Showing 66001 words to 69000 words out of 122700 words

Chapter 23 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

586

hakan ba laifi daman shekaranjiya ne da dare na fita zanje can inda na baza ganyen yandi Dana shanya naji uwar tana surfa Mata zagi ban dai San dalili ba Amma naji ita yayar tata tana Fadin sai kije kiba Zahra hakuri Mana tunda kanwar uwarta ce ni dai Nan na barsu Dana dauko shanya ta".
"Allah ya rufa asiri kowa yayi nagari Kansa ya yiwa kuma sharri Dan aike ne duk inda ka tura shi ze dawo, bansan abinda yarinyar Nan ta tsare musu ba, bana raba day biyu da abinda sukasa Hameedar tayi inaga daga baya ta gane Bata kyauta ba shine tayi magana uwar ke zaginta".
Sun Dade suna tattaunawa.
Gurin Sha Sha daya da rabi magaji yazo ya dauki Inna maimunar zuwa gidan Zahra.
Zahra na barci Dan batasan lokacin da barci yayi awon gaba da ita ba, cikin barcin taji alamar bell din kofa ta yunkura ta tashi ta yafa Veil din rigar saman gashinta.
Tana budewa taga Inna maimuna da magaji, jikin innar ta fada kawai sai ta saki kuka Wanda ita kanta bata San kona menene ba.
" Ke matsa can da Baki rabuwa da shiririta saboda Allah menene abin kuka magidanciya dake, Dan Allah duba min Nan Mai sunan malam wannan ai rashin wayo ne koba haka ba?"
Ta fad'a Tana kallon magaji, duriya yayi Yana fadin "kumfi kusa Inna na bankwana ne tunda Idan Kika shige wannan lungun Sai baba ta gani, ni Naga ma kinyi Rana gaskiya har yanzu Baki tafi ba".

"Ai a Gombe zanyi kwana biyu gidan Dan aminiyata da nayi rainonsa to nayi Masa Alkawarin zuwa idan zan tafi".
Ita dai Zahra tunda ta kwantar da kanta a cinyar Inna maimuna Bata Kara dagowa ba, jinta a jikin innar sai takejin wani sauki da nutsuwa suna saukar mata.
Gashin Kanta innar ta Dan shafa inda gashin ya fito tana Fadin shi dai wannan gashin baisan kitso ba Kullum Yana Nan a nannade kamar gammo".
Dan turo Baki tayi tana Fadin
"Ya zanyi kinsan ba kitsuwa yake ba ko anyi idan ya Dade kwana biyu ne kawai ga zafi".
"Allah ya kyauta kawai dai 'ya'yan zamani Amma har yaushe za'a yita Zama da Kai haka? Yau Wai uwar taku tace meya samu wayarki ko an Kira Bata shiga? tasan ba rashin caji bane tunda ance Kuna da wannan abar Mai amfani da hasken Rana"
Dan Jim Zahra tayi tace ya karbe wayar ai hakan be dace ba, Sai kawai tace.
"Nima bansan meye matsalar ba kawai rufewa tayi taqi kunnuwa".
Magaji ne Wanda yaketa faman cakular waya dago Yana fadin dauko mugani ko abun minor ne".
"Bata gurina tana gurinsa ban sani ba ko dubawa ze bada ayi".
"Shu wa?"
Ya fad'a da sigar zolaya, banza tayi masa kamar bataji ba.
Tashi daga jikin innar Zahra tayi tana Fadin Bari na dawo wlh murnar ganinki ta mantar Dani ko ruwa ban kawo Miki ba". Tayi gaba innar na Fadin "dawo Zahra'u nida ba bakuwa ba".
Gaba tayi abunta.
Saida ta ciko tray babba da dangin Zaki da sanyi har sauran pepper chicken din ta zubo musu, tunda ta aje innar ke binta da kallo tana jinjina abin wannan cimakar bata mai Karamin kafin bace ko ance gida tallafin qungiya ya samu har abinci ci susuka dauki nauyin bashi?"
Ita dai shiru tayi Bata tofa ba Amma a kasan zuciyarta da maganganu fal Wanda zasu tattaunawa da 'yarta.
Ware ciki magaji yayi ya kwashi gara har Inna na Masa Dan biki.
Wayarsa Zahra ta barba ta Kira Ammah ta gaisheta itama abinda ta fadawa innar ta fada Mata game da wayar lokacin data sauke wayar harda share 'yan hawayenta, magaji Yana Mata tsiyar shatwabarta tayi yawa ita Batasan ta kusa Zama uwa ba,Inna na Taya shi.
Sai da Innar ta Gama sannan ta tambayi Zahra.
"Wai Ina Mai gidan nawa ne banji motsinsa ba tunda nazo?"
Kafin Zahra ta lalubo abin fad'a magaji ya rigata Yana fadin.
"Ai kin baroshi can a unguwar mu gashi nan suna magana da Ya Abdul Hakeem a kusa da masallaci har suka daga Mana hannu".
"Awoh to ai kasan ban waye dashi ba sai a hankali".
Nasiha Sosai da ban baki Inna maimuna ta Kara yiwa Zahra tare da kara jaddada Mata mashinmancin biyayya ga miji.
Kaya Zahra ta zubawa inna a wata babbar leda harda atamfa dasu turaruka taba Magajin ya rike mata.

