Showing 78001 words to 81000 words out of 122700 words

Chapter 27 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

596

gaida Dear ba irin wannan local gaisuwar ba"
Sunne Kai tayi tana Dan murmushi, tsugunawa yayin daf da ita yana kallon 'yan yatsun Hannunta sumul sumul dasu kamar Bata aikin komai da Hannun, dagota yayi gaba dayan ta ya mannata a jikinsa "ji nakeyi kamar kada nayi tafiyar nan ko Kuma na daukeki mu tafi, idan na tuna zanyi nesa dake wlh wani irin rauni ne yake kamani naji kamar idan bana Nan wani Abu ze faru".

Ya fada cikin muryar karaya da gaske a 'yan kwanakin Nan Yana Jin wani Abu daya fi na da a tare dashi.
Cikin 'yar siririyar muryarta tace "ba komai kaje kawai Allah Yana tare damu ba abun da ze faru sai abinda ya hukunta a kaina, Allah ya bada nasara yasa a Dace, kawai dai Dan Allah kayi min wata alfarma kafin ka tafi".
Hijabin ya zare a hankali daga kanta ya Dora a Kan bed side kafin ya zaunar da ita a jikinsa as usual.
"Fadi wace bukata gareki".
Dan shiru tayi kamar bazatayi magana ba.
Oya fell free with me, kiyi magana Mana kinsan eight thirty nake so na wuce".
"Daman so nake na ringa zuwa Dr.sulaimanu Adamu college of Hygiene inda nayi service na ringa yin lectures ko sau biyu ne a sati".
Wani kallo yayi Mata na Amma Baki da lissafi.
"Ni matata da yawon aiki? Gaskiya A'a! Wannan bukatar Bata karbu ba, me kikeci na baka na Zuba indai aiki ne wlh sai kin gaji da yinsa, tashi daga jikina kin wani samu cinya kin dane,kada na makara nayi missing flight mu tsuguna duk dan burin bawa ya rushe".
"Yanzu Allah bazaka Bari na rinka Zuwa ba".
Ta fada a marairaice.
"Kinsan Allah wlh Zan hadaki da zayyan Dan nasan Yana daf da shigowa garin Nan ya juya min dake can kauye gurin Hajiya Inna ko banza kin tuka mata tuwon dawa kin mata shara, kinga ita gaba ta kaita balarabiya na mata aikatau ita kuwa bakar fata Kinga sai mu Dora a media muma 9ja munci gaba ana zuwa daga middle East ana Mana aikatau".
Ya karasa fada Yana Jan Dan tsinin Karan hancinta.
Tana kokarin magana wayarsa dake Kan bedside ta dauki wani kidan larabawa Mai dadi.
"Dauko min wayata Dan tsabar na Zama mijin ......, Gashi Nan ringtone din ma kidan kune na saka". Wayar ta dauko, Zayyan ta gani kwalalo idanu tayi Ashe da gaske yake da yace Shi wannan din zezo yanzu ko waye shi kuma "oho" ta fada a zuciyarta.
Wayar ta Mika masa.
"Ka karaso?" Abinda taji ya fada kenan Bata San me yace Masa ba taji yace "ok, ka shigo ciki akwai securities a kofa zasu zasu rakoka gurin da Zan ganka".
Ya kashe Kiran Yana nufar kofa, ki shirya kafin na dawo yanzu zamu wuce".
Yayi Gaga abinsa ya barta da Baki a sake "ikon Allah shi Kuma ko waye yake bada umarni cikin dare ya wayi gari da abinda ya bukata tasan ko waye daga nesa yake Dan jiya tanaji Yana fadin kada a biyo ta jos a biyo ta kano, ita duk ya Gama Dame Mata lissafi wlh.
******
A hankali yake tafiyar cikin nutsuwa Amma da gani kasan tafiyar ta ingarman namiji ce, tunda ya doso gurin Zayyan ya kafe shi da ido, take ya shiga jinjina lamarin ogan nasa wato ana zaton wuta a maqera said gata a masaqa, waze tab'a tunanin sa a irin nan yayi masifar bada kafa.
Bai Farga ya kureshi da ido ba Saida yazo daf dashi, "sorry sir" ya fada Yana sadda kai, baiyi magana ba ya mika Masa hannu wannan d'abi'ar sa ce baka Masa irin gaisawar Nan sai dai kuyi musabihwa. "Barka da Asuba ya Hanya?".
"Alhamdulillahi."
Ya fada sai da Mahmud ya zauna kafin Zayyan Shima ya koma ya zauna.
Kamar bazece komai ba gurin ya dauki shiru.
Saida yaja fasali sannan yace. "I hope ba Wanda ka fadawa munyi waya ga Kuma inda zaka sameni?"
Kai ya girgaiza "ko daya oga ba Wanda yasan inda na tafi kawai nace musu zanje gida ne na samu Kiran gaggawa".
"Good, na kiraka ne zaka zauna gidan da wife Dina take zanyi tafiya, Wanda na saka gadin Naga alamar gaskiya Bata isheshi ba, ko Kuma ze iya komai saboda kudi, zan turo maka pictures na wasu Mata koda Wasa kada kabar kafarsu ta shigar min gida shi yasa na taso ka da tsohon dare ".
Zayyan jin magwnar yayi wani banbarakwai "wife Kuma? To ta ina Hakan ta faru? mutumin da ake tunanin baya kasa sai Kuma ya ganshi a nan Yana wata irin rayuwa hankalinsa kwance, ga abubuwan tambaya Amma ba Halin yinta.
"To in Sha Allah baza'a samu matsala ba".
"Yanzu zaka shiga cikin Ibrahim ze nuna maka dakin da zaka huta daga Nan zuwa sha daya Binyaminu ze shigo kuje gidan".
Ya fada Yana mikewa.
Da kallo zayyan ya bishi har ya b'acewa ganinsa, ajiyar zuciya ya sauke Yana jinjina Lamarin ogan nasu wato duk yanda kasan Shi idan yayi wata bada Qafar saika rasa gane wace alkiblar ya kalla. "Wife Dina". Yanda yayi maganar kasan ba wasa cikin Yana wannan tunanin Ibrahim ya karaso Bai sani ba.
Da azama ya shiga falon a zaune ya sameta da luggage dinsa a kusa da ita tayi rolling da Veil din rigar sai tayi masa wani irin kyau, a slow ya karasa inda take zaune ya saka hannu ya dagota tsaye ya sumbaci saman goshinta.
"Nayi Miki irin gaisawar ku, Ina key din lokaci Yana ja kada da gaske nayi sakaci kija Mana, muna lallabawa, kin hakura da Zuwa makarantar naji Baki ce komai ba?"
"Bani da say, sai yanda kace haka za'ayi".

