Showing 108001 words to 111000 words out of 122700 words
haka nake son ji, ya ciwon ya daina ko yanayi kadan kadan".
"Ya M na warke yanzu ba wani Abu da yake damuna dama mu koma gida kawai tunda ya wuce, kawai naje Naga baby muje mu gaishe da mommy da Umman sajida zuwa jibi mu koma, Dan Allah kace to kaji Kuma fa kaga gidan da oga Sameer ya kawo mu gaskiya ka fada Masa ya mayar damu gidansa ko gidan mommy wallahi yayi girma Ni tsoron inda aka kaini nakeyi gurin yayi nisa da main parlour Kuma wani abin mamaki kasan funitures din dake dakin irin na dakinka ne na Azare komai da komai".
Dan Jim yayi kafin yace irin nawa Kuma wace unguwa ya kaiku?".
Dan Jim itama tayi. "Ina ga ko Dawako Road Nasarawa G.R.A.
"Ok nasan gidan na wani friend dinsa ne, wane bedroom din aka Baki?".
" Bangaren dama daga can ciki sosai".
Shiru yayi wato Sameer be bude Mata master bedroom din ba kenan.
"Precious ki hakura a duba min ke kinsan kuwa tension din dana shiga akan ciwon nan naki? kiyi hakuri ayi bincike akai kawai sai nafi samun kwanciyar hankali, gida Kuma nasan shi Baki da matsala dashi Dan cike yake da tsaro ba wata kafa da za'a shigo cikinsa".
"Baka Gane ba nifa ni kadai ce bazan iya kwana a gurin ba sai dai Aunty Rukayya tazo mu kwana".
Ta fada kamar zatayi masa kukan shagwaba.
"A'a ban Amince ki kwana da kowa ba, ba abinda ze kamaki matsoraciya kawai kice na shirya nida nake fatan Allah ya hore min nayi Miki Wanda yafi wannan girma yanda Zaki sake ki walwala keda yaran mu, to kina tsoron wannan ma inaga Wanda nake fatan ajiye sarauniyar Mata a ciki Zahra fa kike ko cikin taurari keta dabance, haka kawai ki janyo min wata ta hanani rawar gaban hantsi da dare so nake ki ragemin zafi idan da wata a dakin ai kin sabautani ko baza'a taimawa dan malam ba?".
Ya fada cikin wata irin kasala wadda ta saka Zahra Jin wani irin Abu a jikinta. "Ya Ilahiy Ajib"
Ta fada cikin kasakalliyar murya.
"Yan Mata yaya dai Kona gudo ne kina bukatata a kusa"
Ya fada Yana huro Mata iskar Bakinsa ta cikin phone din, da sauri ta cire wayar daga kunnanta, Dan da gaske sakon yaje inda aka aike shi kashe Kiran tayi bako sallama.
AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH.
Page 39.
________Wurin karfe takwas Sameer ya shigo gidan, wayar Rukayya ya Kira yace su fito doctor tana jiransu, lokacin suna bedroom din da zahrar take suna cakusawa da Zahra akan wata Rigar shadda 'yar Mali da Rukayyar ta daukowa Zahra cikin kayan da Sameer ya bada ta sawo haka Nan Rukayyar taga zata Dace da zahrar shi yasa ta nace akan ta sakata ita kuma tana ganin tayi Mata girma da yawa, Jin Kiran Sameer yasa ta hakura ta saka sai gashi tayi Mata das kamar an gwadata aka Dinka.
Shar ta fito kamar ka dauke ka buye saboda kyau sai yarintarta ta Kara fitowa, dauri mai kyau Rukayya tayi Mata tunda ta kware har makeup din amare takeyi, light makeup tayi a fuskar ta sai ta fito kamar amarya ranar a yini.
"Masha Allah" kadai Rukayya ke fada ba karya kyau daban yake ko ita mace zahra ta tafi da imaninta to yayi namiji Kuma? Bata yarda da kyau idan yayi yawa hadari bane sai yanzu da Zahra ke gaban ta Dan babu namiji da ze ganta Bai Kara kallonta ba.
Kasa hakuri Rukayyar tayi Saida ta magantu.
"Allah yasa kiyi ta haifowa big bro Yara masu Kama dake gaskiya Ya Mahmud ya Dace ai shi wallahi gaba ta kaishi gara da aka samu wannan incidence din da Bai faru ba yaushe ze gano Mana ke".
