Showing 99001 words to 102000 words out of 122700 words

Chapter 34 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

889

magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha Allah zasu narke Koda na aikine zebi jinin al'ada ya narke ya zube".
"To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka".
Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama.
Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje Zahra tana barci sun gaisa da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi.

****


Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar suka fice sun Kai ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya dakatar da mutum hudu ya sallami mutane biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin tafiya tayi nisa Kuma baya bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki, zuwan Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai takanas din ya taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials da akayi Wanda suke zargin ba'a biya kudin harajin kasa ba a tun farkon bude kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta wibeside nasu Amma sunqi yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru.
Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi matukar gajiya sosai Koda yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na Zayyan da Habib su sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa.
Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake tare dashi Nan take tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga, Bai saurari gaisuwar da yake Masa ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da nayi bashi da anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da tsohon Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda throughout yau ban kirata ba nayi busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make text".
"Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?"
"Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani information akan komai ba".
Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya Kira shi.
"A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa.
"Wai meke fatuwa ne da Zahra?".
"Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam yace na kaishi Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana barci Amma idan an jima zan koma na qara dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka naji Abban su Yana fadin Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan sanar da kai Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin".
Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa.
Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka yasan wayar na gida Basu dauka ba.
A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama da Asabe Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje duniyar kanwar Babar su Asaben, shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da wayar Amman a.hannu Yana game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah, batare da Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo Mahmud ze Kira ba.
Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar yasa Ammar fadin "wa ake nema ne".
"Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude wayar ba muna aiki sai yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti, Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata fatuwa ba".
Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba.
Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci takeyi, ya akayi suka fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din ta zasu bincike a Kai".
Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa.
"To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano zasu dubata sosai tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka".
Sukayi sallama.
Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita tamkar mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau.
Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin yanayin ciwon nata gashi abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya barta da jangwam yanda aka Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi Kuma yayi masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji ance harda motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan".

Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana fada ne dan ta Bata Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra tana gyara Mata hannunta da aka saka mata drip, itama ko tari be kunce Mata ba bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace.
Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa.
"Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon Allah ba yaron Nan guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake Kar bashi da duhun jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya barta, idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu jinjinan dangi kana ji a sheganta yaro
ko yarinya".
Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo suka juyo tana kallon Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini har dakin mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin".

✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI


✨✨✨

MAMAN FATEEMAH.


Page 36


______Zahra tana Gama fadawa Asaben abinda ke cikinta ta juya musu baya, ko banza bazata kwana da fushin zuciya ba, dan tasan idan ba ita tayi magana ba Babu abinda Ammah zata ce Dan sau da yawa idan irin haka ta faru ko kallon Mama batayi sai dai ta bawa banza ajiyarta.
Daga Asaben har Mama ba Wanda ya Kara magana,haka Ammar ma da Zilai ba Wanda ko tari ya kuncewa, Auta kuwa wayar mamar ya dauka yaci gaba da sha'aninsa.
Shiru dakin ya dauka kamar mutuwa ta ratsa, sallamar Abdul Hakeem da Abba ta katse shirun cikin nuna tsantsar duniyanci Mama ta tashi da sauri tana fadin "Abba har kun karaso sannu da Zuwa" tana gyara Masa kujerar kusa da gadon.
Sai da ya zauna sannan ya amsa gaisuwar dasu Zilai da Asabe ke Masa suna jajanta masa, suka gaisa da Abdul Hakeem sannan suka fice daga dakin.
Mama ce ta Fara gaishe da Abban kafin Ammah ma ta gaishe shi, sannan Abdul Hakeem ya gaisu dasu Ammar Yana tambayar Mai jikin.
Zahar ce ta juyo tana fadin. "Abbana sannu da Zuwa, ina yini?".
"Yauwa uwata lafiya kalau Alhamdulillahi jiki yayi kyau".
"Eh Abba Daman Kai nake jira kazo kayi musu magana su sallameni mu tafi Nina warke na gaji da Asibitin tunda sunyi min hoton da gwajin da safe mun dawo mu karba bana son kwanan gurin Nan".
Ta fada tana hade rai.
"Eh Nima abinda ya taso ni Kenan maganar tafiyar taku gidan ne Dan yanzu haka daga office din doctor din muke sun bamu referral Zuwa Aminu Kano kamar yanda mijinki ya bukata yace da safe zaku tafi kiga gynecology doctor ayi bincke tunda ance kin jima kina fama da matsalar".
Kafin Ammah tayi magana Mama ta rigata.
"Wane irin Kano Kuma ana zaune lafiya, Wai ciwon har ya Kai haka ne idan Asibitin ake son canzawa aje Bauchi Mana Amma har kano akan ciwon mara kawai".
Dan murmushi Ammah tayi Bata ce komai ba.
Abban ne yace. "Yanzu kina nufin na Kira shi nace masa abinda ya fada baze yuwu ba Kenan ko Kuma Yaya kike son ayi?".
Shiru tayi Bata ce komai ba. Ammah ya kalla "kinyi Shiru ko kema hakan ne nufinki".
Kai ta girgaiza tana fadin "A'a tunda ga yanda ya fada ai shike da iko da matarsa ita da waye zasu tafi kanon?".
"Yace Sameer ne zezo sai zilai ta rakata haka dai ya fada min yanzu da Daren nan"
" To Allah ya kaimu yanzu tafiya zamuyi ke Nan?".
"Eh haka ne, ku kuje Abdul Hakeem ya mayar daku gida kafin ya dawo ruwan ya Kare sai na raka uwata gida" ya fada Yana murmushi.
Sororo Mama tayi Jin Abba da kansa ze maida su Zahra gida.
Badai ta tofa ba Amma a ranta taji ba dadi. Tun kafin Ammah ta dauko hand bag dinta Mama ta fice daga dakin.


