Showing 96001 words to 99000 words out of 122700 words
don su fadada bincike akan ciwon tunda ta jima tana fama da lalurar".
"Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an Nemo Mata taimakon ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano wane irin ciwo ne a fada mini akwai magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha Allah zasu narke Koda na aikine zebi jinin al'ada ya narke ya zube".
"To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka".
Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama.
Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje Zahra tana barci sun gaisa da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi.
****
Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar suka fice sun Kai ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya dakatar da mutum hudu ya sallami mutane biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin tafiya tayi nisa Kuma baya bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki, zuwan Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai takanas din ya taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials da akayi Wanda suke zargin ba'a biya kudin harajin kasa ba a tun farkon bude kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta wibeside nasu Amma sunqi yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru.
Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi matukar gajiya sosai Koda yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na Zayyan da Habib su sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa.
Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake tare dashi Nan take tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga, Bai saurari gaisuwar da yake Masa ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da nayi bashi da anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da tsohon Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda throughout yau ban kirata ba nayi busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make text".
"Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?"
"Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani information akan komai ba".
Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya Kira shi.
"A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa.
"Wai meke fatuwa ne da Zahra?".
"Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam yace na kaishi Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana barci Amma idan an jima zan koma na qara dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka naji Abban su Yana fadin Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan sanar da kai Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin".
Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa.
Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka yasan wayar na gida Basu dauka ba.
A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama da Asabe Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje duniyar kanwar Babar su Asaben, shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da wayar Amman a.hannu Yana game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah, batare da Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo Mahmud ze Kira ba.
Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar yasa Ammar fadin "wa ake nema ne".
"Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude wayar ba muna aiki sai yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti, Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata fatuwa ba".
Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba.
Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci takeyi, ya akayi suka fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din ta zasu bincike a Kai".
Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa.
"To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano zasu dubata sosai tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka".
Sukayi sallama.
Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita tamkar mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau.
Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin yanayin ciwon nata gashi abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya barta da jangwam yanda aka Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi Kuma yayi masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji ance harda motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan".
Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana fada ne dan ta Bata Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra tana gyara Mata hannunta da aka saka mata drip, itama ko tari be kunce Mata ba bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace.
Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa.
"Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon Allah ba yaron Nan guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake Kar bashi da duhun jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya barta, idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu jinjinan dangi kana ji a sheganta yaro
ko yarinya".
Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo suka juyo tana kallon Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini har dakin mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin".
AUREN HUCE HAUSHI
MAMAN FATEEMAH
PAGE 35.
________Yana katse Kiran ya tashi tsam ya nufi masaukinsa laptop dinsa ya janyo ya shiga aiki sai kusan karfe daya ya kwanta lokaci bayan lokaci sai yayi murmushi idan ya tuno yanda suka rabu da 'yar gidansa yayi zance mata tana neman tikitawa kanta lissafi Wai ita me miji, kamar ta wani san dadin mijin,Saida yayi wanka yayi nafila sannan ya kwanta.
*
Zahra kasake tayi da waya a hannu kamar itace Mahmud din "me yake nufi da zasu rage Masa dare kenan neman Mata yajeyi?"
Take wata zuciyar tace Masa A'a Yana zolayarki ne da manemin matan ne koda karfin tuwo saiya nemi wani Abu a jikinki, kauda wannan tunanin tayi daga zuciyar ta tasan zato zunubi ne, parlour ta koma gurin zilai sukaci gaba da hirarsu sai kusan Sha daya suka shiga ciki.
Washe gari Zahra Bata tashi da wuri ba sai kusan Sha daya, tun cikin dare bata Jin Dadi wata irin murdawa mararta ke Mata, tana samun irin wannan pain din duk karshen wata idan zatayi period Amma wannan yanda yake mata yayi tsanani sosai tun wurin karfe ukun dare ciwon ya tashe ta farka a gigice, inda Allah ya taimaketa Bata sakaci ta rasa maganinta duk rintsi Yana tare da ita, a lokacin ta sha cikin ikon Allah lokaci kalilan ciwon ya lafa ta koma barci da Asuba ma data tashi sallah da sauki sosai sai Kuma yanzu data farka taji Yana neman dawo Mata, da kyar tayi wanka ta sake inner wears ta zura rigar matarial marar nauyi ta koma ta kwanta idan tana wannan yanayin ko turare Bata so sai guda daya kawai body mist ne na strawberry shi ta fesa ta koma ta kwanta Dan abinci dai baya ciyuwa a irin wannan yanayin.