Ita dai zahra murmushi kawai takeyi, amma Kasan zuciyar ta tambayoyi ne fal, Ta Ina Mahmud ya zama big bro din Rukayya da alama akwai wata dangantaka Mai karfi a tsakanin Sameer dashi bawai aikin NGOs din Nan bane gaskiya.
A haka suka fito main parlour suka tarar da Iya Rahane da zilai suna kallon Arewa 24 suna program din mata a yau.
"Masha Allah, Allah ya kade mugunji da mugun gani".
Iya Rahane ta fada tana kallon Zahra.
"Allahumma Amin. Allah ya tsare uwar dakina ya Baki lafiya yasa a dace".
Zalai ma ta fada, Rukayya tace "Allahumma Amin, sai mun dawo".
Suka nufi hanyar fita, a cikin mota suka iske Sameer, gaba Rukayyar ta shiga ita kuma zahra ta shiga back seat.
Basuyi wata tafiya Mai nisa ba suka shiga cikin Asibitin, bayan sun fito daga motar number Dr. Haseenar Sameer ya Kira, saiga wata sub-staff da wayar a hannunta tana fadin "sunnunku da zuwa doctor tace na tafi daku office dinta tana zuwa suna wani aiki ne"
"Ok mun gode".
Rukayya ta fada.
Har cikin office din ta kaisu ta fita Nan Sameer yabar su yace zeje yaga wani friend dinsa Dr. Sulaiman.
Bai jima da fita ba aka turo kofar su duka suka juya suna kallon Mai shigowa macece wankan tarwada Mai matsakaicin tsawo fuskarta doguwa ce da maidadaicin idanu da hanci tana sanye da doguwar Rigar material coffee Mai haske tayi rolling da milk din veil fuskarta fal fara'a ta shigo tana fadin " wa nake gani kamar Rukayya a office dina rabon daki tako Nan harna manta Sai dai a waya".
Dariya Rukayyar tayi tana fadin "Ina laifin Kiran wayar ma Shima zumunci ne yafi ace ba'ayin ko daya".
Direct gurin da suke zaune ta nufa " Kinga kin dauke min hankali Ina ta zuba ban yiwa bakuwa ta sannu da zuwa ba, sorry na barku a zaune ta fada tana kallon zahra"
"Lah haba doctor ba komai yanayin aikinku ne hakan".
Zama tayi kusa da Rukayya tana maida hankalinta akan Zahra.
Patient din dangen ce?"
Ta jefawa Rukayya tambayar, da alamun mamaki a fuskar ta.
Kai Rukayyar ta gyada mata.
"Anyway Bismillah ta fada tana tashi daga gurin ta nufi table dinta.
Zahrar ta Mike tabi bayanta.
Tambayoyi sosai ta rinqa yiwa zahrar wasu har kunya take kamata ta kasa Bata amsa, tambayar data fi Bata mamaki shine inda take tambayar ta meye tsakanin ta da Mahmud Dange?"
Kafin zahrar tayi magana Rukayya ta rigata "sister din abokinsa ce daga Bauchi, kuma matar aure ce Dan naji Baki tambqyeta ba, ita Kuma Bata fada Miki ba".
Wata ajiyar zuciya ce ta kubcewa Dr Haseenar har Saida Zahra ta kalleta.
"Ai ban sani ba Ruky Naga DANGEN yayi matukar damuwa ne ko yanzu kafin na shigo saida ya kirani yana fada min Kuna Nan Kuna jirana na dubata sosai".
Dan smile zahra tayi kawai ita Kuma Rukayya tace "kinsan halinsa baya Wasa da rashin lafiya komai kankantar ta, kinsan suna China Aunty Fateeha ta haihu sending Ya Sameer yayo Nigeria shi ya wuce Dubai".
Dan murmushin itama Dr din tayi "zeyi abinda yafi haka in dai Dange ne yanda ya damu Zaki dauka matarsa ce wallahi duk yafa rikice kamar ba dangen da Mata ke fada a kansa ba ko kallo basu isheshi ba Sanda muna school a UK da yawa mutane sunyi mamakin yanda muka Dade dashi ba wani matsalar data faru fatana ya dawo su hadu da Daddy ayi a wuce gurin kawai, kinsan halinsa tunda aka samu matsala Nima fa ta shafeni tunda lokacin da abun ya faru munje gida sokoto shiya Hana ayi abinda za'ayi ta fice yabar kasar Kinga Banda case din Nan ta sister din friend nan tashi Bai Kara kirana ba wlh na tura Masa sako ta email dinsa Amma ba reply".