******

Tafiya ce miqqqqiya daga Azare zuwa Babban mutum ta Babura jihar jigawa, direban daya dauko Mama da Asabe ya Dan juyo yana kallon Asabe wadda ta maida hankali gurin cin doyarta da kwai da suka saya a kanya babba yace ",munzo Babban mutum fa Ina zamuyi kinyi shiru alhalin kece idona tunda wannan ba yanyata bace".
"To na manta wallahi kasan da Dan Habu muke zuwa na zata shine ita dai Mama Bata cewa komai Dan niqab nema a fuskarta badan ta matsu da son ganin malam na bande din ba da ba yanda za'ayi tayi wannan kasadar Dan yanda ta fadawa Abban Itas/gadau zasu wata dubiya Alhajin yaso Bala direba ya Kaita ta nuna Masa da kawarta matar tshon Ambassador zasuyi tafiyar abinda ya Hana Bala direba kaita kenan, hanyar tinkin ta nuna Masa alamar Niger zasu shiga.
"Yanzu ke Asabe a she Niger zamu shiga shi ne kikace min kauyen Babban mutum wlh da bani da takardar ecowas da Saida na zubeku ku nemi wadda zata karasa daku kinsan kuwa yanda suke da doka da order?".
Tafiya ce miqqqqiya daga Babban mutum zuwa bande, sun Sami tarba Mai kyau daga yaran malam na ciki suna fitowa su Asabe suka shiga malam din yana zaune akan buzu da wani zabgegen carbi a hannunsa ya amsa musu sallamar su suka zauna suna gaishe shi.
Asabe ya dago kai kalla.
"Baki fad'awa Hajiya sakona ba?"
"Allah ya taimaki malam na fad'a Mata cewa tayi na kawota gurinka tazo taji Koda yanda za'ayi lamuran ne suke neman canza fasali".
Carbinsa ya Fara ja yana girgiza Kai yayi hakan kusan say uku kafi ya sauke wani dogon numfashi yana Kara girgiza Kai.
Mama cikin kidimewa ta furta.
"Da matsala ko malam?".
"To da matsalar Amma Abu mafi ban mamaki shi yaron har yanzu bana ganin komai akan Lamarinsa kwata-kwata sai yau Naga wasu mutane a Kan lamarinsa da Kuma itama yarinyar an tasa ta gaba da dafa'i shiri Kuma na gasken gaske sai dai naga wata tafiya a gaban mijin nata da alama Kuma tafiyar da Alkhairi q a cikinta sai dai idan dauke hankalinsa za'ayi daga garin kwata kwata, idan ya tafi ya kasa ko tunanin garin bare ya dawo, idan ba haka akayi musu ba ba makawa sai kin Zama 'yar kallo a gidan dan duk yaran gidan Mata ba wadda tauraruwarta ta kama kafar tata da gaske haka Allah ya yita da madaukakin Alkhairi".
Zuru Mana tayi ta kasa magana, maganar dai ita kenan Zahra tafi nata 'ya'yan.
"Malam ayi duk abinda ya Kanata inda hali ma ya rattaba Mata saki kafin yabar garin".
""Abinda ban gani ba kenan a cikin auren nasu Dan Idan shi ne ze saketa to inaga sai dai ta mutu da auren Dan Banga hakan ba a tare dashi,ni a yanda na gani a istiharata ma ya Santa batun a Nan garin naku ba Kuma da soyayyar ta Mai karfi a zuciyarsa wadda har abada baze iya rabuwa da ita ba, ayi dai hakan yanda Idan iyayenta suka gaji da jiran dawowarsa Bai dawo ba su raba auren da Kansu". Bayanin ya kwantawa da Mama hankali, ya kawo abubuwa ya bata har Wanda za'a hada da tuaren wuta a bawa zahrar Idan harta turara Mahmud ya shaqa shida Azare har abada.
Kudi masu kauri Mama t✨✨
✨✨

