Showing 120001 words to 122700 words out of 122700 words

Chapter 41 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

579

da fuskar ta inda yake zaune "ya Salam". Ya fad'a a hankali, gani yayi ta Kara yi Masa wani kyau na musamman, Kare mata kallo yayi yaga daga ita sai towel a jikinta, murmushi yayi da gani Batasan da Kaya a dakin ba.
Kayan jikinsa ya cire ya Zama daga shi sai boxer short ya shige jikinta ya janyo lallausan bargon ya rufesu Yana sauke ajiyar zuciya, a cikin barci taji an rungumeta gaba dayanta jikinta ne ya dauki rawa shikenan tasan tata ta Kare shi yasa suka nemota da tsohon dare suka kawota Nan Yan ko wane irin ihu zatayi ba Mai jinta, cikin murya Mai rauni tana cracking ta Fara farin "innalilllahi na Shiga uku wayyo Allah na....
Bata katasa fadin abinda tayi niyyar fada ba taji yace "shittt...Ni ne fa cool down precious ba abinda ze sameki a cikin gidan Nan sai ikon Allah, akwai kyakykyawan tsaro".
sansanyan kamshin turarensa ne ya shiga hancinta, kokarin kwace jikinta takeyi Dan yayi Mata kane-kane so take taga zahirinsa Amma ya Hana hakan, ita mamakinta Daya yaushe yazo garin kuma ta Ina ya shigo Dan ita dai tasan ta rufe kofar nan. Dai dai kunnenta ya saka Bakinsa "ki kwanta muyi barci na gaji da yawa kin hana duniyata kwanciyar hankali kina min kisan mummuqe ko wayar ma kin haramta Mana yinta, tunda Naga alama Nima Mai laifi ne". Ya fada yana shafa gashin kanta zuwa bayanta, hannu Daya yasa Yana zare towel din data daura a jikinta da sauri ta rike tana girgiza Masa Kai.
"Dan Allah ka Bari bafa kyau muyi barcin to".
Wani guri ya taba a jikin gadon wasu irin fitilu suka Kama kamar star masu haske sosai, Bata ankara ba ya fizge towel din gaba Daya daga jikinta Yana Mata wani mayen kallo hannu tasa ta kare kirjinta cikin matsananciyar kunya tace Masa "Dan Allah ka kashe hasken Nan wallahi kunyarka nakeji".
"Ni kike Jin kunya?"
Kai ta gyada Masa, 'Well done Yanzu kuwa Zan cire kunyar nan daga idonki".
Wani bed sheet data gani a gefen gadon ta janyo da sauri ta lullube jikinta dashi tana Kara sadda Kai kasa Dan da gaske ya saka taji kunya sosai.
Wutar ya kashe ya matso sai Jin mutum tayi ya shigo cikin Bedsheet din data rufa dashi ya hanye shi ya maye gurbinsa da lallausan bargon.
"Ki hanani Zama a gurin neman abincina sannan na dawo ki Kama guduna, ai impossible wallahi muyi barcin da safe mayi bayanin".
Ya Kara mannata a jikinsa suka samu body contact da kusancin zahiri.
Sun jima yana sarrafata.Tayi laushi iya laushi dan da gaske da kishirwarta ya shigo garin tamkar mayunwacin Zaki badan tana cikin rashin tsarki ba da Babu abinda ze Hana labarin sauya salo, dan tuni ya wani manta da Alkawarin da ya daukarwa Kansa, Saida tafiya tayi nisa ya ji abinda yayi Masa cikas Dole ya saurara Mata, sun kai kusan karfe uku da rabi a haka shi Mai fad'ar barci ya keji sai gashi ya bige da Hana Mai barcin yin Bata barcin.
Sai sauke ajiyar zuciya suke su duka har lokacin hannunsa Bai daina shafe shafe ba, wani irin yanayi jikinta keyi har mararta ciwo ta Dan Fara Mata cikin dashashshiyar murya mai dauke da salon shagwabar da Batasan iya ba,ta kankame Shi jikinta na wata irin tsuma muryarta ta dishe tamkar me yin mura ta Fara magana.
"Dan Allah ka bari wallahi marata ciwo takeyi...".
Baiyi magana ba sai kakkameta da yayi kamar ze shige jikinta shima ya hade bakinsu Yanda ba Yanda za'ayi ta iya furta wata maganar ba, hannunsa ya tura Yana shafar marar ji yayi tadan tasa kamar ta Dan kumboro, hannun ta rike tana girgiza Masa Kai.
Zare hannun yayi ya dawo dashi sama yaci gaba da sabgarsa ya Kuma ki sakin bakin da zatayi korafin, suna haka har wayarsa ta Fara rera kiran sallah.