Ita dai zahra ba baka sai kunne wata magana sukeyi wadda ta jefata a kogin tunani akan Mahmud abinda kunnen ta keji daban abinda yake nuna mata daban.
"Hum lamarin big bro sai a hankali kin sanshi da zuciya kafin dai yayi fushin ana dadewa Amma idan yayi jam'i yakeyi gurin yanke hukunci sai hakuri komai ze Zama normal".
Rukayyar ta fada.
Forms ta cikewa Zahra ta test-test Wanda za'ayi Mata ta Mike ta fito daga mazauninta tana fadin kuzo muje ayi wannan testses din Sai Kuma muje ayi scanning mu gani akwai abinda nake tunanin yana kawo matsalar Amma bazamu tambbatar ba sai mun duba.
"To Allah yasa a Dace" Rukayya ta fada.
Sai da suka Fara zuwa lab sannan suka nufi radiology department inda za'ayi hoton cikin.
Dr karima ce tayi mata scanning din tambayoyi ta Riga yiwa Zahrar harta gama.
Basu jira karbar result din ba, da safe doctor Haseena zata shiga dasu can Asibitin malam Aminu inda za'a mata saura gwaje-gwajen Nan sun Dan rage ne saboda cunkoson can din.
Har gurin mota doctor ta rakasu suna 'yar tsama da Sameer, sannan sukayi sallama Sameer na Mata godiya saboda taki yarda ya biya ko sisi tace patient din DANGE nata ne, itama Zahrar godiya tayi Mata Rukayyar ma haka.
Har Sameer yayi ribas doctor Haseena ta daga Masa hannu alamun yazo gyara parking yayi ya fito ya nufo inda take a gefen baranda.
"Yana zuwa Bata jira komai ba ta Fara tambayarsa cikin nuna damuwa Dan idanunta har Dan ruwa ya taru a ciki da gani tana cikin damuwa da tashin hankali.
" Wannan yarinyar wacece a gurin DANGE?"
Iska ya Dan huro daga Bakinsa ya hade hannuwansa a kirji Yana kallonta kawai.
"Me yasa Kika yi min wannan tambayar?"
"Just pls answer me who's she?"
"Abinda ya fada Miki da farko yanzu ma dai shi zan maimaita Miki, kanwar friend dinsa ce daga Bauchi sukazo Kuma matar aure ce abinda na sani kenan".
"To Amma me yasa ya shiga damuwa akan lamarin ta ya hanani sakat Ni Kuma nasan wannan ba d'abi'ar DANGE bace".
"To ki Kira shi kiji gaskiyar magana daga Bakinsa Mana".
Ya fada Yana kokarin barin gurin.
"Kada kaji haushina na kasa samun nutsuwa ne"
Bai tsaya ba Dan da gaske nema take ta karya Masa gwiwa har yayi abinda baze musu Dadi ba, gara taji daga baya a bakin wani ba shi ba, Daman yasan za'a Rina dole ta kawo wani Abu a ranta yanda ya nuna damuwa akan lamarin Zahrar.
Jiki ba kwari ya dawo motar ya tada yabar gurin, har lokacin tana tsaye Bata bar gurin ba. Shi kansa yaji Babu dadi a ransa yanda Haseena ta mace akan Mahmud tun suna UK yasan idan taji yayi aure ba Kara min tashin hankali zata shiga ba.
Sai da sukayi nisa da Asibitin sannan Rukayya tayi magana "Dan Allah Yaya kaimu murtala Muhammad way zanyi sayayya a Nameer Sale".
Tsaki yayi kadan da gani ranshi ba dadi, "nifa baba son yawo kinga ai saimun koma baya, me yasa Baki fada min ba tun kafin mu fito nasan da zuwan".
"Kayi hakuri mantawa nayi Amma muje gobe in Sha Allah naje kawai".
Bai Kara kulata ba haka zahra Bata tofa tata ba.
