Showing 81001 words to 84000 words out of 122700 words
ganeki bane sai da Kika fada min sunan ki wlh nice na Kira bansan yanda akayi banyi saving number din ba matar oga Mahmud ko?"
"Eh nice ke wacece?"
"Sunana Fateeha matar Sameer Babban yaron oga jiya ne ya bani number yace na kiraki na gaisheka nayi Miki Allah Sanya Alkhairi sai Kuma ba'a daga ba, an Sha sauga bamuzo mukaga daki ba gashi har sun wuce China, amma in sha Allah idan suka dawo zamuzo indai ban haihu ba har lokacin"
"Nagode kwarai da gaske,Amma naji kince China ba UK zasu Fara Zuwa ba? To can din zasu tunda kune masu tafiyar Amma na dauka da China zasu Fara tunda canne aka samu matsala sai Kuma Dubai, kinsan ogan naki ne kamar computer yake baya gajiya da aiki danma yayi wannan hutun Mai yawa sai Habibi ne yake wasu ayyukan".
"Hakane kam aiya huta yanzu sai a Dora daga inda aka tsaya".
"Ai gaskiya samun kamar oga Mahmud sai an tona".
Basu jima ba sukayi sallama. Ta Dade a zaune tana jujjuya hirar su da matar Sameer, zamewa tayi ta kwanta tana duban sama a hankali ta furta. "Ubangji ga baiwar Mai rauni ka jibinci lamarina Kasan ko waye ka hadani dashi ka Kuma sakamin nutsu a tare dashi ban tabaji bana sonsa ba Amma lamarinsa Yana bani tsora na rasa alkiblar daya duba, Allah ka Zama gata na ka jibinci dukkan lamurana Dan Isar Manzon Allah s .a.w.w.
Tashi tayi ta fita dakin nasa ta koma dauko tray din da Takai Masa break fast, duk wani Abu daya danganci kayan electronic sai ta kashe sannan ta fito tana gangarowa daga steps din corridor ne taji door bell din tana Kara alamar anyi Baki, a Kan dining table ta aje kayan ta gyara gyalenta ta nufi kofar.
Budewa tayi sai sukayi arba da zilai Mai aiki da 'yar jakar kayanta.
Cikin farin ciki Zahra ta karbi jikar kayan tana fadin "sannu da zuwa anti zilai"..
Suka shige ciki murnar Zahra taki boyuwa itama zilan ba Karamin murna tayi ba lokacin da Ammah ta fada Mata zata zo ta Taya Zahrar Zama. Nan suka shantake suna Hira har Kusan karfe dayan Rana kafin Zahra ta raka zilai dayan dakin da ba cikinsa take ba ta aje kayan ta.
Tambayar Zahra zilan tayi me zata dafa musu,
"Ki dafa komai na ni harna manta wlh ashe ko break banyi ba, ga sandwich can ki dauka kada ya lalace, Zan shiga na Dan kwanta kafin karfe biyu"
"To Allah kaimu" zahra tace "Amin"harta fara tafiya zilan Kira sunan ta tsayawa tayi har zilan ta karaso.
"Uwar dakina Naga kamar wani mutum mun gaisa dashi ko Mai gadi kuka canza". ,"Eh Mai gidan ne ya canza shi wlh jiya lfy muka fita Amma yau muna dawowa ya sallame shi, wani ya Kira ya zauna Dani kafin ya dawo.
"Wani Kuma daga Ina,?. "Nima ban san daga Ina yazo ba" Tab Allah kyauta ya kamata asan asalinsa gaskiya zamanin ne yazo da wata irin rayuwa sai godiyar Allah".
"Wannan gaskiya ne". zahrar ta fad'a. Ita nufi bed room ita kuma zilan tana nufar kitchen.
✨✨✨
✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI.
Story
&
Written
By
Maman Fateemah.
This page is deducte to the Family of late Alhaji Isah Musa bakin kasuwa kazaure.
