Showing 72001 words to 75000 words out of 122700 words

Chapter 25 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

867

sauri ta mikawa Mai gadin tana fadar "in Sha Allah zan shigo Amma a fada Mata".
"In Sha Allah za'ayi fada kin gaida gida".
Ya juya da ledar a hannunsa, want abu Asabe ta radawa Mama a kunne tayi saurin tsayawa tana duban kofar da Mai gadin ke kokarin turowa.
"Malam Bismillah".
Ta fada Tana komawa tare da dauko Abu a cikin Jakarta.
Dawowa yayi Yana Dan sadda kai, kudin da Bata San ko nawa bane Mika masa.
"Ga wannan ba yawa Dan Allah a tabbata sakon ya shiga Hannunta komai dare"
"In Sha Allah Hajiya da shi zata shiga ciki, Allah ya Kara sutura na gode madallah".
Ya fada Yana qara gyara rikon ledar da kyau.
"Hajiya ta haka akeyi Nan gaba ko wani aikin kike bukata da gudu zeyi Miki kinsan su bugun Abuja ba bayanin da basa ganewa in dai kina ungo to zance ya Kare Abu sai dai in Baki nema ba, ai Nima goben da sako zan taho Masa Naga alamar kamar zeyi son abin duniya jifa yanda yayi caraf ya karbe kudin daman kamar jira yake.
Dariya sukayi gaba daya harda tab'awa, suka nufi motar data kawo su.

******

Tafiya suke yi Yana rike da Hannunta da nasa dayan, dayan Kuma Yana tuki cikin kwarewa lokaci lokaci Yana Dan matse hannun, ganin sun dauki hanyar barin garin yasa Zahra ta Dan dube shi.
"Wai Ina zamu ne?".
"Siyar dake zanyi, kinji yanda nake samun makudan kudina cikin sauki, duk garin da naje haka nakeyi na duba kyakykyawar mace na aura idan an sake Dani sai nabi dare na gudu nabar garin daman ba Wanda yasan daga inda na fito, bare ke yanda Allah ya surantaki da sura ai ke sai nafi samun alheri a jikinki".
Ya fada Yana wani daure fuska.
Zuruzuru Zahra tayi ganin fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin Nan da Nan jikinta ya dauki rawa, duk sanyin ACn dake motar Saida gumi ya rufeta, kallonsa ta Karayi still dai fuskar kamar bai taba fara'a ba a duniya.
Jikinta tsumar ya karayi kamar ana kada Mata gangi, cikin sarkewar murya ta Fara magana bakinta Yana rawa.
Me nayi maka zaka cutar Dani?".
Rage gudun motar yayi cikin duhu, a hankali ya tssyar da motar, Zahra rufe idonta tayi take hawaye suka wanke mata kumatu.



✨✨


AUREN HUCE HAUSHI


Maman Fateemah

Page 26.



________Sai da ya gangare sosai sannan ya kashe motar, chak ya daukota kamar 'yar Baby ya rungumeta, dai dai kunnenta ya kai bakinsa ya hura Mata iska duka tsikar jikinta ta tashi duk da tana cikin halin rudu bai Hana sakon zuwa ba.
"Ki rufa min asiri ada ace satoki nayi Nan da Nan kin rikice nayi Miki Kama da masu irin wannan d'abi'ar? Wlh zolsyarki nakeyi haka Zaki shide min ki Kira min ruwa daga fita unguwa mu bige da kwanan Asibiti cool down idan na sayar ai Nina kashe kaina".
Ba zato taji ya saka harshensa Yana lashe hawayen Yana Wasa da harshensa a saman idanunta, qanqameshi tayi, "Dan Allah ka bari".
"Na bar me?"
"Hakan ba Dadi".
"To da cewa nayi kiji Dadi? Ni nasaka kukan Kinga ai shanye hawayen ya kamani kada muje inda zamu a juya min baya".
Ya fada yana shinshinar gefen wuyanta.
" Kiyi hakuri bazan Kara ba tunda wannan idon naki Mai arahar kuka ne Ni zanga yanda za'ayi idan abin kukan ya samu".
"Cewa fa kayi ka Saba halinka ne ka Saba yin hakan Kuma fa fuskar ka ba Rahama a ciki kamar Mai tsaron gidan wuta".
"Kai innalillahi! Mai tsaron wuta ni din?" ya fada yana fiddo idanu waje
"A'a ba Kai nace ba kamar nace".
"Ba cinya ba kafar baya"
" Nifa nayi ne Dan Naga idonki, idan kina cikin halin tsorata yana sakani nishadi".
Wayar sa ce ta Fara vibration a jikinsa, Dan zameta yayi daga jikinsa ya dauko wayar ya duba tsaki ya d'an Yi.
"Dan matsala kawai".
Ya fad'a yana saka wayar a handsfree.
"Ya akayi Hayatu".
Dariya ce ta kwacewa Sameer Wadda Bai shirya Mata ba.
"Wlh zan kashe, wato abin dariyarka na Zama ko?".
"Sorry sir wlh ji nayi gaba daya tazo min, Kuma ko sallamar da nayi baka amsa min ba".

