. Fara Mai farar aniya sukari bakai farin banza Fatima Zahara'u 'yar Muhammadu sani, jikar hardon fulanin Mubi, Amarya gidan Mahmud Kuma uwar gidansa Alherin Allah ya Kai Miki, Mama!Ammah ku fito ga abin arziki ya sauka". Har rige-rigen fitowa a key tsakanin Mama da Salma yayin daga dakin Ammah Inna maimuna ta fito.
πβ€οΈ
πβ€οΈ
AUREN HUCE HAUSHIN
πβ€οΈ
πβ€οΈ
WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE NINEπ·(9)
____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"
Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda kin koma roko".
Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanzaro a bene" .
Ta Kara kwarara wata gudar.
Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga karamar Arziki"
Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke fama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne.
Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.
Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin zamane Allah ya hada arzikinsau.
Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin.
Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.
Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra.
Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana ba.
Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki".
Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.
"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"
Tana Gama fada