A hankali cikin muguwar kasala ya saki bakinta yana Maida numfashi da sauri da sauri gefe ya margina Yana dafe da tasa marar idanunsa a rufe, Zahra naji ya raba jikinsu ta Kara takurewa a cikin bargon wani irin tsoro ne ya lullube ta da gaske yazo Mata da wani lamari Mai girma, ita ai ko idanu bazata yarda su hada ba ai da kunya wallahi duk yabi ya tsorata tas ya lalube ko Ina na jikinta, Ashe can baya Wasa ne kawai yayi Mata yanzu ne ya nuna Mata true colour dinsa tana ganinsa salihi Dan bawan Allah Ashe shima guda ne ba gyale ba, kirjinta sai zogi da ciwo sukeyi mata yayi son ransa da jikinta.
Tana jinsa ya tashi ya shige toilet ya jima tana jiyo motsinsa, sannan taji ya fito alamun tsayuwarsa taji a Kanta,a hankali ya saka hannu ya janye bargon kankame jikinta tayi Dan daga ita sai pant Kare Mata kallo yakeyi take yaji alwalarsa na neman warwarewa, laimar hannunsa ya Dan yarfa Mata a jikinta "wash...Allah na!".
Mayar Mata bargon yayi ya shige clothset din dakin jallabiya ya sako Fara tas da hula mahadinta raka'atanul fajri yayi, jikin gadon ya matso ya Dan zauna "zanje masallaci".
A dawo lafiya tayi Masa tana kudundune Yanda take, tanaji ya fice daga dakin.
Sai ta tabbata ya Kai masallacin sannan ta yunkura ta tashi ta nufi toilet, tsabtace jikinta tayi sannan tayi wanka ta fito,lotion din data gani ta shafa sai body mist na itacen sandal wood Dana oud ta hada ta fesa kayan da zata saka ne ya zama cikas Dan bazata iya mayar da Wanda ta cire ba Kuma bazata Kuma Zama da towel ba tunda taga abinda hakan ya janyo Mata, Shawarar duba clothset din tayi idan taga Kaya sabo Kona waye zata saka, tana mamakin ace Mai gidan Nan bashi da Mata Kuma ya sakarwa abokai irin haka baya gudun a ring aikata fasadi a cikinsa, were Dan wannan sai ka shekara a ciki ba'asan kana nan ba.
Ba karamin mamaki tayi ba ganin kayan Mata masu yawa har Sunfi na wancen apartment din ba wani d'ar undies ta saka ta saka doguwar Rigar material Bata daura Dan kwalinba wasu hulina na Mata ta gani da yawa ta duba kalar ash irin flowers din jikin material din ta saka a Kanta, barci takeji sosai Dan tunda Allah yasa ya tasheta da aalonsa Bata Kara rintsawa ba shiko gogan Allah besa an raba barcin jiya dashi ba.
Harta juyo zata bar gurin taji tana son ta bude dayan side din, kayan make up ne dasu turarika shoe and bags turaren ta dauka tana dubawa duk yawanci irin nata ne sai wasu irin nasa ga Kuma kayan maza nan Lodi Lodi dasu underwears tana tsayen tana dubawa taji kawai an rungumota ta baya, ajiyar zuciya ta sauke tana lumshe ido Sam bataji alamun bude kofa ba ko takun tafiyarsa, Kansa ya Dora a kafadarta Yana Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunne "Good morning my previous".
"Morning Yayana".
Ta fada da wani salo, juyo da ita yayi suna facing din juna.
"Bude idonki ki kalleni ki fada min waye yayan naki? Wato har yanzu da sauran Rina a kaba kenan ko? Nifa bazaki tauyeni ba Ni ba wani Yayanki bane a bani special name Dina, kodan kinga mu 'yan gargajiya ne "ya'yan Alarammomi Malam soro, bamu da wayewa irin taku ko?"
Batasan lokacin data sauke ifanunta a Kan nasa ba, tana jinjina maganarsa.
"Wayewar saita kasheku".
Tayi subul da baka ta fada harga Allah a zuciyar ta tayi niyyar fada bakinta ya subuce ya fada.
"Kai! Nine wayewar saita kashemu to nida waye zata kashe din?"
Kauda Kai tayi tana Jin kunyar maganar.
*Ni ba haka nake son fada ba Bakina ne ya furta hakan".
*Ok, zomu kwanta barci nakeji tunda kin hanani barci da fitinarki".
Rigar ya zuge zif din ya cire mata ita ya barta daga ita sai undies kawai ya dauketa can ya nufi bed din da ita tana mutsulmutsultun ya sauketa ya kiya Saida ya dangana ta da saman bed din, shima jallabiyar ya zare ya janyota ya lullubesu da gaske barcin za'ayi Dan tunda ya sakata a jikinsa Bai Kara yi Mata komai ba.