"Nace A'a! in dai Ina raye da lafiya ta bazaki nemi komai ki rasa ba Koda kuwa faskare zanyi to zanyi na samu abinda zankula dake".ya fada Yana daukar luggage din ita Kuma ta nufi kan fridge inda ya ajiye key din jiya.
A jere suke tafiya sunyi wani irin dacewa wadda dole idan ka kallesu ka qara suna kokarin fita daga reception su Zayyan suna kokarin shiga, Mahmud ya kalla da jakar matafiya a hannu Yana rike da Hannun Zahra,.
"Kam bala'i"
Yaji Bakinsa ya subuce ya fada Yana matsawa baya Kamar yanda Ibrahim yayi.
"A sauka lfy" Ibrahim din ya fada shi kuwa Zayyan kamar an saka makulli an datse Masa baki.
"Ka bashi key din dakin ka biyoni mota Zan baka sako".
Ya fada Yana duban Ibrahim, mota Zahra ta shige ta barsu suna tattaunawa kafin ya shigo ya tada motar ya nufi get din fita har yabar harabar hotel din, Zayyan na lekensa ta window sai dai yasan idan yayi magqnar Nan da wani kwabarsa ce zatayi ruwa daya fesa labari, oga da rije jikar mace uwa uba yana tukata da kansa Kai wannan abin surprised da yawa yake"Ga bikin zuwa ne babu zani.