💎 AUREN HUCE HAUSHI 💎

✨✨
✨✨


MAMAN FATEEMAH


PAGE TWENTY FOUR (24)


_____ Tun bayan tafiyarsu Inna da magaji sai gidan ya zamar Mata shiru Bata Dade a parlourn ba ta koma ciki, da taga tunani yana neman ya dameta saita dauko qur'an dinta ta Fara karatu Saida taji Kiran sallah ta aje taje tayo alwala.
Bayan ta gama sallar ta Haye gado ta Kara A/C tayi kwanciyar ta ba tafi minti talatin da kewnciya ba taji alamar Baki ana Danna bell, tashi tayi ta nufi kofar da gaske dai bazata samu barcin na kirki ba,Kofar ta bude a hankali su Amatu ita da Aunty safiyya ne guri daya suka zauna a Dr sulaimanu Adamu model school of Hygiene inda tayi service, su Kuma permanent lecturers, rabon ta da Amatu tun ranar daurin aurenta dan lokacin da zata wuce jama'are garinsu Bata biyo ta gidan Ammah ba daga gidan Aunty Hasana ta wuce kawai. Cikin nuna tsantsar farin ciki Zahra ta rike hannun Amatu tana fadin "wlh nayi fushi Amah Ina nan Ina jama'are? Amma kikaqi dawowa ni Aunty safiyya zanyi welcoming kawai Amma ke kam dai sai a hankali kawai, Aunty sannu da zuwa". Ta fad'a Tana Basu hanya tare da karbar yaron Aunty safiyya dake hannun Amatun.

"Hakan ma na gode tunda an karbi Auntyn ai shike nan tunda ita ta gari batayi laifi ba saini da nake can kauyen mu".
Ta fad'a Tana Zama a cikin one seat dake kusa da ita.
"Eh wlh Aunty tana da excuse a gurina tunda nasan Bata Nan taje gida sokoto Amma ke kuwa ko waya fa Baki Kira kinji ya ake ciki ba".
"Kice dai ban Kira ba. Amma tambayi Sajida kiji na kirata yafi sau ashirin ma ke dince lokacin Kiran baze yuwu ba Sai ki qara narkewa".
Dariya suka saka su duka harda Aunty safiyyar.
"Wlh Amah saina rama kinci bashi, Wai na narke kamar wani danyan tuwo".
"To da mecece? mutuniyar dake somewa Kikayi fa dif kika dauke wuta".
Kyale Amatu Zahra tayi ta karasa kusa da Aunty safiyya ta zauna ta Dora Shureem a Kan cinyarta tana Fadin.
"Aunty sannu da zuwa Ina yini?"

"Lafiya kalau Amarya ya Amarcin Naga ya barbeki kanwata Masha Allah".
Dan sinne Kai tayi tana Fadin "Kai Aunty Ina wani Amarci a Nan kawai dai".
"Gulmammiya Kinga yanda kikayi wani mahaukacin kyau kuwa? Ai da gani Amarci ya tabbata a gare ki,wa Zaki kife a baibai yarinya Kar nake kallonki fa".
"Allah ya shiryeki tunda haka Kika zama, Bari ki gani".
Ta Mike da Shureem a hannunta ta nufi kitchen, saida ta Zuba musu kayan garar a plate ta dauko musu ruwa da drinks ta dauko plate ta fito tana Fadin "Amah shiga ki dauko dayan Dan Allah".
Sai da suka Gama sannan Zahra tace su shiga suga gidan, ko Ina suka shiga Fadi suke Masha Allah! a gurin fridge din dake cikin Dan Arc din dake tsakanin kitchen da dining area ne Aunty safiyya ta kasa hakuri Saida ta magantu lokacin data Kai hannu ta bude tana fadar.
"Yau ne ganina na biyu da fridge din nan naso shi kamar qaddara Amma da aka fad'a Mana kudinsa Saida na Raina kaina"