*** *** ***

Tunda Ammi tayi sallah Bata Koma barci lazimi ta zauna tana yi amma zuciyar ta Babu dadi kwanan nan kusan Kullum sai tayi mafarkin Mahmud da wata yarinya budurwa Yana rike da ita da hannu Daya dayan Kuma Yana ta faman fada da wasu irin halittu mara kyawun gani, to yau ma shita Karayi Saida taga wasu mutane dattijai guda biyu sunzo sun Taya Shi kashe wadannan halittun sun tasa su shida yarinyar har wani gida sai da suka shige sannan suka juyo suka tafi.
A haka Mai gidan ya sameta Saida ya zauna ya Kare Mata kallo yasan da akwai damuwa a tare da ita sai dai tana kokarin biyewa.
"Ammin Yara me yake damunki duk kwanakin Nan Baki da walwala Sam ko kula dani ma tayi baya ko Baki huce bane har yanzu?".
Kai ta girgiza "A'a kawai dai lamari Hussain ne yake damuna kofa da Rana Daya Bai taba kirana ba ko sako ta email Bai taba Yi min ba, gashi a kwanakin nan sai wasu irin mafarkai nakeyi dashi marasa dadi abinda yafi tsaya min a Rai Kullum da wata yarinya budurwa kamar 'yar India nake ganinsa da ita Ina tsoron wani Abu wallahi na rasa yanda zanyi Dan Allah kayi wani Abu akai".
Sai hawaye sharrrr.
"Subahaballahi! Haba zainab ya Zaki ringa yi Masa kuka kinsan masifar zubarwa da d'a hawaye kuwa ko wani abun yake aikatawa ai saiya karu idan kina Masa kuka, addu'a zamuci gaba da Yi Masa nifa jikina Yana bani Yana Dubai Dan last week na samu leakage akan Yana can din Dan yayi wasu ziyarorin bazata a can harya dakatar da wasu ma'aikatansa sai dai duk kokarin a gano min masaukinsa sabo hakan yaci tura Dan ba'a inda yake sauka ya sauka ba tunda gudun hijira yayi".
Hawayen ta goge ta tashi tana ninke sallayar ta zauna kusa dashi. "Shikenan Allah ya shiga cikin lamarin ya kureshi daga sharrin zinace zinacen zamani wallahi badan komai nufin Allah bane Wanda yaso yake bawa kyautarsa danace dama bashi ya samu wannan budin ba da kananun shekaru to yanda yaso haka yake tsara kayansa, Amma ga yayunsa Nan ba Wanda ya takura musu Suma ai suna da wadatar,tunda Allah yayi muku karfin arziki waye talaka a cikin family din nan?".
Dan murmushi general yayi Yana kallon yanda take fadin magana abinda ba halinta ba inda akan twins ne sai dai wani yayi magana Amma ta zage tana fadin son ranta.
"To ya zamuyi da hukuncin Allah shi yaso ya daukaka a cikin zuri'ar da Wanda ya Isa yace a'a Ina cewa Alhaji Ishaq ne ya bashi jarin Daya Fara sana'a dasu tun Yana hannun Hajja, Amma yanzu zaki hada arzikinsu ko kusa ko alama Babu Hadi,.koni Dana haifeshi ya mallaki abinda bani da kwatqnkwacinsa, Keda Kika haifeshi kin mallaki abinda yake dashi? To kiyi istigifari ga Allah tunda shine yace Yana azurta Wanda yaso ba tare da hisabi ba,ai kin gane?".
"Na gane Allah ya Zama gatansa a duk inda yake,Amma fa yarinyar Nan ta tsaya min a rai idan Yana kusa da wannan ai zai manta da kowa ne tunda cikin bacin rai yabar gida ga Kuma kudi a tare dashi kaga sai Allah kadai ze kare shi".
Dariya ta bashi sai da yayi sosai kafin yace.
*In Sha Allah in dai Zina gado ce to Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w zuri'ar mu bazasuyi ba Ni ba mazunaci bane haka kema ba ita bace in Sha Allah.Allah baze jarabcemu da ita ba, Kika sani ko bushara ake Miki ke uwa kin samu sirika".
"Haba dai har abun ya Kai haka yayi aure ba sanin iyayensa ai kuwa da lamarin ya lalace".
'yar dariya yayi.
"Kedai kije ki shirya min breakfast daurin Aure zamuje kabba na Dan gidan sanata Abdul Aziz"

"Ok.bari na shiga kitchen din"
Ta tashi ta fice tana baza kamshinta as usual.