Tafiya yake da hanzari Dan ma safiya ce sosai titin ba yawan jama'a cikin Kan kanin lokaci suka shigo unguwar, Horn ya danna da karfi da gudu Mai gadin yazo ya bude yana fadin "barka da zuwa!"
Da gudu ya Koma ya dauko sakon dasu mama suka kawo jiya Yana fadin "barka da Asuba yallabai gashi jiya bayan futarku su Hajiya Babba sukazo suka bada a ajewa Hajiya".
Ya fad'a Yana risinawa Yana mikawa Mahmud ledar.
Saida ya karewa shi da ledar kallo, sannan ya hade gabas da yamma yace ka rika idan kana so, Kuma
Ka hade kayanka in anjima kadan binyaminu ze zo da Wanda ze canjeka aikin Nan adalci daya nayi maka ban koreka ba zaka koma share-sharen makarantar Yara kawai".
Jiki na tsuma Mai gadi ya durgusa Yana fadin "Yallabai me nayi haka da zafi Dan Allah kayi hakuri wlh baza'a qara ba ka rufa min asiri".
"Iya Alfarmar kenan bana korar ma'aikaci sai lefinsa ya Kai uku to Kai daya kayi ba tare da kasan laifi bane shi yasa nayi maka uzuri bazan rabaka da rufin asirinka ba dauki kaje yanzu Zan fito". Jiki ba kwari ya dauki ledar ya juya Yana ta faman tunanin ta ina ya kuskuro yallabai jiya lafiya kalau suka rabu yau Kuma ya tashi da canjin gurin aiki da Allah ma ya dube shi da Rahama daba Kora bace days shiga uku.
Suna shiga Mahmud yayi bed room dinsa ita Kuma ta nufi kitchen ta Fara hada abu marar wahala coffee ta dafa Masa sai sandwich kawai tayi shaf-shaf a tray ta Dora direct bedroom dinsa ta nufa ya fito daga wanka Yana goge jikinsa a ranta tace shi baya mura any time wanka kamar dangin kwadi.
Sallamar ta ya amsa Yana aje towel din dake hannunsa.
"Ke! Me kikayi daga zuwan mu ba dai abinci bane ko? Ni bana cin komai a irin wannan lokacin".
Langabe Kai tayi tana dubansa kasa-kasa har Zuwa lokacin wani nauyinsa takeji. Yana ankare da ita.
"Coffee ne fa da sandwich nayi maka Dan Allah kada ka tafi da yunwa,alhalin gani a tare da Kai ai da naji kunya daga zuwa ka nemi abinci a kanon".
"Inye ashe dai ana son mamudan?".
Ya fada yana nufar inda ya aje kayan da ze saka kananun Kaya ne na kamfanin Armani ya saka bako kunya ya cire rigar wankan ya tsaya daga shi sai boxer short, da sauri ta runtse idonta Dan Bata zata zeyi irin wannan abunba Yana kallonta ya basar yaci gaba da shiryawarsa, Zama yayi Kan sofa Yana umartarta ta kawo masa coffee din nan duka ta dauko ta aje gefensa ya dauka Yana sipping Yana kallonta tana Wasa da gefen veil dinta da ya sauko, sandwich din daya yaci ya yaji ya isheshi Shima Dan kada ya watsa mata kasa a ido ne, amma Sam baya iya cin komai a irin wannan lokacin.
"Zauna muyi magana" ya fada Yana dubanta,.gefen sofar tayi niyyar Zama ya tikota "Kinga gurin zamanki Nan ya dorata inda ya Saba..
"Zan tafi Baki San cikakken asalina ba, Zan fada Miki saboda sha'anin Rai da rayuwa kona dawo ko ba na dawo ba, Ni haifaffan garin sokoto ne iyayena duka biyun sunan Nan ni dangatan iyayena ne da kakata Hajiya Inna, suna Sona yanda Baki zato yanayin rayuwa ne ya kawoni nan, duk family na ba Wanda na fadawa labarinki sai kakata ta sanki a hoto tasan wasu labaranki, kota Allah ta kasance wannan dana Kira ya zauna yayi min gadinki sunansa zayyan na fada Masa ke matata ce ze sadaki da Family na, Dan Allah kiyi min Alkawarin duk rintsi bazaki juya min Bata ba, ki rike min aurena da Kima da daraja, idan Allah yasa na dawo Zan fada Miki koni waye da duk abinda ya shafeni na rayuwata Daman taki na sani ba sai kin fada min ba,
duk abinda kike bukata ki duba waccen lokar akwai kudi a ciki bangaren abinci Kuma nabar komai a Hannun Habib, ga Kuma kudin da Sameer ya Baki ban Baki ba". Ya aje mata su a akan cinyar ta.
Jin tayi shiru yasa ya dago fuakarta da hannunsa,kukan Zuci take ba wani sound sai dai hawaye"subhanallahi kuka dai? Kona fasa tafiyar nan kawai tunda Naga hankalinki yaki kwanciya da ita"
"Ba komai kaje kawai naji Kanata nanata maganar in baka dawo ba na sani ko idan ka tafi bazaka dawon ba".
Lakuce Mata Baki yayi "ai kece bazan dawo din ba, wannan ya shafa cikinta sai kin ajiye Mana babies a ciki idan naki dawowa aini nayiwa kaina, ki kwantar da hankalin ki nema zani ki min addu'ar samun nasara".