Innalilllahi wa Inna ilaihi raji'un! Ina Mika sakon jaje da ta'aziyya ga jama'ar garin MAJIA TAURA LG bisa ibtila'in daya samesu na gobara Mai Muni sakamakon faduwar tankar man petrol, Wanda yayi sanadiyyar rasa daruruwan rayuka Allah ya jikan wadanda suka rasu,wadanda Kuma suke gadajen Asibiti Allah ya tashi kafadunsu ya Basu lafiya yasa ya zamar musu kaffara ya kiyaye faruwar haka a gaba dan darajar manzon Allah s.a.w.w
Page 30
_______Misalin karfe daya da rabi Mai a dai daita sahu ya sauke Asabe a bakin gate din gidan Zahra Dan yauma Saida taje can kauyen jama'are gurin wani mutum da wata kawarta ta tab'a fada mata shi, Nan ma ta karbo abubuwa Wanda za'a binna a gidan Wanda har abada Mahmud baze kara waiwayo garin Azare ba ko sunan jihar Bauchi ma Sai yaji ya tsane shi.
Cikin karfin gwiwa ta karaso bayan ta sallami Mai Dan sahun tunda tasan Mai gadin Dan hannu ne dubu biyu ta Isa tasa yayi musu kowa ne irin aiki ne, iyakar ta tace masa na tsarin gida ne ze binna Mata saboda yau da gobe.
Knocking tayi da Dan karfi tana mazurai ita ga uwar matar gida. Cikin takunsa na kakkarfa ya bude kofar gate Dan da hanzari tayi baya Dan ji yayi Kamar ze bangaje ta, kallo daya yayi Mata ya gane face din Dan hoton da oga ya nuna Masa yafi bada mahimmanci akanta Dan ita ce suspect dinsa ta farko, yasan da ita za'a yi amfani gurin isar da ko wane irin sako ne.
Da hargagi Zayyan ya tunkaro ta.
"Wa kike nema?"
Duk daburcewa tayi nan da Nan jikinta ya dauki rawa.
A'a Daman gurin matar gidan nazo munzo jiya ne basa Nan shine na dawo yau".
Ta fada tana rawar murya.
"Kama gabanki Nan ba wata mace a ciki gidan maza ne, idan Kuma Zaki shiga Bismillah tsuntsu daga sama gasashshe, Dan muna da kudajen da basa haram akan duk Mai tsautsayi, idan na Kara ganin giccinki a wurin Nan saina hadaki da karena yayi min fata-fata dake, wuceeee min daga nan" yayo kanta,da gudu ta kwasa ko waiwaye babu.
"Stupid! Da gani wannan tsohuwar kwarkwar ce wlh Banda oga ya hana da kinci na jaki banza wato kin samu oga a araha shine kuka Neman zaku masa shegantaka akan matarsa ni na rasa yanda akayi ma oga ya Fado garin Nan,? Kuma har ya iya Zama a haka ba wani damuwa, ko Dan meze dameshi Yana tare da wannan danyan gold din".
Ya fada Yana komawa bakin aikinsa Amma zuciyarsa fal tunanin abinda ogan nasa ya sani game da wannan matan daya turo Masa hutunan su ya Kuma shata musu dogon layi.
Asabe Bata samu zarafin tsayawa ba Saida ta dangana da wani gurin me suyar kifi a bakin titi shima gani tayi gurin da jama'a ko cimmata yayi za'a ceceta, gefe ta koma tana mayar da numfashi sai lokacin ta dubi hanyar data fito ko Mai Kama dashi Babu. Gefen wani dutse ta zauna tana tunanin to koba gidan da sukaje jiyan bane tunda ba wannan basamuden suka tarar ba Amma daga Daren jiya Zuwa yau har lamarin ya canza ita damuwarta daya shin sakon da suka bayar ya sameta ko kuma na jiyan ba shine asalin Mai gadin ba yayi musu ta 'yan duniya ya barbe kayan da kudin ya wuce nasa gurin.
Tashi tayi Kamar wadda aka tsikara ta dauki 'yar ledar data sawowa Mai gadin Dan abun tohiyyar Baki sai Kuma labarin ya canza salo. Harta dauko wayar ta Sai ta mayar idan tayi gigin fadawa Mama kwabarta zatayi ruwa Dan a yauma Saida Mana ta karo kudi masu nauyi tace a bawa Mai gadin yanda duk abinda za'a saka shi yaji baze iya gardama ba, to idan ta koma Mata da wannan labarin amshe kudin zatayi tasan halinta kayan ta, data Bata naira dubu gara ta bawa Dan tsubbu dubu hamsin, Sam Bata karuwa da ita saita wadannan hanyoyin idan ta aiketa tunda itace amintacciyarta ta Nan takeyin nata duk rintsi bazata so ta rasa wannan mafakar ba Dan Kusan da ita ta dogara gurin kwaramniyar yau da Kullum nata.
