Showing 87001 words to 90000 words out of 122700 words

Chapter 30 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

877

ledar, ledar yace ta bude lafiyyayan dambun naman rago ne yasha kayan Hadi ya sayu jawur dashi sai Kamshi ke tashi, Dina yayi yakai Bakinsa ya tauna Yana fadin "Masha Allah uwata ta Gama min komai wlh har Raina Ina son yarinyar Nan bilhaqqi uba ta daukeni sak duba ki gani Rabi'a ga Asma'u a zaune amma Ni ta yowa wannan garar Kai madallah, Yau abincin ki sai dai yayi hakuri na uwata zanci".
Ya fada yana kallon Ammah. 'yar dariya tayi Ammah tana fadin "Ana ta sabon d'a wa yake ta tsohon da inji barmani choge".
"Gaskiya kam, ai Babu Mai shafewa Zahra Zane a gurin Abba"
Mama ta fada.
"Ki Fadi ki Kara Zahra yarinya ce mai tsananin yi min biyayya ki duba yanda lamarin auren Nan ya kasance Amma tunda tayi 'yan koke-kokenta ta hakura ba Wanda ya Kara Jin kanta, duk da mijin nata Mai Karamin karfi ne akan wadanda suka nemi aurenta Allah be nufa ba da Kuna duba da inda ta fito da Kuma uwa uba dangin mahaifiyar ta Amma tayi zaman ta Ni kuwa ba abinda bazan yi Mata ba matukar baifi karfin arzikina ba".
"Wannan gaskiya ne duba da yanda ta waye tayi karatu Mai zurfi ai ba wata ce bijirewa zatayi ayi ta Kai ruwa Rana"
Mama ta fada.
Yar dariya kawai Ammah tayi duk Dadi ya cikata Bata taba tunanin Zahra nada wayo haka ba tasan dai abun duniya Bai rufe Mata ido ba.

✨✨✨
✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨✨
✨✨✨

Maman Fateemah.



Page 32



_______Qaran alarm din daya saita ne ya tashe Shi sallar Asuba, duk da bai kwanta da wuri ba Dan sai Kusan karfe biyu na dare suka shigo gidan, meeting din nasu sun jima suna tattaunawa akan sabon kafanin da zasu bude a jihar kebbi na shinkafa, masallacin da suke sallah da gidansu akwai tazara sosai shiyasa ya saita kafin sallar Asuba da kamar hour daya, sai da yayi yaqi da Shaidan sannan ya samu ya sauko daga gado Bai jima a toilet ba ya fito sanye da bathrobe Fara tas Mai jikin towel. Jallabiya ya saka yayi raka'atanul fajri sannan yayi waje a Yana niyyar yiwa Sameer knocking ya bude ya fito.
"Barka da Asuba" Sameer ya fada yana mikiwa Mahmud hannu sukayi musabaha,
"Ashe ka tashi ai nayi tunanin saina shafa maka ruwa sannan ka mitsa".
'yar dariya Sameer yayi Yana fadin "irinku da kuka San inda kuka dosa Kuna dagewa da mujahada to mu ta Yaya zamuyi kwance muna barcin asara ai sai lalacewa tayi yawan".
"Kayya Kai dai Allah ya datar damu kawai"
"Allahumma Amin"
Sameer ya fada lokacin da suka jero suna Kara tattaunawa akan harkokin yau da Kullum, Sameer ne yaja musu motar suka fice daga gidan, bayan sunyi sallar zama sukayi akayi karatu Kusan masallacin mahadar 'yan Africa ne mazauna can Kusan duk Wanda yake a kukkuken gurin Baya Bari khamsu salawat ta wuce shi, sai da gari ya waye sannan suka nufo gida.
A hanyar ne Sameer ke fadawa Mahmud sunyi waya da Habib jiya a kan training din da za'ayi na matasa maza da Mata na koyon sana'a.
Har suka zo gida suna zancen, yaso yayi barci amma ya fasa, so yake ya Kira Nigeria baze iya mazewa ba Kamar yanda yayi niyya Bai gane shi Mai rauni bane sai akan yarinyar nan,sai da yayi Mata nisa ya gane shayi ruwa ne, duk da Bata shigo rayuwarsa da Wasa ba kafin ya hadu da ita shi jarimi ne sannan shi baima fa San yanda kake kwana da Abu ka Kuma tashi dashi, shifa idan ya tunata har wani ji yake zuciyarsa ta harba, yaso ya dan Bata iska, so yake ya fahimci shin ta karbeshi da zuciyarta da gangar jikinta ko Kuma har yanzu tana zaune dashi ne by force na iyayenta, amma idan ya kalli kwayar idanunta Yana hango wani Abu na daban a cikinsu Kuma uwa uba yanda sukayi rayuwa a Dan zaman da sukayi da ita.