"Kai haba Aunty bakiyi niyyar saye bane".
Zahra ta fada.
'yar dariya Auntyn tayi. "Bazaki gane ba Idan ci baizo daya ba ai koshi ma baya zuwa daya".
"Haka ne kam Aunty".
Amatu ta fada, suka nufi bedrooms dinta ko Ina dai maganar daya ce Masha.
Amatu ce ke fadar "Allah ya mayar damu danshinki".
"Amin. Amma Banda kalubale irin nawa, ba Dadi Amah har gobe abun Yana damuna bani da nutsuwa ko Kankani wlh duk lamurana sun tsaya cak bani da wani karsashi irin na amarya a gidanta, komai ganinsa nake Wai banbarakwai kamar a mafarki haka".
Sai Kuma idanunta ya ciko da hawayen da taketa kokarin kada su zubo.
"Ayya haba Zahra kiyi hakuri Mana, ai zuwa yanzu yaci ace kin hakura da koke-koken Nan tunda Mai abkuwa ta abku ai sai hakuri ki rungumi abinda Allah ya Baki ki dangana wata Rana sai labari".
Aunty safiyya ta fad'a.

Parlour suka dawo sukaci gaba da Hira, rabi duk ban Baki ne Aunty safiyyar kewa Zahra da nuna Mata ribar hakuri a cikin hirar ne Amatu take fadawa Zahra sakon Sajida na tana kiran wayata Amma Koda yaushe switch off.
Dan lumshe ido tayi sannan ta bude tana kallon Amatun.
"Matsala wayar ta samu shi yasa ba'a samuna Amma in Sha Allah soon zan sayi wata, yanzu bani taki na kirata".
Wayar Amah ta Mika Mata tana dialing din number ta.
Tana dauka ta Fara mata tsugudidi.
"Yau wacce Rana Amatu ta kirani".
"Assalamu Alaikum ayi sallama Mana bestie".
Ta fad'a tana murmushi.
"Kai!!! wa nakeji haka bestie, haba Dan Allah kin kyauta kenan ba waya ba wasika kin barni a tunani kala-kala Sam na kasa samun nutsuwa". Tashi Zahra tayi ta shige ciki tana Fadin "Bari kawai bestie guy din nan ya fa karbe wayar tun ranar da Kika tafi ya dauketa da safe daya shigo, shine fa daya shigo ya tarar duk na hargitse gado ina neman ta yace tana gurinsa, ya kama min wasu zantika akan Kiran da Musbahu yayi ranar ni kuma na kasa hakuri shine yayi min Rashin mutunci Kuma ya hanani wayar".
Ta fada kamar zata fashe Mata da kuka, tambayar ta tayi yanda abun ya faru Bata rufe Mata komai ba ta fada Mata. Bata katse Mata hanzari ba har ta gama.
"Amma ban taba sanin Baki da wayo ba sai yau, Gaskiya Baki kyauta ba ko alama Ina hankalinki ya tafi kada ki Kara Koda Wasa saboda wani ki ciwa mijin aurenki fuska ai wallahi jarimi ne daya iya hadiye fushinsa bakiji a jikinki ba".
Ta fada a kufule, kit ta kashe Kiran.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana kallon wayar a zuciyarta tana fadin ji a jiki na nawa Kuma ba ze fadu bane shi yasa.
Lokacin da zahrar ta fito wasu bakin ta tarar sun shigo su biyu har Amatu ta kawo musu ruwa da drinks suna hira dasu Aunty safiyya, sallama tayi musu sannan suka gaisa Nan Amatu tace musu "ga matar gidan nan".
"Masha Allah"