Yana zuwa round yayi ya dawo ya nufi murtala Muhammad way din, tare suka shiga da Sameer din yace zahra ta duba abinda take so, har Rukayya ta Gama daukar abinda tazo nema zahra Bata dauki komai ba, ganin haka yasa Rukayyar ta daukar mata kayan shafa dasu turarikan gashi Dana wanka shi Kuma Sameer ya daukar Mata dangin su wafer da ice cream, a hanya hira sosai Rukayya keyi musu Amma ita Zahra hankalinta Yana Kan maganganun doctor ita fa abin yafi karfin tunanin ta ke nan da lauje cikin nadi, shin waye uban gidan wani tsakanin Mahmud da Sameer idan ba kunnenta ne baiyi daidai ba taji Rukayya na cewa Mahmud ya Turio Sameer gida daga China ya wuce Dubai zance yayi dai dai Dana Fateeha matar oga Sameer lokaci tafiyar su.
Har suka shigo unguwar hankalin ta baya tare da ita tayi zurfi cikin tunanin makomarta kodai yanda ya taba fada Mata Yana yaudarar matan ne ya gudu dasu tunda yanzu yasa an dauko su ba Wanda yasan inda ya kawo su daga Rukayyar har Sameer din ba Wanda yasan takamaimai Ina ne asalinsu an kawo su ita da baiwar Allah an killace su a wannan uban gidan kamar resident na matar shugaban kasa.
Sai da Rukayya ta Dan tabata lokacin da suka tsaya a kofar parlourn Dan da gaske tayi mugun zurfi a tunanin Dan zabura tana Fadi. "wallahi har naji tsoro".
"Ai ke dince Ina ta magana Amma kinyi Zurfi a cikin tunanin, ki rage yawan tunani saboda lafiyarki kinsa Yana shafar lafiyyar Dan Adam".
"In Sha Allah Zan Dena na gode".
Ta yungura ta fito Bata jira ba ta nufi kofar shiga tana fadin oga Sameer sai da safe kaina yake Dan Sara min a shafa min Kan Abeed"
Dariya Sameer.
"Zeji in Sha Allah Banda mamansa ko?"
"Kaina bisa wuyana na Isa ayi min gaisuwa, zanzo muyi jegon tare".
Wani kallo Rukayya tayi Mata tayi wani killer smile ta matso daidai kunnen ta "saurin me kikeyi in dai jego ne kamar yaune kinsan Yayana ba rago bane daina gaigaye zakiçi tumo".
Tayi gaba abinta kamar Bata Fadi komai ba. Ido Zahra ta zaro tabi bayanta da kallo, ta fuske kamar ba ita ta Fadi maganar ba.
Ganin haka yasa Sameer ma ya basar ya dauko wasu ledojin yabi bayan Rukayya data dauko wasu.
A Nan parlour sukayi sallama da Sameer ya tafi, su zilan Basu tashi daga kallon ba suka Yi musu sannu da zuwa tare Da tambayar ya jikin nata, bata jima ba ta dauki kedar cosmetic din da robar ice cream Daya da biscuits da chocolates ta nufi hanyar masaukinta tunda yace Mata ba komai a gidan da tsaro sosai ta Sami kwari gwiwa da kwanciyar hankali, tana barin gurin ta dauko wayarta ta kasheta gaba daya tana fadin.
Wallahi kwana kusa ba zasu gaisa ba tunda shi wani irin mutum ne marar Alqibla. Kuma tafiyar ta zatayi ta koma inda ta fito haka kawai Kullum ita kenan cikin matsala gara ta koyi jajurcewa itama kowa ya samu dama saiya ringa dokata kamar wata ball impossible wallahi".
Ta fada tana zura katin bude kofar ta shige ciki, a Kan sofa ta zube kayan ta shiga cire kayan jikinta Daman duk sun dameta, wanka ta shiga Dan wallahi barci takeji, barcinta zatayi tasan mutum Bata wuce kaddararsa.
******
A gajiye ya shigo masaukinsa yau throughout bai samu hutu ba, hankalinsa gaba Daya yayi gida so yake ya ganta ra'ayal ain bawai ta wayar ba yaji dumin jikinta ya tarairaiyi kayarsa suyi barci tare su tashi tare ya gaji da watangaririyar Nan gara ayi wadda za'ayi kawai game din ya Zama over.