*******
Saida Zahra tayi barci Mai isarta sannan ta farka lokacin biyu har da minti ashirin da hudu, da sauri ta Mike tana addu'ar tashi daga barci tayi mamaki ita fa gani tayi kamar barcin minti goma Sha biyar tayi Ashe lokacin ya ja haka, alwala tayi tazo ta Fara sallah bayan ta idar wayar ta da dauko Ummee ta Kira cikin shauki tun dazu ta nemeta network din na garin ba kyau sai hakura tayi, Bata jima ba tana ringing aka daga ba Ummeen bace wata ce ta daga tana ta yi Mata larabcin gargal ita kuwa zahrar na language yafi kwarewa a Dan daburce tayi Mata bayini ta gane Ummeen ta fita masallacin Annabi sallah tunda har lokacin suna Madina basu tafi ba Kuma a yanda sukayi daga Saudi Arabia Nigeria zasuyo gurinta, sallama tayi wa matar ta kashe.
Number sajida ta lalubo ta syprus tasan zata Sha mita tun ranar da sukayi ways da wayar Amatu tayi Mata buyagi ta kashe Basu Kara waya ba, har tayi ringing ta katse Bata dauka ba, Bata hakura ba wani Kiran ta karayi shima Yana daf da ze katse aka daga.
"Haba bestie Ina ta kira kin shareni ko har yanzu fishin ne?"
Mai makon taji bestien sai muryar Fatima taji tana kwallawa Sajidar kira tana fadin "ku taho ga Amarya Zahra! Zahra" ta kirata da karfi tana murna kamar zata tsaga wayar, daya bayan daya suka dunga gaisawa suna ta korafin amarci Dadi ta Kama waya ta rufe wato Bata so a shigar musu rayuwa ko? Hakuri ta Basu tare da fada musu tayi missing din waccen wayar ne har sim din, sai daga karshe sajida ta karbi wayar.
"'yar duniya wato kinji dadin lamarin ko Kika wani shareni, ni yanzu ai yallabai Mahmud ya fiki kirki kinsan ya kirani Kusan sau uku? Daman ko Baki kirani ba Zan kiraki dazu wurin Sha daya ya kirani Wai na kiraki na lallasheki yayi tafiya ya baroki kina kuka?".
Ya fada tana kunshe dariyar ta.
"Malama ki fito kiyi dariyar ki sosai kada ta kume Miki a ciki,da kike wani kunsheta".
Dariyar tayi da gasken sai tayi Mai isarta tace. "Dan Allah bestie mekika bawa wannan guy din Kinga yanda yayi masifar macewa a Kanki? Wlh har tausayi yake bani Ni har mamaki nake idan ya kirani Yana min maganarki ranar Nan fa cewa yayi na bashi labarin zamanki a Nan syprus din wlh nayi zaton da Wasa yaki tunda nasan ba Karamin cajin kudi za'ayi ba. Amma haka na ware na rinka bashi labarin har na Gama ko a jikinsa, yanzu Ina aka tsaya da fatan komai ya dai daita? Dan nafi son dai dai lokacin ganawarmu muyi murna biyu graduation da naming ceremony".
"Wlh Zan kashe yaushe Kika zama haka Mai bin kwakwkwafin jama'a? to bazakiji ba an fada Miki kowa ma irinki ne ai wlh ya Abdul Hakeem ya debo ruwan dafa kansa Dan nasan Dan bawan Allah saiya rinqa guduwa daga gidan"
Wata irin dariya ta saki tana fadin "billahil Azeem gara wata wainar data wake yarinya gyara zancen ki idan ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma idan ana sallah ba'a magana".
"Wlh sharri zakiyi Masa Amma shi dai salihi ne".
"A inda salihai sukayi karanci ba".
"Mubar zance kawai tunda abun ya Zama haka".
