Showing 60001 words to 63000 words out of 122700 words

Chapter 21 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

584

rusa muku budget din sai kuyi duk abinda zakuyi, an fada Miki Nima son abin nakeyi ne? da har Zaki tsaya kina min rashin kunya akan wannan lusarin Mai karairaya kamar mace,ke yanzu wannan har wani namijin arziki ne da ze iya dake? wallahi da kinyi tsautsayin aurensa da kin Gane Baki da wayo, idan Kika Kara gigin fada min magana makamanciyar irinta zan Baki mamaki wallahi, , har kike wani zakewa kina fadawa mutane magana, kice tak akansa billahil Azeem sai kin Raina kanki a dakin Nan saina banbance Miki tsakanin namiji da muna maza".
Yayi tsaki ya juya abinsa cikin takunsa na ingarman namiji ya fice daga dakin zuciyarsa kamar zatayi bombing.
A yanda su zulai sukaga ya fito Saida abin ya Basu tsoro kallon kallo suka shiga yiwa juna, sahura ce tace.
"Zulai bakiga yanda Mai gidan nan ya fito bane? Allah yasa ba mutuniyar taki bace ta taboshi Kinga ai ba haka ya shiga ba".
Zama zilan tayi tana fadin "waya sani sahura muna Nan tare dake, nifa shi yasa nace ba zanzo ba yau amman Ammah ta matsa akan sai nazo na Gane mata lafiyar ta,tun safe wayarta idan an Kira Bata shiga".
"To Kinga kuwa dole ki dubota ki gani ko Lafiya ya fito a haka kofa a dawo lfyr mu bai amsa Mana ba".
Jiki ba kwari zulai ta nufi bedroom din Zahra ganin zilan ta shige cikin corridor sahura ta Ciro wayarta Nokia ta Kira Mama. Ba bata lokaci ta dauka kamar jira takeyi ta shiga labarta mata abinda ta gani tun daga kan kayan da suka Zuba store har fitowar Mai gidan yayi da alamun bacin Rai a tare dashi, to kawai sahurar ke fada alamun wani Abu mamar take fad'a Mata sannan sukayi sallama.
Sai da ya fice harabar gidan ya Ciro wayar daga aljihun wandonsa ganin Sameer ne yasa ya Maida wayar ya nufi inda Sameer din yake zaune cikin mota, Bai Masa magana ba, zagaya yayi ya shiga motar yana fadin "let's go"
Ganin yanayin daya fito ya hana Sameer din korafin barinsa a waje baice ya shigo ba, dan kwantar da kujera Mahmud din yayi ya kwanta yasa hannu ya dafe kansa da gaske Sara Masa yakeyi lokaci lokaci Yana Dan Jan tsaki, Sameer dai be tanka Masa ba yasan a kusa yake, sai da sukayi nisa da gidan Sameer din ya Dan juyo yana tambayar.
"Ina muka nufa yanzu nifa na gaji ga yunwa Ina ji kace muzo gida muci abinci Kuma ka watsar dani a mota inaga ma sai da ka rage zafi ni in Nan Ina hamma ka shanyani".
Ya fada Yana Maida hankalinsa a titi.
Tsakin ya Kara yi Yana dagowa daga kishingidar da yayi Yana duban Sameer din "Allah ya shiryeka ka dauka kowa ma irinka ne Wanda baya iya kauda Kai a Kan Mata? Muje can hotel din kayi order abinci kaci tunda bani na gayyato ka ba cewa nayi ka dorowa mota kayan Kai Kuma sai gurin jibi kazo, to bansan wane kinibibin ya kawo ka ba ka bar yarinyar mutane da ciki kana gantali".
Ya karasa maganar Yana hararar Sameer din.
Dariya yayi Yana "fad'in easy man bani na kar zomon ba rataya aka bani, waya fada maka lamarin su da sauki? bakaji abinda Abbanta ya fada maka ba? ai da yace sai ana hakurin da gaske ne Zama dasu Saida hakuri".
Wani sakaran kallo Mahmud din ya aikawa Sameer da shi.
"Ka wani zaqe kana ta zuba wani Abu nace maka tayi min ne? da kaketa faman fadin maganganu haka tsabar saka ido kawai, gobe ka tattara ka koma inda ka fito tunda ba gayyato ka nayi ba da zaka dameni da kananun maganganu zan shigo da kaina kanon ba ai ba bakuwa ta bace ba".
Ya fad'a da gaske Yana Bata rai.
Shiru Sameer din yayi ganin da gasken koma Nene yayi touching dinsa sosai.
Suna shiga harabar hotel din kafin Sameer ya Gama parking a parking lot Mahmud ya bude ya fice abinsa Yana picking din wayarsa da aka Kira.