Bayan sun shiga gida kowa nasa gurin ya dosa Dan shi dai Sameer barcin ya kama, shi kuma daya shiga wanka ya sake, shifa idan ze wuni Yana zubawa jiki ruwa bashi da damuwa. Sai da ya gama komai ya Haye gado daga shi sai singilet Fara sol da boxer short.
Wayar ya dauko dauko cikin ikon Allah yaga Zahra online ji yayi wani Dadi yaji ya rufe shi, vedio call ya Kira daya wayar Kuma ya bude connection din CCTV.
Tana cikin charting da Aunty Nawwara kawai kiran nasa ya shigo Yana kallon yanda ta kwalalo Ido waje abin har yaso bashi dariya, hijabin da tayi sallah ta dauko ta rufa kirjinta sannan ta daga Kiran suna hada Ido taji gabanta ya Fadi ji tayi abun Nan na da ya dawo Mata.
Sallama yayi mata da husky voice dinsa wanda ya saukar Mata da wata muguwar kasala, a hankali ta daga idonta ta kalleshi cikin murya Mai rauni da rashin karsashi ya amsa Masa sallamar, kuri yayi da idon Yana kallonta yanda tayi Masa wani irin kyau Kamar shi gani yayi a tsakanin jiya da shekaranjiya Kamar an Kara Mata kyau.
"Ki bude Ido ki kalleni ki bani labarin abinda ya faru daga tafiya ta Zuwa yau, kuma wlh ki cire hijabin nan tunda ba sirikinki bane Ni da Zaki dauko hijabi ki Kama rufe jiki wato Ni ban cancanta Naga abinda yake halalina ba ko?"
Kai ta girgiza tana masa kallonsa a shagwabe.
"Nifa tunda nayi sallah nake sanye da abuna bawai saboda Kai na saka ba nida bansan zaka tuna Dani bama ballentana ka kirani, nifa na dauka Kama shafe babina tunda baka nemana wanda ka damu dasu kake nema".
Ta fada tana juya sexy eyes dinta wanda Bai sani ba ze dauka da niyya tayi Hakan.
Ajiyar zuciya yayi Yana Hadiyar yawu shifa ganin Nan da yayi Mata ta jangwalo masa wata fitinar da sai Allah kawai.
"Ki cire hijabin Nan Allah kona Baki mamaki". Kafada ta make tana kallon gefe Dan wani fitinan nan kallo yake Mata.
"Dan Allah ka dena kallona".
"Ikon Allah wato naje nayi ta kallon Mata a titi kenan ba ruwanki ke ko irin 'yar kissar Nan ta Mata Ni baza'ayi min ba tunda ni ba Mai aji bane banyi boko mai zurfi ba ko
"Ni kuma? Yaushe nace bakayi karatu Mai zufi ba?"
Yar dariya yayi irin ta kana cikin ?nishadi din nan.
"Wato wayo zakiyi min na bar maganar hijab wlh ki cire Kona biyo dare nazo Nigeria na....
"Dan Allah ka Bari wlh Zan cire kada ka fada".
"Ki Bari kiji mezance Mana my previous".
Ya fada Yana Kashe Mata ido.
Itafa mamaki yake Bata idan Yana fadar wasu kalmomin turanci sai taji Kamar zurfin iliminsa ya wuce yanda ake fada, ta ko Ina a waye yake ga wata irin tsabta ta ban mamaki itafa idan ba karya idonta yayi Mata ba sai tace Bata taba ganin ya Mai maimaita Kaya ba idan ya saka Bata qara ganinsu a jikinsa.
"Wlh kiyi abinda nace kona baro Miki aikin da Baki shirya Masa ba, 'yar yarinya dake kin hana zuciyarta sakat tunda na Dora idona a kanki komai ya kwance min duk, akanki na iya tsayawa nayi doguwar magana na iya ja in ja akan Abu duk soyayata da Hajiya Innata saida mukahau sama da ita mukayi uwar watsi nayi Mata yaji Kuma haka kawai Allah ya dubi diminiya ta ya tausayawa Dan malam kiyi min rowar ganin halalina, wlh Zan fadawa oga Sameer ayi min afuwa na dawo gida na fasa attending din meeting din a saka wani na dawo na rungumi 'yan kayana".
" Wai Kai baka jin komai idan ka Fadi magana! Dan girman Allah kayi zamanka kayi abinda ya kawoka in dan hijab bari ba cire. Amma Dan Allah ka Bari na saka riga Allah ba kaya a jikina sai vest".
Wani kallo ya jefeta dashi na Amma kin Raina ni.
"Dan Allah, wlh kunyarka nakeji da gaske"
Ta fada tana sunkuyar da Kai kasa.