******


Tun idar da sallar Rukayya ta taso ta nufo part din da zahra ta kwana,abin mamaki an canza pin kofar dan ta kwada yafi sau goma Amma taki budewa. Nan da Nan taji hankalin ta ya tashi me Kenan badai wani bane ya shigewa 'yar mutane ba gashi jiya Taki Kai Mata wayarta da ba saita kirata ba, gudun kada tace sai sun kwana ya hata ta Kai mata.
Number ya Sameer ta lalubo lokacin Yana barci,
Yana dauka ko gaishe shi bata tsaya yi ba ta Fara fadin "Ya Sameer ka taimakeni wallahi tun sassafe bake kokarin shiga part din da zahra take Amma kofar kofar kamar an canza pin din na saka yafi sau goma Amma yaki budewa".
Tsaki yayi "Waike Dan Allah Ruky yaushe Zaki girma ne? to oga ne ya shigo cikin dare Nima da asuba naga text message dinsa Dan haka ki Zama ready idan na shigo saimu wuce tare Amma yanzu kada kuyi komai za'a kawo abinci".
"To ai su Iya Rahane har sun kusa gamawa baka fada min ba tun dazu".
Ok, ba komai sai a hada tunda gidan da jama'a, yauwa zuwa an Jima ki bude musu part din Nan na kusa da parking lot sai su zauna a nan tunda shima ogan Bai san ze shigo kanon ba harsu Gama su koma to matsalar madam din ce inaga ta caza Masa Kai Wai cewa fa yayi daina amsa Masa waya tayi".
"Kamar ya Bata amsa masa waya? Batasan kowaye bane da zata ringa yi masa haka?"
"Eh kusan hakan ne gaskiya"
"Allah ya rufa asiri" ta fada.
Sukayi sallama ta kashe Kiran tana dariya "su oga anzo hannu ana walagigi da rayuwar 'yan Mata gashi kaima kazo hannun yarinya tana juyaka son ranta, nasan bana raba Daya biyu saboda shi ta rufe wayarta jiya, taki magana dashi a wayar Ya Sameer karshe ma ta sakata jirgi, yes! Haka nake son irin matansu su kasance, idan suka samu wadda ta mace a kansu ta Zama sorry Amma wannan ta shuka mulkinta yanda takeso tunda Batasan waye shi ba".
Ya juya ta koma kitchen inda tabar su zilai suna aiki, tana shiga zilan tace Wai ni lafiya yarinyar Nan? naji shirun yayi yawa ko dai rakani zakiyi na gano lafiyarta kada na Zama babbar kwabo an hadoni da yarinya nayi wasarere da lamarinta".
'yar dariya. Rukayya tayi "gaskiya kinaji da matar big bro irin wannan shiga damuwa jiya fa ko barcin kirki bakiyi ba kina zaman jiranmu yau ma tun Asuba kike ta nemanta, ki kwantar da hankalin ki Aunty sirikinki ne ya taho ba Shirin wannan 'yar taki tsaye ce taki saurarensa ko a waya dole ya tsallake hidimominsa ya nufo Nigeria".
Iya Rahane ce ta aje Wukar hannunta tana duban Rukayya "kikace uban gidan mu ya shigo garin?"
"Kwarai kuwa iya jiya cikin dare ya shigo Kinga kuwa sai ki fadawa Aunty ta kauda Kai kawai gurin son ganin 'yarta ba yanzu ba gaskiya, Dan haka da an gama aikin Nan zamu bar Nan Bangaren mu koma wancan".
"Wannan gaskiya ne inba tayi dalili ba yaushe zamu shigo wannan guri harda kwana a cikinsa, Amma dalilin uwar dakinmu mun dangwali arziki ai wannan ba komai bane akan gidan da aka sauke mu a sokoto, Kai Naga inda arziki ya amsa sunansa wannan yaro uwarsa tayi farar haihuwa wallahi Nan kusa Banga mutane masu karamcin su ba, uwarsa yarinya karama sai halin girma".
Ita dai zilai sai ta rasa Wai wannan maganar dawa ake ne waye suke zance a kansa ne ita fa maganar Zahra take musu su Kuma sun kamo wata tashar Ina hadin zahra ba Wanda suke magana a kansa ko dai Mai gidan ne ya dawo Basu gane me take nufi ba, ita Zahra matar Almajirin Malam Bukar Wanda gidan zaman ma na Baba Malam ne mutanen da yaje yiwa aiki turawa suka gyara Masa shi, to Ina shi Ina wannan Aljqnnar duniyar suda aka kawosu zaman 'yan kwanaki na ganin likita.
Cikin nuna mamaki zilan tace "ikon Allah ai ban sani ba kice da anyi uwar banza gara da Kika fada min kada naje nakai kaina girma ta Fadi".
"Ai Koda kin shiga basa Nan ba a nan suka kwana ba".
Wayar Rukayya ce tayi qara ta dauka ta fice daga kitchen din shine abinda ya Hana zilai fadar abinda tayi niyyar tambayarki Rukayyar.
Hira iya rahane taci gaba da yiwa zilai a Kan Mahmud amma ko Daya zilan Bata gano ainishin waye take magana a kansa ba.

.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login