"Ka Fadi abinda zaka Fadi Kona kashe da gaske Kuma sallama na amsa Kaine dai bakaji ba, duk safiyar Allah baka tashi kirana ba sai yanzu da tsohon dare salon ka Hana mutum rawar gaban hantsi, na fada maka idan Ina bukatar Abu ni zan nemeka Amma tsabar saka ido sai ka kirani ni, to fad'i meya faru? Ina jinka".
Ya fada Yana maido ta jikinsa.
"Game da maganar tafiyar Nan ce anya zanje kuwa wlh jiya danaje sokoto daukar wadannan hardcopy din na shiga gurin Hajiya Inna muna cikin magana saiga uncle Mustapha ya shigo a sukwane bansan wane minafikin bane ya fada Masa nazo garin ba tunda bana zuwa lokacin da suke gida, ya tasani gaba da sababin nasan inda kake ina kallon su suna walaqiqin nemanka Amma nayi mirsisi naki fad'a musu komai, Ni Ina ta faman lallaba mutuniyar taka amma Saida Uncle mustapha ya Bata lamarin Dan wlh kuka take da hawayen ta bibiyu tana fadin Dan Allah na fada Mata idan mutuwa kayi saita hakurw tasan ita kadai zata nesanta ka da ita, wlh yanda ta bani tausayi da bude aiki kawai zanyi sai Kuma na tuna da warning dinka kawai na fasa, Kuma wlh yanda uncle yayi ba abinda ze Hana shi bibiyata ta karkashin kasa ban sani ba a gida da waje amma ya kake ganin za'ayi? Numfashi ya sauke me karfi yana Kare matse zahrar a jikinsa har Saida tayi 'yar karar Jin zafi.

"Karar me nakeji a kusa da Kai ne?".


"Ina ruwanka tsabar saka ido, to madam ce a kusa Kona baka ita kaji for confirmation, a'a Barta a gaisheta".
Tana jinka a speaker wayar take, ka Bari kawai Zancen baze yuwu ta waya ba idan Allah yasa na shigo sai mu tattaunawa Kuma ka tabbata komai ya kammala kafin na shigo goben in Sha Allah"
"Noted, in Sha Allah a gashe min da ita sosai a fada mata Batool tayi ta kiranta dazu ba'a dauka ba".
"Ina ga a gida ta baro wayar ka ganta Nan sai rigima take zabga min irin tasu ta shagwababbun 'ya'yan larabawan" ya fada yana dan matse dantsen Hannunta kadan.
"Wash Allah na da zafi fa".
Ta fada tana Masa wani kallo Mai ma'anoni kala kala.
"Allah ya bamu Alkhairi"
Sameer ya fada Yana kashe wayar Bai jira yaji abinda Mahmud din ze fada ba.
"Kinga kinja ya katse Kiran bamu gama bayani ba irin wannan Abu haka ai sai ayi zaton muna hanyar shuga wata nahiyar ne".