"Kunyata ni Kuma wlh immediately kuwa Zan cire kunyar Nan aini cutuwa zanyi, To wai tsaya na tambaye ki yaushe Hakan ta faru? Ko bayan na baro kasar ne ki? amman ai bakya jin kunyar kallon tsabar idona ki tarewa wani Kato fada Dan nace masa lusari kika Kare min tas har kina fadin na Kama ki na runguma ko kina min kallon Dan duniya ko? humm Ashe ma duka nine lucky din a cikinsu dama na San abin nawa ne Aida saina dama daddawata da moda a lokacin Dan wlh a Ranar sai da na Raina kaina Banda mutum besan gobensa ba Aida saina Yi wandaqata a lokacin" fuskarta ta rufe da tafin hannunta dayan, da gaske so yake ya koya Mata fitsara taga alama shima ba kyalle bane cikakken zani ne. Idonsa ne ya sauka q gurin data cire hijabin.
"wow!! Masha Allah! Koke fa Amma da kin zumbuda hijabi Kamar wata matar liman ai yanzu hirar zatafi Dadin yi ki kawar min da tunani kowa daga zuciyata sai naki, Baki fada min abinda kukayi jiya ba Naga harda spare girki a waje" .
Zaro ido tayi tana dubansa "waye fada maka nunyi wani Abu a gudan?
"Nina gani kinsan nabar idona daya a Nan na taho da daya, ga Kuma Dan gidana magaji shine yayi min voice note ya bani labarin selfishness din da kikayi na kawai su Abba Kika garar arziki ta juma'a Kika ware min iyayena Mata, shi yasa Kika saye zuciyar su Abba da Baba malam kenan,? Kullum maganar daya ce ga amanar yarinyar Nan ka kula da ita Ashe dai tushiyar Baki kike bayarwa".
"Kai wlh ba haka bane ai gani nayi idan na kaiwa Abba Kamar na bawa Ammah ne, haka Baba malam ma ai Iya Abula na bawa koba haka ba"
"Eh kusan Hakan ne amman dai da gyara, Kuma kike wani cewa Abula ko 'yar Karar Nan Babu nifa sunan tsohuwata ne,amma kici gaba da fada wata Rana kunya zakiji idan Kika fada a gabanta tunda bakinki ya Saba fada kinsan dai mu mutanen karkara bama Raina abun fada can zakiji zance ya zagaye cikin kauyen mu ace Mamuda ya auro 'yar birni ko sunan Inna Bata sayawa gatsau take fada".
Kai ta Dade tana tadan turo Baki irin na sakatattun yaran Nan tana fadin "Nifa ban sani ba Ina janta ne tunda sunan kakata ne babar su Ammah zakace min waye waye nima ai Mamana ce ba taka bace Kai kadai yanda kayi kutse a gurin Amma Nima haka zanyi a gurin Mamana harda Hjy Inna".
"Kice nayi celebration ana son da Ammi, inye matar Mahmudun ba, fada min wace addu'ar kike min Dana kasa kallon ko wace mace da sunan so tun bayan kin shigo rayuwata, da dai bana musu da kowa Amma a kanki humm har bore Saida na koya, oya fada min sirrin inji?"
Shiru tayi saboda ji tajeyi kamar zir take a gabansa, Amma ta lura shi ko a jikinsa kamar ma be damu da yanda take din ba.
"Kinyi shiru ko abun sirri ne baza"a fada min ba?"
"To me kake so na fada maka".
"Komai ma, me kike fadawa samarin ki idan sunzo zance? Nima yau zancen nazo Wanda ban samu damar yi ba a baya shine yanzu nike qara'i".
Batasan sanda tayi dariya ba "Au dariya ma na baki ko? Shike nan wlh nifa a kanki na iya zance me yawa da mace ada daga Ammi sai Hjy Inna kawai nake doguwar Hira sadu, nasan duk ranar da Hjy ta ta ganki sai tayi Miki ciwon Baki tace dan kwali yaja hula kinsan meta fada lokacin Dana fada Mata mgnr ki?" Girgiza kai tayi alamar A'a.
"Cewa tayi idan na cika cikakken namiji na shiga duniya na nemoki, Ni kuma nayi wani Alkawari daga ni sai Allah saina bata mamaki wlh".
Kama Baki tayi tana Dan Zuba masa sexy eyes dinta wadan da ke rikita Masa lissafi.
"Kakar taka zaka bawa mamakin duk soyayyar da kake yi Mata kace za'a ganku a rana?".
Kai ya gyada Mata yana gyara kwanciyarsa.
"Yes ai kece mahadin aikin da zanyi na Bata mamakin ko bazaki tayani ba?".
"Ni kuma meya hadani da dabin ku?"
"Kina son sani na fada Miki?"
"Uhm".
Karan doorbell ne ya dakatar dashi daga kokarin bayanin da ze Fara mata.
"My precious Afuwan naji ana bukatar shigowa Bari naje I will call you later, take care by".
Ya tura mata wani hot kiss Yana kashe Mata ido ya sauka daga online din.