******Tunda zulai ta doshi kofar bedroom din Zahra take jiyo Kamar shashhshekar kuka, hannunta har rawa yake gurin bude kofar Dan ba maganar knocking, rubda ciki ta sameta tana faman shashhshekar da sauri ta mayar da kofar ta rufe ta karasa gurin zahrar da sauri tana Fadin.
"Subhanallahi uwar dakina me zan gani haka me kikayi masa? Dukanki yayi? Dan Allah kiyi magana Kona Kira Aunty Hasana ne sai ki fad'a mata ko na Kira Miki Ammah".
Kai ta girgaiza mata alamun a'a, "to ki fad'a min ko zan iya yi Miki wani abun Mana".
Saida kukan ya lafa Mata sannan ta yunkura ta tashi zaune ido zulai ta zuba Mata ita ba yarinya bace kallo daya tayi Mata tasan da wata a kasa ganin yanda take a yamutsa ga labbanta sunyi jajir abinka ga farin Mutum ga gashin kanta duk gyaran ya turje. Zama tayi kusa da ita sai a lokacin taga gaban rigarta a yage Hannun bra dinta guda a tsinke.
Kai kawai zulai ta dafa tana Fadin "mezan gani haka ni zulaihatu! Haba Zahra'u me yayi zafi haka ai sai kisa ya illataki a banza, gardama kika yi Masa yayi Miki haka?"
Cikin shashhshekar kuka tace "A'a maganar Musbahu yake min shine ya Fadi Abu marar Dadi a kansa shine kawai Dan na mayar Masa da amsa Nima yayi min haka". Ta karasa fad'a tana kuka.

Kasake zilai tayi tana duban zahrar kafin tace
"Haba Zahra'u da wayonki da hankalin ki Zaki rinka irin wannan abun har yaushe Zaki ringa maganar wani namiji a gaban mijinki har kiyi ikirarin fad'a Masa magana marar Dadi akan shi ai yayi Miki kadan wallahi idan wani ne yau basai gobe ba saiyayi Miki kaca-kaca yanda ko sunansa ba Zaki Kara fad'a a gabansa ba, kada ki kuskura ki Kara irin haka Zaki ragewa kanki kima da daraja a idonsa, duka yaushe akayi daren da shashshawa zata Bata,Ina cewa jiya aka kawo ki amma ace an Fara da haka kinga abin baiyi kyau ba ko kadan, yanzu ki tashi ki shiga kiyi wanka da ruwan dumi zanje na cewa sahura kina wanka ne, mu tafi kawai tunda nasan halinta Abu kadan zata fara yaya tashi tunda nasan badan Allah ta biyoni ba dan Saida na fito harabar gidan ta biyoni.
Sallam zulan tayi Mata Tana Kara tausarta akan ta ringa tauna irin maganar da zata ringa fada masa.

Cikin karfin Hali ta Mike ta nufi toilet da gaske ya tsumama mata jiki ta jima a toilet din tana kuka maganganunsa sun Mata ciwo matuka har wani gori yake Mata Shima ba sonta yake ba, to an fada masa ita son nasa take har yake wani Mata wulakanci, ita ta rasa a Ina ta kuskuro ne take haduwa da fitintinu daga wannan sai wancan? "Astagafirullah".
Ta fada a zuciyarta, alwala ta dauro ta fito ba wani kwalliyar azo a gani tayi ba duk ranta a cunkushe ga 'yar wayar da zata debe mata kewa ma ya dauke, a ranta tace "mugu kawai wani sumumu kasam dashi Kamar na Allah Nan kuwa dan duniya ne Mai lasisi".
Tana cikin saka kaya taji karan bell alamun Baki a gurguje ta ida yafe gyalen rigar ta dan fesa turare tayi gaba.