Sunne Kai tayi a jikin kirjinsa, "Dan Allah ka Bari ni me nayi,".
"Ba komai".
"Bayani zakiyi da yaren garinku yarinya".
Gurin zamanta ya maida ta sannan ta tada motar suka koma kan titi, tunda zahra ta koma gurin zamanta take Masa kallon tukuma da neman Karin bayani.
Amma saiya fuske abunsa kamar be gane ba, Yana ta faman tukinsa ko a jikinsa. Zaranda hotel taga sun shigo, kallon mamaki tayi Masa a kasan zuciyarta tana tunanin me kuma za'ayi a Nan shida yace unguwa zata raka shi to Wai mema ya hada shi da hotel ne? Gurin da aka tanada don parking ya nufa ya kashe motar.
Fitowa yayi ya zagayo kofar da tare zaune ya bude ya Mika Mata hannunsa ta Kama ta fito.
Kulke motar yayi ya jata suka nufi ciki, a Hanya suka hadu da wani security da gani akwai sabo sosai a tsakaninsu.
"Ranka ya Dade an shigo lfy?
Ya fad'a Yana kallon Zahra a kaikaice.
"Lafiya kalau Ibrahim ya aikin?"
"Lafiya kalau yallabai".
Ya fada Yana niyyar wucewa yana Kara kallon Hannunsu dake sarke Dana juna.
" Ibrahim gafa madam Dina Yau na kawota taga mafakata".
Ya fada Yana Dan murmushi.
Dawowa yayi Yana fadin.
"Masha Allah yallabai Allah ya bada zaman lfy, ai Dani aka daura Auren babban masallacin juma'a, madam sannu da zuwa gurin namu".
Ta amsa ta gaishe shi ya amsa yana Mata Allah Sanya Alkhairi sannan sukayi gaba, dakin da yake kusan mallakinsa ya bude musu suka shiga lumshe ido Zahra tayi Dan wani special kamshi da sanyi A/c ne ya bugeta, yanayin ba Karamin Dadi yayi Mata ba, direct kan sofa ya nufa da ita tare suka zauna har lokacin Bai sakar Mata hannu ba. Falon tabi da kallo ba karya komai yaji Dan an kawata shi sosai.
"Wai me zakayi a nan?"
Ta fada tana masa kallon ido cikin ido.
"Me kikeci na baka na Zuba? ai dai muna tare dake ko! zakiga abinda zanyi yanzu ki zauna ki dan tayani aiki kafin naje unguwar ku gurin iyayena sallama".

"Dan Allah kaje Dani "
"Kai ! Naje dake Ina? Lallai kina so na amsa tambayoyi kenan kwanan ki nawa rabonki da gidan? Kawai na kawoki Nan ne kisan dakin yana cikin abubuwan da suka zamar min abin tunawa a zamana na garin Nan kinsan saboda ke na kama shi ya Zama permanent dakina tsawon shekara kusan biyu da nayi a garin nan?".
Galala take kallonsa.
"Saboda Ni kamar Yaya?".
Wani kallo yayi Mata Yana Dan taune gefen lips dinsa na kasa.
"Naki Wasa ne yarinya,Wai kin zata daga cewa an bani Mata saina karba kawai? Niga sarkin tausayi ko to Daman Nima Ina son kayana kawai dai kinfi karfina ne na mikawa Allah kukana Ina zaune Kuma ya juya lamarin gareni tunda shiya hadani dake a inda ban zata ba ya cusa min soyayarki lokaci daya nasan baze Bari na shiga gararin rayuwa ba, duk rintsi ze kawo min mafita sai gashi ya kawo min lokacin da har nayi given up Ina kokarin barin garin idan na shaida dauri Aurenku, amma fa da Allah kadai yasan meya faru yanzu to Sai ya taqaita cikin shikimarsa".
Agogon hannunsa ya duba, Zahra tana kokarin magana ya katseta.
"Adana tambayar saina dawo Kinga idan na biye Miki ba inda zan fita, a 'yan kwanakin nan kin mayar Dani wani parrot sai magana nakeyi ba comma ba full stop, wlh kin canzani kwata-kwata da Hajiya Inna zata ganni Ina zuba haka hum..".
Ya fada Yana daukar luggage din daya shigo da ita da dayan hannun dayan Kuma ya mikar da ita tsaye.
"Zo muje ki tayani shiryawa".
Nokewa tayi tana Dan ware idanunta. Shiryawa kuma? Kaje kawai Ni ina nan".
Gaba yayi yaga alama da gasken ze iya shashancewa a gurinta.
Komawa tayi ta zauna tana jujjuya lamarin bawan Allahn nan sai wasu maganganu yake fada Mata ba tare da fashin baqinsu ba.
Kamshinsa shiya fada Mata wanzuwarsa a falon, a hankali ta dago Kai ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a hankali Dan ba lallai yaji ba.
Gurin da take zaune ya Dan tsuguna a gabanta ya Dora Mata laptop din dake hannunsa da wasu takardu da list na sunan mutane kusan dari da ashirin da biyar daga local government hudu Alkakeri, Jama'are, Zaki da Dass, karkashin makarantun Allo zasuyi step down training a Nan Azaren schedule ne na aikin da payment dinsu.
Ta dago zatayi magana ya Dora Mata yatsa a biki "kiyi kawai idan na dawo kin tambayeni duk abinda kike bukatar sani bana son nabar garin Nan aikin Nan Bai kammala ba".
Ya Mike fuskarsa ya kawo dad da tata ya Bata light kiss a gefen kumatunta, saina dawo take care". Ya nufi kofar da sauri da key din motar a hannunsa.