********


DAMAGARAM.

Waya ce a kunnenta tana magana cikin tsantsar ladabi kamar tana gaban Mai magabar, cikin ladabi ta Fara fadin "wlh Hajiya ba haka na fada Masa ba cewa nayi kada ya tura kowa Abuja nayi booking din flight ne daga Abuja Zuwa sokoto, tunda Yaya ishaq jirgin Abuja ya yi min booking Kuma nace masa ko nazo sokoto bana son a turo min kowa yanda na fita Ni kadai haka bake bukatar dawowa ni kadai kinji yanda mukayi dashi ai nace masa Zan dawo Amma gani yake kamar gaba zan karayi"
"To ai yanda Kika gindaya Masa dokar ne yake tantamar hucewar taki, kiyi hakuri Zainab anyi Miki ba dai daiba Amma ki zama mai yafiya akan laifin da akayi Miki kema sai Allah ya yafe Miki naki kura kuran, ki Kara godewa Allah kece karama ke Kuma Allah ya daukaki naki Dan fiye da kowa a dangi ki dauka abinda ya faru jarabawarsa ce tazo a haka,Daman Allah swa yace shin bana jarabceku ba? to ki dauka hakan rubutaccen al'amarine daga Allah idan aka daure wata Rana sai labari, shi ba yaro karami bane da za'ace ya bata kawai yayi Mana fushi ne inaji a jikina Yana kusa da dawowa garemu da izinin Allah, ai kawunsa mustapha yace min ba abinda ya tsaya a harkokinsa Dan yana bibiyar lamuransa a yanar gizo yaga komai yana tafiya daidai".
"Nima Ina bibiyar lamarin nasa Hajiya Amma abinda yafi damuna koni bai taba kirana ba ko sau da har zuwa Yau".
"A'a Zainab mu duka masu laifine lokacin daya kamata a saurare shi kowa baya ya juya masa, Banda Mai biyaya bane yanda Allah ya daukaka shi ko ganinsa basai yayi Mana wahala ba? Amma yaro Mai ladabi da biyyayya mun taru mun yi masa naqi ba dole yayi nesa damu ba".
Saita balle da kuka, da kyar Ammi ta lallasheta tayi shuru. Sannan tayi mata sallama tana Kara jaddada Mata zuwan tare da fadin ta turo direbanta ya daukota Dan gidanta zata sauka tunda anan tabar motar data zo gurin Hajiyar da ita a Ranar data wuce YAMAI.
Aunty Badi'a ce ta karaso kusa da Ammin tana fadin "ina ganin soyayyar uwar miji da matar d'a amma ban taba ganin irin taku ba inaga yanda Hajiya Inna ke sonki ko Yallabai Bata so haka gashi ta kwallafa rai kan Mahmud kamar me"