*****
Sai Bayan sallar magriba su zilai suka karasa gida dai dai lokacin Magaji ya fito da manya warmers a hannunsa sai Autan Ammah da basket a hannunsa Shima, zasu kaiwa zahra abincin dare.
Suna shiga zilai ta wuce part din Ammah ta fada Mata sun dawo ita Kuma sahura ta nufi nasu bangaren sai da zulan ta shige part din sannan sahura tayi wuf ta shige sashen Mama.
Salma kawai ta samu a falon tana kallon series na India ko arzikin amsa sallamar sahurar Bata samu ba sai wani kallon banza tayi mata tana Fadin "lafiya Kika wani shigo afujajun haka?".
Kafin sahura ta samu zarafin Bata amsa Mama ta fito daga bedroom din ta tana Fadin Kamar maganar sahura nakeji?"
Cikin azarbabi tace "nice Mama mun dawo".
Ta fada tana Zama a kasa kan carpet.
Cikin kwarewa da munafurci ta shiga korawa mamar bayanin abinda ta gani harta Kara da cewa.
"Anya Mama yaron Nan kuwa Babu abinda yake boyewa kin ganshi kuwa? Gaskiya wallahi baiyi kama da fakiri Mai neman abincin yau da gobe ba, kayan abincin da muka zuba a store din wallahi ni wani abin ma ban taba gani ba hatta madara wannan manyan gwangwwnaye sunfi ashirin Nama kuwa na kaji kawai sun Kai hamsin Banda na rago Banda na shanu Banda kifi Allah Mama Saida muka cika freezer din cikin kitchen din ga lemuka da ruwa Kamar banza ga......
Bata Bari ta garasa ba ta daga mata hannu "bar shi kawai jeki zan nemeki".
Mikewa tayi tana Fadin "a huta lafiya Bari naje nayi sallah naji ana Kiran insha'i". Ta fice.
Tunda ta fita Mama ke jijjiga Kai tana kwafa, Sam hankalin salma na can gurin kallon ta Bata damu da abinda su mamar suke ba, Saida mamar ta Kira sunanta sannan hankalinta ya dawo Kan mamar tasowa bayi ta dawo kusa da ita tana fadin.
"Mana menene Naga kamar ranki a bace,?".
Tsaki tayi tana fadin.
"Anya Abbanku da Asma'u ba ninkeni sukayi a baibai ba kan auren yarinyar Nan? ni daman tunda naga daga b'angaren Asma'u da 'ya'yan ta da 'yan uwa ba wata turjiya nasan da abinda suka taka bakiji labarin da sahura tazo min Rashi ba?".
Kai salmar ta girgaiza alamar bataji ba, Nan Mamar ta shiga fad'a mata abinda sahurar ta fada Mata, Nan da Nan hankalin salma ya tashi ta shiga fadar "ai laifinki ne Mama Nan nazo na fada Miki naga wani inaso a gurin Baba Malam Kika dinga zagina duk yanda naso ki fashimceni shi ba irin wanda kike tunani bane ni naga abinda na gani Amma Kika shafawa idanunki toka kikaki saurarena ai gashi nan duk fafutukar ki ta tashi a banza ko yanda kika fada min gidan yake ai kinsan da wata a kasa".
Ta fad'a tana share hawaye, Nan da nan hankalin Mamar ya Kara tashi idanunta sukayi jajur, cikin kaushin murya ta Fara fadar.
"Ni za'a yiwa haka wallahi sai dai kowa ya rasa Dan wannan auren sunansa matacce dole ya saketa ko baya kaunar Allah ai indai Ina raye yarinyar Nan sai dai kyanta ya Kare a banza ba dai tayi aure inda zata huta ba ita da hutu sai dai tayi nata gaji da aiki, duk wani haske na rayuwarta saina dusashe shi Bari ma ki gani".
Ta yunkura ta Miki ta nufi bed room dinta tana lalubar wayarta.
Ayi hakuri ba editing Naga kwanaki wata na fadar kada a karanta rubutun ba kyau.