Harya rufe kofar Bata dauke idonta daga gurin ba, ita fa mutumin Nan ya Fara Bata tsoro mutane suna daukarsa wani Abu daban ita Kuma tana ganinsa wani Abu daban.
Ta Dan jima Tana sakawa da kwancewa daga karshe ta watsar da komai ta dauki laptop din ta shige cikinki bedroom din ta Haye lafiyayyan gadon ta bude ta shiga aikin inda Allah ya taimaketa yaci karfin aikin karasa Masa zatayi.


*******
Lokacin da Mahmud ya fito Ibrahim da wani sulaiman ya Kira ya Basu aikin kula da dakin da Zahra ke ciki duk da yasan suna da matakan tsaro sosai Amma hankalinsa Bai kwanta ba sai da ya Kara Mata da nasa, gurin motar ya nufa bayan ya zauna ne ya Ciro wayarsa ya bude ta haka Nan ya shiga CCTV da akayi connecting da wayarsa.
Hotunan ne suka fito rababa na dakinta yayi zooming qura Mata Ido yayi lokacin data fito daga wanka tana daure da Karamin towel fararen cinyoyinta sunyi wani sambal dasu ta Kai ta kawo Yana kallonta harta gama, tunda ya Fara kallon yake sakin wani Nishi kadan kadan Dan da gaske ta yamutsa Masa tunani ji yake kamar ya zubar da Alkawarin daya daukarwa kansa a kanta, komawa yayi baya na kofar gate ya dauki hankalinsa ganin wata mota mata sun fito sun dauko wani Abu a Leda sun nufi gate din gidan full screen yayi da gurin da suke ya waye da mama amma Asaben çe bai ganeta ba yana kallon duk abinda sukayi har Zuwa lokacin da Asabe tayiwa Mama rad'a a kunne ta Kira Mai gadin ta bashi kudi suka juya
da yanda suke kwasar dariya har da tabawa kamar yara sai abin ya bashi mamaki, meya kawo su gidan su kadai ga Kuma motar da gani ta commercial ce, girgaiza Kai kawai yana tunanin abinyi.
Da gurin malam ya fara zuwa ya Dan jima tare dashi kafin ya aje Masa Alkhairi yayi Masa sallama, Yana Kara yi Masa addu'ar samun nasara a tafiyar da godiyar Alkhairnin daya bashi, Habib ne ya Dan kalli Mahmud din bayan sun fito Yana tambayarsa..
"Da gaske baka fad'awa Baba malam ba inda zakun kada fa yaji daga baya yayi fada yace ka tsallake kasa baka fada Masa ba.
Kafadarsa ya dafa.
"Kada ka damu da kaina Zan fada Masa in sha Alllah".
Tare sukaje gidansu Zahra inda suka Dace suna kokarin yin knocking sai magaji ya fito, daga gani wani gurin zaya yanda yayi Shar dashi.
Gaggaisawa sukayi kafin Magajin yayi musu jagora zuwan gurin Abban nasu. Anan falon ganawa da bak'insa suka sameshi, sun gaisa Sosai a Nan Mahmud ya fada masa tafiyar da zeyi, Abban yasa Albarka soshi.