Zama sukayi a Kan sofa daya dake cikin dakin.
"Wlh Ni kaina Aunty Ina jinjina yanda Hajiya ke Sona da dukanin yarana shi yasa sau da yawa idan wani Abu ya taso a gidan bana Bari taji ko labarin sa Dan nan da nan zata tashi hankalin gidan sai Kuma abun ya Zama wani Abu daban Dan Kullum gani sukeyi na Gama da kowa a gidan ballentana abinda ya biyo bayan rigingimun da akayi wanda suka saka na baro musu gidan,sai Abun ya Kara zafi ganin irin tujarar da general yayi da irin hukuncun daya yanke".
Dan nisawa Aunty Badi'a tayi kafin tace. "Abinda dai baiyi tsabta ba Kam sai dai fatan Allah ya kiyaye gaba, Daman shigowa nayi muyi magana akan hukuncin da Zaku yanke ne hada Mahmud Aure da 'yar aminiyarki matar takawa, tun a jiyan naso mu tattauna sai nayi Baki sauka cinye lokacin, me ze Hana ki Bari aga dawowar tasa tukunna sannan kiyi masa tayin yazo yaga yarinyar idan Allah yasa tayi masa a irin matar da yake ra'ayin ta Zama iyalinsa Kinga shike Nan idan Kuma an samu sabainin haka Daman ba'a amsa ba bare zumuncin ku ya samu matsala ko ya Kika gani?".
Shiru Ammi tayi tana nazarin maganar matar yayan nata Kuma 'yar uwa abokiyar shawara.
"To ai abin dubawa Aunty kada fulani taga ban kyauta mata ba tayi min na huce ace na buda Mata kasa a ido bazan iya ba, idan Allah ya dawo dashi mijin mace hudu ne idan Yana da wadda yake muradin aure ya Kara da ita Dan nasan bazeki Haura'ul Insiyya ba, duk abinda ake nema ga Diya mace Allah yayi Mata ga uwa uba nasaba".
"Haka ne Allah ya dawo Mana dashi lfy ya Kuma zaba abinda yafi Alkhairi, Amma dai in ina Raye wlh ba Mai yiwa yarona dole ba ruwana da Amincin ku can tsaninku"
Baki Ammi ta Kama tana Fadin "Tofa kaji masu 'ya'ya wato kin nuna side ko?"
"Ki fadin koma meye Amma dai a barmin yaro ya samu peace of mind gaskiya, shi bashi da idon ganin matan ne? Ina cewa kasashen duniya yake yawo Kinga kuwa wane irin Mata ne be gani ba, Kuma da bakinki kike fadin yace shi da wadda yake so daman biyayya ce kawai zeyi ya karbi auren da aka bashi Amma komai Daren dadewa zeyi wani auren to ki cire kanki a cikin jerin masu tilasta 'ya'yan su auri abinda sukeso, ki bishi da addu'ar Allah ya hada shi da abokiyar Zama ta gari kawai, se kimarki ta karu a idanunsa ki Zama abokiyar Shawarar sa babu abinda ze rufe Miki Amma kina shigo Masa da irin wannan zance ze Miki wani aji na daban, baze saki jiki dake ba balle kisan menene matsalarsa, ki tsaya kiyi nazarin abin nidai shawara ce na baki"

Tunda Aunty Badi'a ta Fara Kora bayani jikin Ammi yayi sanyi saboda suk abinda Aunty Badi'ar ta fada gaskiya ne, nisawa Ammin tayi "haka ne Aunty wannan observation ne me kyau hakan zanyi Daman fulanince ta Fara kawo maganar Naga Kuma ya dace na Bata goyon baya, Amman in Sha Allah zanbi Shawarar ki...✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI


✨✨✨

Page 33.


MAMAN FATEEMAH.


________Zahra ta Dade a kwance tana sakawa da kwancewa, wani irin yanayi takeji a jikinta ita abun har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login