Zahra ta fada tana cire hijabinta daga jikinta vest ce Fara Kal sai wando shima fari ai pink din kananun flowers gashin tayi parking a tsakiyar Kan ta kashe da band shima pink, sai fito baby sak.
Gyara kwanciya tayi, tayi ringinnine da wayar a kunnenta Hira sukaci gaba da sajida yawanci duk akan auren zahrar ne. Sun dauki lokaci Mai Dan tsawo suna tattaunawa akan bututuwa da dama kafin suyi sallama, ta nufi toilet wanka take son yi kafin ta fita cin abinci.
********
Jirginsu Mahmud a Addis Ababa Bole international airport yayi landing, daki biyu Sameer ya kama musu Nan kusa da airport din tunda a kalla zasuyi Kusan three hours.
Saida ya kaiwa Mahmud jakar laptop dinsa sannan ya nufi nasa dakin, bayan fitar Sameer Mahmud wanka yayi sannan yayi sallah maimakon ya kwanta ya Dan huta sai kawai ya bude wayarsa so yake ya ganta duk wani matsi da yayi tana manne da zuciyarsa so yake ya ganta kafin ya kirata. CCTV ya shiga ta wayarsa duk abinda akeyi ya rinka bi Yana gani yasha dariyar karon Zayyan da wannan matar wadda ko sunanta Bai sani ba, shi yasa ya dauko shi yasan shi kadai ne cikin amuntattunsa Wanda ze Masa wanna aikin ba tare da an samu matsala ba.
Saida ya gama kallon ko ina na gidan yaga ba wata matsala, sannan yayi zooming din cikin bed room dinta daga ita sai vest purple da wando skintight kanta tayi parking da purple din band sai tayi wani irin kyau na musamman, kura Mata ido yayi Kamar ya warto ta yakeji, turare ta dauko tana fesawa a jikinta. Nan ya shiriri ce Yana kallonta knocking din da akayi Masa ya katse Masa abinda yakeyi, umarni ya bada a shigo Sameer ne sai ma'aikaciyar hotel din dauke da tray na abinci sai karairaya take shi har dariya abin nata ya bashi, me Kamar zahra yaushe irin wadannan zasu burge shi, bayan ta wuce ne ya dago ya dubi Sameer "kada ka qara zuwar min da irin wannan a rinqa bawa maza suna kawo min kawai".
"Noted sir"
Ledar dake hannunsa ya Mika Masa Mai tambarin wani boutique ne, sannan ya aje Laptop dinsa a kusa dashi Yana nuna masa wasu ayyukan da ya Gama yanzu, sun jima suna aikin kafin sameer ya fita saboda lokacin tashinsu ya kusa cika shi kuma Mahmud ya ciro kayan da nufin sakawa.
Saida Zahra ta Gama feffesa turarenta sannan ta dauko after dress ta zura ta yane kanta da gyalen sannan ta nufo parlour, zalai ta samu tana 'yan goge goge duk da ba wani datti a gurin, gaishe da zilan tayi tana Mata sannu, ajiye mofar tayi "Allah ya taimaki uwar dakina ga abincin can nayi Miki abinda kikeso faten dankalin turawa da pepper soup din kifi"
Zama Zahra tayi tana fadin "Kai Amma wlh na gode kwarai da gaske shi yasa nake yinki kinsa favorite Dina wlh".
"Ai shi yasa na cewa Ammah kada a wani dauko yarinya tun daga Mubi Nima na isa na zauna dake saina kirawo Kanwata Alawiyya ta cigaba da yiwa Ammar kafin Allah yasa yallaban ya dawo, ai ni har zaman wanka ni zanyi Miki Koda kuwa bakwa garin Nan ne".
Dan smile tayi kawai bata ce komai ba saima ta canza akalar zancen.
"Ni Kuma Aunty zilai kin mikawa mutumin Nan abinci kuwa?".
"Ai tunda na Gama na zuba na hada harda ruwa da lemo na mika Masa. Naga Dan gayu ne beyi kalar masu gadi ba".
Dariya zahra tayi tana fadin "Aunty zilai kenan shi Mai gadi har Kama gareshi".
Yana da kama Mana Wai Kinga wannan din?"