Ganin Sha biyu tayi Zahra Bata fito ba yasa zilai nufar bedroom din nata ta gani anya lafiya kuwa?
Knocking tayi taji Shiru ta qara you taji Shiru Bata kara ba uku ba ta tura kofar a can tsakiyar gadon ta ganota a kudundune, da sauri ta karasa gaban gadon tana ambatar sunan ta "Zahra kafiyarki kuwa har Sha biyu ta gota Baki tashi ba abin Karin ki har ya Fara sanyi?"
Da kyar ta dago ta kalli zilan cikin miryar marar lafiya tace Mata "bana Jin dadi tun cikin dare marata take ciwo".
"Subahaballahi Kuma Kikayi Shiru Baki fada ba idan haka ne bani da amfani Kenan ace tun cikin dare kina fama da ciwo ki kasa fada mini, ina maganin da kike Sha yake na dauko Miki Ni wlh cewa nake tunda ance idan Kikayi aure ze dena, to na dauka kin rabu dashi yanzu, ai haka wannan likitar ta fada Miki zuwan mu na karshen ko?".
Kai Zahra ta gyada Mata kawai alamar Eh Dan ita kadai tasan azabar da takeji.
"Fada min Ina maganin yake na dauko Miki"
A hankali tace mata "Na sha".
"Kin sha Kuma marar Bata Dena ciwon ba?"
"Eh" ta fada tana runtse ido saboda azabar ciwo.
Fita zilai tayi da sauri ta koma dakin da aka sauketa ta lakubo keyboard dinta ta lalubo number Ammah, lokacin tana tare da Abba suna maganar komawa makarantar Imam Kiran zilan ya shigo.
"Abba Bari na daga Kiran Nan Zilai ce naji ko lafiya".
"In Sha Allahu ma lfy".
Abban ya fada.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu"
Ammah ta fada bayan ta daga wayar daga can zilan ta gaishe da Ammah sannan ta Dora da fadin "wlh Ammah jikin Zahra ne ba Dadi tun cikin dare ciwon mararta ya tashi Tasha maganin Kuma a banza shine nace Bari na Kira na fada Miki Koda abinda zakiyi mata tunda kema Aikinki ne ko Kuma a turo Mana malam Bala ya kaimu Asibiti taga likitar ta" .
"Ikon Allah! Yanzu ina zahrar?".
"Tana daki tana faman mukususu kamar me nakuda wlh abin gwanin ban tausayinsa".
"To shike Nan ki dubata za'a San yanda za'a yi ki jira".
Ta kashe wayar ta dubi Abba Wanda Shima itan yake kallo, kafin tayi magana ya rigata.
"Meya samu Uwata naji Kuna magana Bata da lfy ne?"
Ajiyar zuciya Ammah ta sauke "wlh ciwon mararta ne Wai ta tashi tun cikin dare Tasha maganin da take Sha Amma ba wani cigaba shine zilan tace ko Asibiti zasu koma suga likitar da take gani Dan munyi expecting idan tayi aure zasu rabu to Kuma a yanda zilai ta fada min kamarma yafi na baya zafi".
"Ikon Allah! Allah ya saukake Bari a tura musu magaji ya kaisu Asibitin tunda duk sauran basa Nan sai mu bisu daga baya mu kuma, ai hakan yayi ko?".
Kai ta gyada Masa tana kokarin tashi da nufin tafiya, riko hannunta yayi ya mayar da ita inda ta tashi dayan Kuma Yana Kiran wayar magaji.
"Ka dauki mota kaje can hayin banki zaka Kai uwata Asibiti".
Ya kashe Kiran yana kallon Ammar.
"Ina zaki Kuma Kika tashi? Ki kwantar da hankalinki in Sha Allah ba wata damuwa Kika sani ko jika zamuyi kwanan nan"
Ya fada Yana dariya irin tasu ta manya.
Itama Dan murmushi tayi tana fadin Allah yasa".
"Amin yauwa kokefa dauko gyakenki mu bisu wata Kila muje tare tunda gani a gida araha sai nayi aikin bariki tilas ne".
Zilan Ammah ta Kira ta fada mata su shirya ga magaji Nan ze kaisu Asibitin, Suma zasu samesu a can..
Dakin Zahra zilan ta koma yanda ta barta haka ta sameta, kusa da ita zilan ta matsa tana fadin na hado Miki ko ruwan shayi ne kisha Asibiti zamu".
Kai ta girgaiza Mata alamar bazata Sha ba.