AUREN HUCE HAUSHI



Story
&
Written
By

Maman Fatimah.

Godiya da yabo sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Amincin su tabbata ga shugaban mu Annabi MUHAMMAD s.a.w.w.


Page twenty two. ( 22)


📖🖋️

________Mahmud Bai bar cikin hotel din ba Saida yayi sallar insha'i, cikin gari ya koma gurin malam lokacin sun Fara karatun dare da maza manya Kamar Yanda suka Saba, shima littafin ya dauko na Riyadussalihinp ya zauna daukar karatun sai gurin takwas, bayan jama'ar sun watse ya rage daga malam din sai Mahmud da Habib.
Ganin Mahmud din ya zauna malam yasan da magana, Saida Habib ya gama gyara littatafan kusan aikinsa ne shida Abubakar, bayan fitar Habib din kusa da malam din Mahmud ya matso Yana Fadin Baba barka da dare".
Cikin sakin fuska malam ya amsa Masa Yana Fadin.
"Ya akayi ka zauna har wannan lokacin baka koma ba kasan ba sabawa tayu ba itama ya kamata a ringa kula". Kai yadan Sosa Yana Fadin in Sha Allah yanzu zan tafi daman na tsaya ne Ina son muyi magana".
"To Babu laifi ina saurarenka".
Qara sadda Kansa yayi Yana Fadin.
"Daman game da maganar tafiyar da zamuyi ne nace ko za'a samu wadda zata zauna da yarinyar Nan ne?".
Gyaran murya malam din yayi kafin yace

"Eh hakan yayi dai dai saidai ka tuntubeta kaji nata ra'ayin tunda Naga gidan nasu da wadatar juma'a ko wata zata tayata zaman tunda kasan sha'anin yau sai a hankali kada a Kai Mata wadda za'a samu matsala".
Tunda baba malam ya fara Kora bayani Mahmud ke gyada Kai sai da ya Kai Aya sannan Mahmud din yace. "haka ne in Sha Allah zan nemi shawarar tata duk yanda mukayi zan fad'a maka, na gode" Ya fada kafin su fad'a wata hirar akan wani sabon project da suka samu daga usaid karshi gwamnatin jihar Bauchi da sukazo musu aikin plane na shekara bakwai. Bashi ya bar gurin malam ba sai wurin Tara da rabi, daya fito ma majalissar su ya nufa gurin su salisu Nan suka dunga yi masa chari akan ya zagaye ya tafi gidansa bai nemi rakiyar kowa ba ko rowar ganin Amarya yake musu, shi kuma ya Kare kansa da hujjar Shima be San da zuwenta ba kawai da yamma Baba malam yace yaje can gidan ya jira Alhaji Jafar Yana son ganinsa, Yana zuwa kuma ya ganshi da zahrar ya kawota da kansa, to wa zaya Kira Kuma ihu bayan hari.
Sunyi masa Allah Sanya Alkhairi da Alkawarin zuwa su gaida amarya sai goma ya karbi lifan din Habib ya nufi hayin banki.