Na ga wani dai dazu ban sani ko shine Wanda aka Kira jiya cikin dare".
" Cikin dare Kuma?"
Kai ta gyada "Mata kusan Hakan tunda Sha biyu ta wuce ya kirawo wani kawai umarni ya bashi yazo garin Nan da safe kinsan bakwai a Nan tayi mass nifa mutumin Nan wlh tsoro yake bani na kasa gane kansa".
Dan murmushi zilan tayi tana kallon Zahra "kiyi hakuri uwar dakina a hankali Zaki San komai a kansa badai Kuna tare ba da sannu Zaki gane shi din waye, kici abincin sai muci gaba da hirar idan kin gwma".
Bata k'i Shawarar zilan ba ta tashi ta nufi dining ita Kuma zilan ta nufi dauko Mata ruwa da mutuniyarta farm fresh, sai da ta Gama cin abincin sannan ta dawo parlourn gurin da tabar Aunty zilan sukaci gaba da hirar su, amma Kusan hankalin Zahra yana Kan Mahmud haka Nan sai taji ya fado Mata ta yarda da ake cewa sabo turken Wawa, yanzu da baya Nan sai taji duk kewarsa ta kamata, tun dazu take duba waya ko zataga kiransa Amma shiru tasan tsakanin Nigeria da inda zasu indai da gaske chinan zasu da nisa a kalla jirgin zeyi landing a Ethiopia da India yaci ace ya kirata Amma shiru har Yanzu ko lfy? ta ayyana a cikin zuciyar ta.
Ganin tunanin Zahra yayi zurfi yasa zilan ta tashi tana fadin Bari nayi wanke wanke tunda kin Gama da kwanukan"
Tayi hanyar kitchen, ita kuma ganin tunanin ze dameta yasa ta kunna tv ta kamo MBC MAX tana son finafinan su sosai,Aunty zilan ma data Gama Zama tayi sukaci gaba da hirar jefi jefi har aka Kira magariba suka shiga sallah. Tana addu'oin yaumiyya na cikin du'aul mustajaba ne kira ya shigo wayarta da sauri ta dauko tana duba Mai Kiran Ummee ta gani da sauri ta daga tana fadin "Ummeena"
Amsawa tayi suka gaisa Ummeen ke fadar an fada Mata ta kirane nan tayi Mata fadan rufe layi da tayi,nan Zahra taji kuka yazo Mata, Nan da Nan Ummeen ta rude tana tambayar ta ko tana da damuwa ne ta fada Mata cikin kukan tace "Ummee Shima fa wannan daga kawo ni gidansa ko sati daya ban rufa ba ya tafi ya barni Wai aiki zejeyi uk" shiru Ummee tayi kafin ta shiga rarrashinta da kalamai na kwantar da hankali da nuna Mata ba lallai ne hasashenta ya kasance gaskiya ba, kada ta damu saboda ita har Umara tayi bayan auren tayi mata addu'oin samun nasara akan dukkan lamuranta, sannan ta yi mata fadan ta kiyayi yawan kukan Nan bashi da ma"ana, daga karshe tayi Mata albishir zawan su next week harda Mama Hanifa da Aunty Nawwara duk suna hanya Daman ko Bata sameta a waya ba zata kira Hajiya Asma'u tasa a fada Mata. Murna ta shigayi Kamar tayi me har Ummee na Mata dariya Nan da Nan ta ware ta shiga lissafo abinda takeso Wanda za"a taho Mata dashi.
Bayan maga wayarsu da Ummeen Ammah ta Kara kira lokacin tana tare da Abba.
Tana zubawa Abba Dan fruit salad wayar ta dauki ringing Abban ne ya dauko ya duba 'yar dariya yayi Yana mikawa Ammar wayar tare da fadin.
"Uwata ce ke kira". Ganin Kiran ze yanke yasa Abban karbar fruit salad din yaci gaba da zubawa Yana fadin "A dauki Kiran uwata kada ya yanke".
Daukar tayi tana amsa sallamarta da gaisuwar da take mata.
"Ammah yanzu Dan Allah bazakizo ba Kuma Aunty Hasana ma fa batazo ba fa Kuma Ni sonake na ganki".
"Ikon Allah