******
MAHMUD
Bayan sun gama waya dasu Abba, Sameer ya Kira harta katse ba'a dauka ba sake Kiran yayi tana Fara ringing ta dauka.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Ya fada Yana Zama kusa da Fateeha tana shayar da jaririn su.
Daga can Mahmud ya amsa sallamar ya Dora da fadin "gobe in Allah ya kaimu ka shiga Azare ka taho da madam zataga doctor a Nan kanon na Kira doctor Haseena za'a kawo patient dina".
"Doctor Haseena fa! ita zata duba maka madam din?".
"Eh Mana ko da matsala ne?".
"A'a gani nayi kada taga anyi Mata cin fuska".
"Ba wani damuwa kawai,do what I said".
"Ok. In Sha Allah".
"Kada ka kaisu gidanka a kaisu gidan dake Nan DAWAKI ROAD su zauna har su Gama abinda zasuyi su koma".
"Kana ganin Bai musu girma ba kuwa? dana karkasara aka kaisu yafi kusa da Asibitin ma akan na Nasarawa GRA".
"A Nan nake son ta zauna kake maganar girma har wani babban gida ne ka barta ta saba da Zama a irinsu tun yanzu Kai dai kasan kuma abinda zaka fada Mata, a Kai musu duk abinda ya kamata sai dai na fada ba kayi komai kawai, ka fadawa momi ta Basu house maid daya su hadu da tata sai su ringa aikin tare, kayan sakawa dai nasan ba matsala ka Kira Rukayya ta duba abinda ya kamata sai taje ta sawo, ka Bata card din master bedroom na kasa ta sauka a nan.
"Shike Nan za'ayi yanda kace, amma baka tunanin taga wata shaida data danganceka a gidan?"
"Gaskiya bana tunanin akwai wata alama dake alamtani da gidan".
"Anyway, Allah ya kaimu goben, takwaranka na gaisheka".
"Oh sorry a shafa kansa sai nazo ganinsa, kaina ne ya dauki zafi".
Dan murmushi Sameer ya kashe Kiran Yana kallon Fateeha dake Masa kallon Karin bayani.
"Oga ne, Kinga yanda ya shiga damuwa kuwa nifa Banga abinda oga ya damu dashi ba irin yarinyar Nan idan Kika cire Iyayensa to ba na biyunta, ai ban Gama sarewa da lamarin sa ba saida ya nemi guri ya zauna a dakin kofar gida na almajirai duk da gurin bashi da wani aibu". Baki bude Fateeha ta bi Sameer da kallo "dakin Almajirai fa tace shi ogan da kansa? Tab lamarin Azimun ne, Allah ya bamu ko Rabin yanda tayi sa'ar sace zuciyar jarimi kamarsa Wanda Mata ko kallo basu isheshi ba".
Lakuce Mata kumatu yayi Yana fadin.
"Waya fada miki ba'a Miki so irin Wanda ake mata?" 'yar dariya tayi kawai tasan zance ne inji 'yan magana

*******

Lokacin da Ya Abdul Hakeem ya dawo ruwan ya qare har an cire Mata.
Cikin marairaita Zahra ta kalli Abban da Ya Abdul Hakeem.
"Dan Allah Abba ka tafi Dani gida wlh jiya nasha wahala gashi ba kowa a kusa dani kada na mutu Ni kadai a daki".
Saita saka Masa kuka.
Baki Ya Abdul Hakeem ya bude alamar mamaki.
"Ke! Amma wallahi wannan dai abun kunya ne ki wani kama kuka, kin manta yanzu ba da bane kema fa soon Zaki Zama uwa".
"Ungo Abdul uwata kake fadawa haka a gabana? Fita ka Kirawo zulaihatu ta tattara musu magungunan Nan sai mu tafi can din"..