Saida yayi wanka yayi order coffee sannan ya janyo wayar ya shiga nemanta da gaske yayi kewarta ba kadan ba, shifa yana ganin yarinyar Nan itace weakness dinsa duk inda take tana manne a kirjinsa ko barci yake itace a cikin barcin idan ba ganinta yayi ba ko yaji muryar da da akwai damuw, yaga alama any nan gaba ze iya kulla wani abun arziki kuwa? tun yanzu da gishiri bai Sha Kan kazar ba yana jinsa haka Yaya idan labarin ya sauya salo?
Abin mamaki wayar switch off.
Zuru yayi Yana kallon wayar "me kenan?"
Yasan dai ba matsalar charge bane, Sameer ya Kira, duk da basu Dade da Gama waya ba.
Sameer yayi mamakin ganin wani Kiran nasa.
Kafin Sameer ya Kai ga magana Mahmud ya Riga shi.
"Meya faru ne a Asibitin naji wayarta a rufe ko jikin ne ta tashi da akayi Mata gwaje-gwajen?"
"A'a gaskiya normal muka dawo har muka biya nan Murtala Muhammad way sukayi sayayya Kasan Rukayya bataso a zauna lafiya,idan tajita da kudi ba zaman lafiya. Dan Allah ka daina turo mata kudi har madam tabar garin nan, kasan Ruky da yawo Kullum aka fita saita qirqiro zuwa wani gurin, wani Abun ne ya faru yanzun ?"
"A'a ba komai, kada ka manta da maganar kayan da za'a sauke gobe a Nan kanon a turasu can Azaren munyi magana da Habib dazu".
"Ok in Sha Allah".
Sukayi sallama, ji yayi baze iya fada masa komai ba. Wayar ya aje kusa dashi wani tunani yayi sai yaji dariya ta kubce masa "zakiyi bayani da yaren garinku yarinya duk yanda akayi taji wata maganar yanzu a Asibitin yasan Haseena farin sani yanda yaji ta damu da sanin relationship din dake tsakanin sa da zahra yasan zatayi duk yanda zatayi ta shigo da wata maganar wadda zatayi touching dinta tunda shekarun da wayonsu ba Daya bane.
Itama Zahra kasa cin komai tayi fridge ta bude ta saka ice cream din da chocolates tayi kwanciyar ta bayan tayi Addu'a, amma barcin Kuma yace baisan zancen ba, tashi tayi zaune a tsakiyar gadon tana tariyo rayuwarta ta baya "ko yaushe Zan Zama stable a rayuwata? sai hawaye suka zubo Mata "Ubangji ka hanani ganin bakin cikin gidan Aure, lamarin Yana neman yafi karfina ka jibinci lamurana Dan isar fiyayyan halitta Annabin Rahama Muhammad s a w.w.
Bansan ko waye ba wannan bawan naka, kafini saninsa ka amintar Dani a cikin lamarinsa daka barni na tozarta, ka kareni daga dariyar makiyana Ubangiji kasan ko suwaye suke mini yankan Bata a cikin lamarina, kayi min kariya ka bani juriyar abinda ka jarrabeni dashi kasa ya zamar min kaffara.
Tasa tafin hannunta a fuskarta taAUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH.
Page 40.
______ karfe takwas saura Zahra ta fito cikin shigarsu ta asali doguwar Riga baka Mai aikin zare maroon sai kananan stones har kasa,tayi rolling da maroon din veil, cikin takunta na rausaya take gannaro steps din, tana baza sansanyan kamshi, ba kowa a parlourn sai wani sanyi da kamshin freshners ke tashi, Dan Jim tayi tana tunanin ta koma kota zauna sai Kuma ta jiyo alamun motsin kwanuka a kitchen gurin da taga suna shiga ta nufa tunda ba sanin Kan gidan tayi ba, tunda ta shigo iyakarta Nan sai Kuma bedroom din da take, tana dosar gurin wani kamshin girki yayi Mata sallama, babban kitchen ne na zamani Mai kunshe da na'urori birjik kamar a wani babban Hotel ko irin modern restaurant din nan iya Rahane ta gani tana yanka wani Abu yayin da zilai ke tsaye tana duba wani abu a tukunya.
Sallama tayi musu tana fadin "Ina kwanan ku".
A tare suka juyo suna amsawa tare da fadin "ya Kika kwana da jikin?".
Dan juya Kai tayi tana fadin. "Nifa Babu abinda ke damuna kawai dai Dan a dunga yawo ne da Bata lokaci, wallahi har kunya nake ji" .
"A kul Kika Kara fadar haka tunda mijinki yace Kizo a duba aga menene