✨✨✨
✨✨✨

AUREN HUCE HAUSHI


Strory
&
Written
By
Maman Fateemah


Page 29


📖🖋️
_____ Sun jima a haka Yana lallashinta kafin ya dagota su tashi tsaye tare " me za'a bani nayi guzuri dashi?"
Ya tambaye ta, shiru tayi kafin ta Dan watsa hannu tana Dan kallonsa ta gefen ido.
"Ai kaga bamu kwana a gidan ba bare nayi maka wani Abu Saida idan biscuits din Nan Zan dauko maka sai ka tafi dasu na bada a sawo min wani".
Dariya abin ya bashi ita bilhaqqi da gaske take fada Wai biscuits kamar wani yaro.
"A'a niba shi nake so ba tsarabar da zan rike Ina tunawa da ita har na dawo".
"Me Kenan?" Ta tambaye shi cikin nuna rashin sani.
Jikinta ya matso sosai ya riko ta Yana kallonta da wani yanayi mai wuyar fassarawa, Bakinsa ya Kai Kan nata Dan bakin yasa Hannun ya talkafo kanta batayi zato ba tsammani taji harshensa na yawo cikin bakinta ya lalubo nata harshen cikin gentle yake tafiyar da ita ba kamar ranar nan ba, sun dauko Kusan minti biyar Yana Abu daya ji tayi kafafunta na neman gagarar daukar ta, jin jikinta na rawa yasa ya Kara mannata da jikinsa wani Nishi tayi ba Halin magana, kokarin yanye harshenta take daga Bakinsa Kai ya girgaiza Mata sai da yayi mai isarsa ya saurara Mata Kan gadonsa ta zube da gaske ya kashe Mata jiki ji take idan ta taka kafarta faduwa zatayi.
Dan rankwafawa yayi saitin fuskar ta "Haba 'yan Mata be strong Mana me akayi da maza inji karya, taso muje ki rakani idan na biye Miki labarin salo ze canza".
Ya kamo hannunta ya mikar da ita, jakar laptop dinsa kawai taga ya dauka, gyalenta wanda yake yashe a kasa ya tsuguna ya dauko Mata Yana rufa Mata a kanta.
"Zaki bani Aron motar ki naje Kano da ita? amma fa saina dawo na dawo Miki da ita a airport Zan bada ajiyarta yanda idan muka dawo saina karba kawai".
Kai ta gyada Masa alamar Eh.
*A'a magana zakiyi idan kin amince to idan Baki amince ba na nemi hanyar Tasha kawai".
"Ka dauka kaje da itan koka dawo ma na bar maka za'a kawo min wata ba kaji Abba ya fada ba".
"Ke! Kinsan kudin ta kuwa zakice kin barmin Dan ki hau Abba ya saya Miki, Aron ma Ina laifi".
Yaja hannun ta suka nufi kofar a falo ya tsaya Yana wasu 'yan dube duben da Batasan Kona menene ba sannan suka nufi harabar gidan, kasa hakuri tayi ta jefa Masa tambayar.
"Wai haka zaka tafi ba kayan sakawa da takalma da sauran abun bukatu ne?" Dan shafa gefen fuskar sa yayi ya Dan furzar da iska daga Bakinsa. "Bana tafiya da Kaya ai wahala ce nasan duk inda zani akwai na sayarwa na saya kawai, aikin gane?"kallonsa kawai batace Masa komai ba.
Saida yaje gurin Mai gadi ya bashi wata envelope sukayi maganganu sannan ya dawo gurin da take tsaye.
"Zan tafi sai Allah ya dawo Dani, ki kula da kanki bana son yawo Amma idan gidan Ammah ne ko Aunty Hasana idan Bata koma Jos ba kina iya Zuwa".
"To na gode, Allah ya tsare hanya ya bada sa'ar abinda akaje nema".
"Allahumma Amin. Allah ya tsare min ke daga sharrin mutum da Aljani da dukkan abinda yake cutarwa, ya Ubangiji na bar maka amanar iyalina ka Zama gatan mu".
Ya fada yana nufar motar, a hankali ta biyo shi ya bude ze shiga ta riko hannunsa ta Manna masa kiss a tsakiyar hannun. "Safe journey" ta fada da wata murya Mai rauni da gudu ta juya idonta fal hawaye. Tsaye yayi Yana kallon ta har ta shige ciki, ajiyar zuciya ya sauke kafin ya shiga ya tada motar jikin window ta tsaya har Saida ya fice daga gidan.