Dariya yayi ya fice Yana mamakin Abba yanda yake nunawa Zahra soyayya fiye da kowa.
Ba zato ba tsammani Amma taga zilai ta shigo da Kaya a hannu Zahra na biye da ita.
"A'a ku kuma ya haka Naga Abba yace ze rakaki gida sai Kuma gaku a nan?"
Maganar Abban Ammah taji a bakin kofar parloun.
"Ni nace ta taho gida tunda batajin dadi Kuma gida su kadai, gashi Mai gidan nata yace goben zasu wuce kanon gara su kwana a Nan kawai tunda ke dai ba can zaki bita ba gara su tafi a gaban ki".
"Ok, ai ban sani ba nayi tunanin ko gaban kanta tayi nasanta da kulafucin gida ganin ta samu dama zata iya fakewa da haka ta taho kaima Abba kasan halinta"..
D'an Bata fuska tayi "Kai Ammah Dan Allah fa....."
"Kinga uwarta wuce ki kwanta ki huta Keda Baki da lafiya gida dai ai na danki ne, ba Mai hanaki shigowa Zan Kira shi Mahmud din na fada masa ".
"To Abba na gode".
Ta fada tana shigewa cikin Zilai ta bita da ledar magungunan ta.

Abban Bai jima ba ya fice saboda ya baro mutane masu son ganinsa da yawa a kofa.
A bakin kofar bedroom din Ammah suka had'u da zilai tana kokarin fitowa.
"Ku kuma sai koyo gudun hijira bakwa tsoron maganar mutane masu jiran k'iris su karawa miya gishiri?".
"Kayya Ammah idan za'a biyewa maganar mutane ai ko ruwa ruwa ka shiga sunce ka tada k'ura, Kuma ma waye ya ganta Kuma gobe da safe zamu wuce Kano idan Allah ya dawo damu ta wuce dakinta".

Zahra na shiga ta fada toilet Dan babu abinda take bukata sama da wanka du ji take jikinta na warin Asaibi.
Ta jima tana zubawa kanta ruwa kafin ta fito, sabuwar rigar barci ta dauko cikin kayan Ammah ta saka, ta dauko zumbuelen hijabin Ammah ta Fara sallah.
Ammah ce ta shigo dakin lokacin Zahra ta Idar da sallah Tana addu'a, sai da ta shafa sannan ta juyo tana fadin.
"Sannu da dawowa Ammah".
"A'a ke za'a yiwa sannu, ya jikin naki?".
"Da sauki sosai nifa da Abba ze fada Masa bama sai munje wani Kano ba, na warke tunda Daman na Saba duk wata inayi wannan ne kawai ya matsa min sosai".
"Kamar Yaya Abba ya fada Masa shi wa za'a fadawa?".
Ammah ta fada tana kallon zahrar, Baki ta turo tana fadin. "kema Ammah kin sani fa kowa nake nufi".
Dan murmushi tayi kawai.
"Ki Kira ki fada Masa bazakije ba Mana sai Abba ne ze Miki tafinta, tunda yace ga yanda yake so ai haka Zaki hakura kuje a duba ki tunda Naga alama Nan din be kwanta Masa ba, Kuma dazu naji kina maidawa Asabe har da Mama magana tona Hana kada na k'ara Jin makamanciyar magana irinta daga bakinki, ki bar mutum da halinsa kedai ki Zama me kauda Kai kawai ki Kuma rike Addu'a takobin mumuni ce kuma hassada ga Mai rabo taki ce".
"Kiyi hakuri Ammah in Sha Allah bazan Kara tankawa kowa ba,gani nayi basuji kunyar maganar a gabanki ba shi yasa na rama Nima".
Knockig da Sallamar Abdul Hakeem ce ta dakatar da abinda Ammah zata fada. Ammah ce ta amsa sallamar ta bashi uzinin shigowa.
Sannu da dare ya Kara yiwa Ammah sannan ya mikawa Zahra wayarsa dake Hannunsa da alama vedio call yakeyi, Yana fadar "gashi Mahmud zeyi magana dake".
A d'an kaikaice ta kalli gafen da Ammah take kafin ta Mika hannu ta karbi wayar.
Tana karba Ya Abdul Hakeem ya juya, Ammah tabi bayansa tana Masa maganar danyar Madarar da akace ya Aiko da ita da yamma lokacin tana Asibiti.
Saida Zahra ta tabbatar sun fice gaba daya daga dakin sannan ta dubi
Screen din wayar fuskarsa ta gani Yana kallon ta sai taga yayi wani zuru-zuru kamar Wanda yayi ciwo sai hancinsa ya Kara fitowa zuwat dashi hakensa ma ya qaru.
"A hankalin tayi masa sallama tana fadin "Ya M baka da lafiya ne Naga ka rame?".
Bushashshen lebensa ya da tura cikin Bakinsa ya lumshe idanunsa tun lokacin da aka fada Masa Bata da lafiya bai samu peace of mind ba sai yanzu daya ganta. Dan ita ke ciwon Amma shi keda zulumin da ramar Dan tun daga lokacin zuwa yanzu daya ganta Baya Jin yaci wani Abu na kirki a cikinsa.
A hankali ya bude idonsa ya Dora akan tata fuskar dake kallonsa, wani yarrrr taji da suka hada idon.
Cikin tsantsar kasala da jigata ya bude Bakinsa a hankali yace.
"My previous hankalina ya tashi, wallahi gani nakeyi kamar Zan rasaki, ya jikin naki? Kuma tun yaushe ciwon ya kamaki Baki fada min ba? sai Zayyan ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login