"Ki daure ko kadan ne Dan Allah Kinga wata Kila ayi Miki allura gara kici ko kadan ne".
"Cornflakes".
Abinda ta iya fada Kenan ta koma ta kwanta.
Ba laifi tasha cornflakes din da Dan dama, rolling kawai tayi suka nufi parlour zilai na rike da ita. Basu jima ba sukaji dirin mota alamar magajin ya karaso Kenan, zilaice ta bude kofar tun Bai karaso ba direct inda zahrar ke kwance ya nufa akan two seater.
"Sannu Adda ya jikin naki?"
Da kyar ta cira Kai ta dubeshi tana fadin "da sauki".
"Allah ya Kara sauki, kamota muje kada Rana ta karayi yanzu twenty five minutes to one fa".
Zalai ta riketa tana tafiya da kyar suka fito compound din Zayyan yana zaune Yana game a waya tunda bashi da aikinyi a Nan sai zama,ba zato yaga an fito da Zahra haka, da sauri yayi wurgi da wayar Allah ya taimake kan jacket dinsa ta fada da sai dai wata ba ita ba, ya nufo gurinsu Yana tambayar "Lafiya meya faru? Oga kuwa ya sani? sannu" duk a lokaci daya yake jero wadannan tambayoyin da gani a rude yake.
Magaji ne ya nufi inda yake suka Kara gaisawa Yana farin.
"Ba wani abun damuwa bane Bata Jin Dadi ne zamuje Asibiti kada ka damu".
Zilai magajin ya duba "kun fadawa mujinta kada mu tafi babu sanin sa".
"A'a bamu fada Masa ba ai ko daga bayane an fada Masa yanzu dai muje Asibitin wannan ma wani Bata lokacin ne".
Da sauri Zayyan ya bude musu gate suka fita yayin da Zayyan din ya dauko wayarsa Yana Kiran Mahmud.
Ya kirawo shi Amma Sam taqi shiga sai text kawai Zayyan ya tura Masa ya koma ya zauna yana mamakin ogan nasa na neman gurin Zama a wannan Dan gurin shi ko takura ma yaga alama bayayi wata sabuwar rayuwa yake shimfidawa cikin kwanciyar hankali.
Direct A&E magaji ya nufa zilai ce ta taimawa Zahra ta fito daga mota suka shiga ciki shi Kuma magaji ya nufi inda ze karbo file.
Ba jimawa yazo ya kawo file din, bayan duguwar tambayar da wata likita da take on call tayi Mata ta rubuta Mata magunguna da allurai da drip ana cikin saka Mata ruwa su Ammah suka shigo dakin, ma'aikatan da masu jiyyar suna ta gaishe da Abba, gaban gadon Abban yaje ya tsaya sunan ta Abban ya Kira ta bude Ido ta kalli Abba tana kokarin tashi zaune "A'a uwata koma ki kwanta ya jikin naki?"
"Da sauri Abbana, Ina kwana?"
"Lafiya kalau".
Ammah ce ta matso tana fadin "sannu Ashe ciwon cikin ne ya tashi?"
"Eh Ammah wlh har yafi Wanda nakeyi kamar Zan mutu".
Ta fada tana goge hawayen daya zubo Mata.
"A'a uwata Banda kuka ai kin girma".
Abba ya fada Yana dariya. Itama Zahra dan murmushi tayi ta juya Kai kunya ta kamata ta.
Abba Bai bar Asibitin ba Saida aka Maida Zahra Aminity ward.
Tun bayan tafiyar su Zahra Zayyan ya kasa tsaye ya kasa zaune, ya nemi number Mahmud tafi cikin carbi amsa daya balarabiyar da akayi linking da computer ke bashi wadda ba fashimta yake ba, sai dai hasashe kawai number Bata tafiya take fada Masa.
A gida Abba yayi sallar Azzahar bayan an fito ne ya fadawa Baba malam Zahra tana Asibiti Bata Jin Dadi.
Cikin nuna jimami Malam yace "tun yaushe take Asibitin ba'a fada min ba, kuma menene yake damun diyar tawa?".
"Wlh ciwon cikin ne take fama dashi tun cikin dare shine dazu Mai Taya ta Zama ta kita Asma'u ta fada mata, sai nasa magaji ya Kai su Asibitin sai suka Bata gado Wai zasuyi Mata hoton cikin da sauran gwaje-gwaje don su fadada bincike akan ciwon tunda ta jima tana fama da lalurar".
"Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an Nemo Mata taimakon ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano wane irin ciwo ne a fada mini akwai