________________________

Tunda Mahmud ya bar cikin gari ya saki motar, rabon da yayi tuqi irin wannan har ya manta, kyakykyawar awa daya da minti arba'in da Tara ta kawo shi Kano, daga Hotoro NNPC sai ya shiga ta ring road ya fita 'yan kaba haka ya dunga yayyankewa har Zuwa round about na sani Baban kwari Sannan ya nufi Malam Aminu Kano international airport,Yana daf da shiga gate din ya saka face mask da glass sannan ya shiga, wayar Sameer ya Kira tana daf da katsewa ya daga.
"Kana Ina? Na shigo yanzu ina fatan komai ya dai-daita?". Dan Jim ya yi yana sauraren sa. "Ok kazo ina parking lot inda ake bada ajiyar motoci".
Ya sauke wayar Yana kalon masu Kai da kawowa.
Yana Nan tsaye har sameer din ya karaso ya gaishe da Mahmud cikin girmamawa, jakar laptop din Sameer ya karba da key din motar ya nufi inda suke da alhakin karbar ajiyar, shi Kuma Mahmud ya nufi reception din.
Sameer Bai jima ba ya dawo da takarda shedar bada ajiya, sun Dan tattauna kafin lokacin tashinsu yayi, zasu shiga screening ne Mahmud ya Kira wayar zahra, tana kwance a gado rungume da pillow bayan tayi kukanta Mai isarta ta lallashi kanta tunda Babu Mai lallashin gani takeyi shima kamar ya tafi kenan. Ringing din waya taji da sauri ta tashi Dan ita Sam tama manta da wata waya tunda ya Bata Bata karabi takanta ba, da sauri ta dauko tana duba waye ya Kira MM DANGE ta gani wani sanyi taji ya saukar mata,
Picking tayi tare da sallama, sai kuma tayi shiru.
"Zamu tafi ne nace bari na kira na fada Miki, ko zamu sake waya ze iya kaiwa jibi kada hankalinki ya tashi idan komai ya dai-daita Zan kiraki in Sha Allah".
"Tom Allah ya saukeku lfy".
"Allahumma Amin my precious, please take care bye".
Ya katse Kiran yasan idan yaci gaba kuka zata saka Masa ya rasa wane irin idanu gareta masu saurin kuka.
Sha biyu da rabi jirginsu na kamfanin air Max ya daga.


Wayar tabi da kallo kafin ta aje kusa da ita, sai Kuma ta tashi kamar wadda aka zabura. Wayar ta dauko dubawa tayi wata baguwar number ta gani batayi kasa a gwiwa ba tabi Kiran Dan missed call ne tunna jiya. Cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga Bata jima Tana ringing ba aka daga muryar matashiyar macece daga ji tana ji da ajinta sallama Zahra tayi Mata suka gaisa sannan zahrar tace Mata taga missed call dinta ne a wayar ta.
"Missed call Dina gaskiya bani na Kira ba Amma Dan Allah wacece ke?.
Yar dariya Zahra tayi kafin tace "sunana Fatima Zahra Muhd sani Ni mazauniyar Azare ce ta jihar Bauchi".
Kit ta kashe wayar ta yunkura ta tashi, ta nufi kofa tana daf da fita taji wayar ta Kara daukar Kara ta dawo number dazu ce yi tayi kamar zata share sai Kuma ta dauka taji me zata fada Mata.
Sallama tayi daga can ta amsa sannan ta Dora da fadin "Dan Allah kiyi hakuri da farko ban

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login