Suka fada a tare sannan babbar wadda zatayi kamar sa'ar Aunty safiyya tace "mune makotanki da hannun dama sunana Hafsat Amma ana kirana maman junior, wannan Kuma kanwata ce Nuratu da take karatu a Nan Abubakar Tatari Ali polytechnic (ATAP) aiki ne ya kawo Mai gidana mu 'yan Taraba ne".
"Masha Allah! Allah ya taimaka ya bada sa'a".
Suka fada.
Sun Dan jima ana hira dasu sannan suka tafi har gate Amatu ta rakasu da ledar kayan garar biki.
Suma mikewa Aunty safiyya tana goya Shureem da yayi barci, Dan langabar da Kai Zahra.
"Wai har zaku wuce ne Kuma Aunty?".
"Eh mana zan shiga gidan fachalata data haihu bana Nan".
"Amman Banda ke dai Amah gaskiya tunda nasan kina garin Nan sai karshen wata keda jama'are".
Aunty safiyya ce ta tari numfashin zahra
"Ai ita ke driving dinmu ya zan barta a Nan ta dawo Miki special ko weekend ne".
Alamar bude kofar da akayi ne yaja hankalinsu, Mahmud ne ya shigo Yana musu sallama da katuwar leda a hannunsa, tunda ya shigo Aunty safiyya ke kallonsa ita dai tasan wannan fuskar amma ta Yaya za'ayi haka ko Kuma kama ce kawai.
A cikin takunsa na cikakken namiji ya shigo, da sauri Zahra ta nufo gurinsa tana Fadin.
"Sannu da zuwa". Tana Mika hannu zata karbi ledar.
"Da nauyi bazaki iya dauka ba".
Ya fada Yana kallon ta.
Har cikin kitchen ya shiga da ita sannan ya wuce bedroom.
Amatu ce ta zunguri zahra.
"Ke! meye hakan Kuma? Kika wani sharesa Kada dai kice min sokoncin da kike bazawa a gidan kenan ko Kuma Dan kin gammu ne kikayi wani biris dashi".
"Gaskiya Kam ki dage ki Kama mijinki irinsu tsada suke".
Aunty safiyya ta fada tana nunawa Zahra hanyar daya bi.
"Kai! Aunty Kuma ......"
Bata karasa ba Amatu ta Kama hannunta ta nufi steps din tana Fadin "kije kawai tunda daman tafiya zamuyi saina shigo Saturday in Sha Allah".
Dan raurau tayi tana kallon Aunty safiyyar.
"Na gode Aunty ku gaida gida saina zo har gida ban gajiya".
Dariya Auntyn tayi.
'Haba dai sai dai mun dawo, wannan turaren kada kiyi Wasa dashi tun daga besse na taho Miki dashi kakata ta wurin Babana take haduwa da Kanta Yana da matukar kyau sosai ba sai fada Miki ba da kanki Zaki nema".
Dawowa tayi Saida ta rakasu har gurin mota duk da mitar da Amatu ke mata, ta hadasu da kayan garar fal ledoji biyu dasu bokitan roba da mug masu kyau da plates Wanda Aunty Hasana ta bada aka kawo mata saboda Baki masu zuwa.
Saida suka fice daga gidan sannan ta dawo ciki.
Bata shiga ciki ba a parlourn ta zauna tana mitar. "Idan na shiga me zan Masa wanda yake ganina a wata Mai neman rayuwarsa".


***
Saida Amatu ta dai daita a titi sannan da Dan dubi gurin da Aunty safiyyar ke zaune tana rungume da Shureem.
"Aunty nifa wani Abu ya bani mamaki da daure Kai"
"Kamar me fa?".
"Duk gari ya dauka an aurawa zahra Almajiri k'olo saboda ita ba 'yar Alhajin bace, surutu dai gashi nan, ni Kuma yanzu Naga sabanin abinda ake fada, yaushe Zaki kalli wannan kice Yana Qasqantacciyar rayuwa irin wadda ake fada?".

"Ni Nama fiki mamaki Dan ni dai Idan ba gizo idona yayi min ba ko Kuma kama ce ta halitta tunda ance kowa Yana da Mai Kama dashi a wani gurin, da sai nace Miki M.M DANGE na gani".
"Waye hakan?".
Amatu ta tambaya.
"Bazaki gane ba Amatu wasu Family ne a sokoto masu mahaukanta kudi Nima fa sau daya na taba ganin M.M DANGEN a bikin wata cussing Dina zainab data auri Dan Family din, Kai gaskiya bashi bane inaga Kama ce kawai, amma Kuma kamar harta baci sai dai ba yanda za'ayi DANGE ya iya rayuwa a nan".
"Kamar Yaya Aunty?"

"Tab kinsan kuwa waye shi? ai inaga kaf ba Wanda ya mallaki abunda ya mallaka a duk Family din, gashi yaro matashi Kinga gidansa na sokoto ma kuwa? Banda na Abuja da sauran garuruwa, to in kuwa shine me zeyi da Dan wannan gidan ai ji zeyi kamar Yana rayuwa a kurkuku ne, bama shi bane shifa ko bodyguard dinsa abin kallon ne Suma sun Zama done fa"
Ido Amatu ta zaro.
"Kikace wannan gidan kamar kurkuku? Duk yanda na ganshi Aljannar duniya".
"Naki wasane Amatu. Allah ya kawo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login