.
✨✨
✨✨


AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH


Page 27



_____Dan Jim Mahmud yayi kafin ya Dan muskuta kadan ya Kara sadda kansa kasa.
"Abba Dan Allah ko za'a taimaka a bamu Aron daya daga cikin masu aikin Nan Mata su tayata Zama kafin Allah ya dawo damu". Ya fada a ladabce
Dan gyaran murya Abban yayi Yana fadin "Hakan babu laifi kayi tunani Mai kyau baza'a bar yarinya ita kadai ba gara da babba, ba komai kome kenan da safe za'a turo wadda zata zauna da ita, Allah yayi Albarka ya bada sa'a"
Sun jima suna Hira da Abban har suke fada Masa harkar kayan spares na kayan motocin da zasu ringa saidawa, Albarka ya sanye musu sannan sukayi Masa sallama, har sun Kai kofa Abban yace Bari ya fadawa Ammah ku shiga ku gaisa, a waya ya kirata ya fada Mata sannan yace su karasa ciki.
A kofar gate na shiga ciki suka samu Musaddiq Yana jiran su, cikin ladabi ya gaishe su Yana tambayar Mahmud Aunty Zahra, hannunsa Mahmud din ya Kama Yana bashi amsa har suka shiga part din Ammar.
Sallama sukayi tana zaune a parlourn, sallamar ta amsa tana fadin. "Su Habib ne sannunku Bismillah".
Ta fada tana nuna musu gurin Zama.
Basu zauna a kujerar ba sai suka zauna a Kan carpet.
"Ina yini?"
Suka fada a tare, "lafiya kalau ya wajen malam?"
"Lafiya kalau yace a gaisheku".
"Masha Allah muna amsawa, Allah yayi Albarka, yayi muku jagoranci cikin dukkan lamuranku, ayi ta hakurin Zama da yara".
Ta fada a kunyace Dan har ga Allah tana Jin nauyin yaron da kaunarsa saboda karamcinsa da halin fattako daya nuna lokacin da aka bashi Auren zahra da Rana tsaka ya Kuma sa hannu biyu ya karba.
"Amin na gode ba komai, zahrar tace ma a gaisheku, kuma nazo ne nayi muku sallama zanyi tafiya ne amma in Sha Allah bazan jima ba, na fadawa Abba a samu wadda zasu zauna tare kafin Allah yasa na dawo".
"Masha Allah. Allah yayi taimako hakan baze gagara ba ko can gida Mubi Sai a samu wadda zatazo su zauna tunda akwai yaran sosai ba sai an dauko bare ba tunda yau din ta Zama wata iri Amma kafin tazo sai su Fara Zama da zulai tunda Bata da matsala"
"Godiya muke Allah ya kara sutura" Habib ya fada, suna mikewa har lokacin Autan Ammah Yana jikin Mahmud a zaune. Addu'a Ammah take musu har suka fito Nan da nan wani rauni ya shigi Mahmud haka tasa Umman take Masa a duk lokacin da ze shiga wurinta bakinta baya gajiyawa da Yi Masa addu'a, duk kewarta sai ta rufe shi, "kaimu gurin Mama mu gaisa".
Mahmud ya cewa autan Ammah.
Part din Mamar suka nufa, Musaddiq ne yayi knocking har sau biyu ba'a bude ba Kuma suna jiyo maganganu da sound din tv.
Habib ne yace "mu tafi Dan Allah yaushe zamu tsaya kamar wasu 'yan maula". Har sun sauka daga steps din balcony din sannan aka bude kofar, Asabe ce ganin Autan Ammah da mutane yasa ta fito tana fadin ku shigo Dan Allah wlh bamuji ba sai daga baya Salma ke fadin Kamar taji bugun kofa".
Habib ne yayi farat yayi magana "ai ba komai a gaishe da Hajiyar Daman mujin Zahra ne ya shigo ya gaishe ta".
Sukayi gaba suka barta a tsaye.
Ciki ta koma jiki ba kwari.
Mama ce ta kalleta.
"Wai su waye Naga kin fita Kuna magana dasu ne Kuma Basu shigo ba?"
Zama tayi kusa da mamar, "sirikin ku ne inda mukaje basa Nan yazo gaishe ki da alama Kuma sauri suke tunda sun jima a tsaye ba'a bude ba".
"Wai kina nufin Mahmud mijin Zahra?"
"Shifa sunce a gaishe ki, da alama sauri suke Dan har sun fice.
Baki Salma ta tab'e tana fadin. "saura kiris dai uban kowa ma ya rasa, ba dai kunce kun Kai turaren wutar ba, yanda aka wayi gari aka ganshi da hakoransa talatin da shida haka za'a wayi gari yayi layar zana inga ta qafafar da ake anyi aure, auren ma Dan jeka nayi ka da ba wani armashi yayi ba, Shima Abba Dan ya ganshi handsome ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login