Lokacin daya shiga falon shiru ba motsin komai sai ni'imtaccen kamshin turarukan wuta 'yan asali da kuma na roomfreshner masu dadin kamshi lumshe ido yayi Yana shakar kamshin.Nan da Nan yaji wata irin kasala ta rufe shi ga wani mahaukacin feeling yana bijiro masa tun bayan barinsa gidan yake fama da wani irin tunanin ta duk motsin da zeyi sai ta fado Masa,moment din yake tunawa duk da ba cikin dadin Rai yayi ba Amma ya tsaya Masa a zuciya sosai Kamar magnet haka ya d'afe Masa.
A hankali ya taka zuwa tsakiyar falon komai tsab Kamar wani mahaluki Bai shiga falon ba, harya Fara Hawa steps din da zasu sada shi da bedrooms nasu hankalin sa ya Kai wurin dining din manyan warmers ya gani a hankali ya sauko ya nufi gurin abinci ne mai rai da lafiya sai Kuma pepper soup na cow tail da hadin salad da alama na ba'a taba ba yasan aikin Ammarta ne kada kai yayi Yana fadin "wato abincin ne bazataci ba ko me take nufi? baiwar Allah ta Bata lokacinta ta bada a kawo Amma ba za'aci ba"
Dakinta ya nufa Yana zuwa ya kama handle din yaji ta a rufe, shiru yayi wata zuciyar na cewa yayi knocking wata Kuma na kwabarsa, juyawa yayi ya koma gurin dining din shi dai baze iya cin abinci Mai nauyi ba, abincin ya dauka yabar pepper soup da hadin salad din tinda bashi da yawa.
Gurin Mai gadi ya nufa yana Fadin "Ga abincin nan a samu ayi amfani dashi yayi yawa".
Da hanzari ya taso Yana fadin "To yallabai ai dazu ma Mai gidan ta Aiko dashi har Saida na bawa wasu Yara ma sauran, wannan kuma Bari na kira Mustapha yazo ya kai musu can gida madallah dai an gode da dawainya".
"Haba ba komai gashi idan yazo sai ya biya mashin dasu". Ya aje Masa 5k akan warmer din ya juya yabar Mai gadin Yana sheka Masa addu'a da fatan Alkhairi.
Saida yayi wanka sannan ya dawo dining din yaci iya Yanda yake ganin ya isheshi sauran ya Kara kaiwa Mai gadin sannan ya koma daki.
Kan kujerar desktop computer ya zauna Yana kunnawa da ita akayi masa connecting din CCTV din dake gidan, a hankali ya fara watching Yana kallon duk wani abinda ya faru a gidan wani irin murmushi yakeyi lokacin daya ke kallon dabin su da ita da yadda tasha kukanta, wani Abu daya ja hankalinsa shine yadda yaga su zilai da yadda yaga sahura tayiwa zilai dabara ta turata ciki gurin zahra, ita Kuma tana waya bayan ta gama Kuma yaga ta shiga store ta fito tana kudundune Abu a cikin hijabinta wanda be San ko menene ba, take a Nan ya Dora mata question mark.
Saida ya Gama ganin komai Dan yanzu ma littafi ne take karantawa har lokacin daya murda handle din kofar da Yanda ta wani zaro sexy eyes din ta Kamar zasu Fado kasa saboda razana, murmushi yayi Yana fadin "matsoraciya kawai wannan za'a Sha drama da ita Dan Naga alama shagwaba tabi jikinta Bata San wahala".

Zahra kuwa tunda ta shige ta rufe kofarta tayi duk abinda zatayi na al'adun kwanciyar ta, sai ta dauko littafin ta du'aul mustajaba tana karanta addu'ar barci, bayan ta Gama ta shafa shiru kawai tayi tana tunane tunanen zuci ba, memories na abinda ya faru tsakanin ta da Mahmud ya shiga dawo Mata, Dan guntun tsaki tayi tasa hannu a kirjinta data wuni suna Mata zugi, a hankali ta Fara magana Kamar Mai gudun kada wani yaji ta.
"Jarababbe kamar maye duk ya cinye min labba da harshe ya shafeni tas yana wani gurnani kamar na zaki, da wasu idanunsa da gani na fitinannu ne! Ni Zahra na gamu da gamona na shiga Tara bama uku ba, shikenan na Zama nama sai Yanda hali yayi". Hawaye ne sharrr suka zubo Mata duk lamarin ya cud'e Mata ta rasa mafita, alwala ta shige ta dauro tana ayyana gara ta kaiwa Wanda baya barci wani abu Kuma Bai taba boyuwa ba a gurinsa kukanta tasan shine sami'uddu'a.
Sallah tayi raka'a hudu ta zauna tayi istigifari da hailala da salati ga fiyayyan halitta Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w har Saida taji zuciyarta ta samu nutsuwa kafin daga karshen ta daga hannuwanta sama tana Fadi cikin raunin murya da Qasqantar da Kai ga Allah s.w.a
"Ya Ubangiji Kaine mafi sani ga abinda yake faruwa Dani, wani Abu Bai sameni ba sai da izininka na gode maka a duk halin dana samu kaina a ciki, ka zama gata na,ka lullubeni da bargon Rahamarka, ka suturtani da suturarka, ka rufa min asiri da rufin asirinka, kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka, Ubangijina ga wannan bawan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login