Showing 63001 words to 66000 words out of 122700 words
naka Nan kasan ko waye shi lamarinsa Ubangiji ka sani ba boyayye bane a gurina Idan Yana da wani kaidi kada ka Bari yayi tasiri a kaina Dan isar Annabi MUHAMMAD a gurinka. Ubangiji kajikaina ka duba raunina ka tausaya min kada ka Bari makiya suga wallena ka bani rinjaye a kan dukkan al'amurana".
Duka hannuwanta tasa ta rufe fuskarta kamar me shafa addu'a Amma kuka ta saki Mai tsuma zuciya tana ayyana "Wai fa ita Amarya ce wadda ya kamata ace a irin wannan time din ana can ana riritata kamar a hadiyeta dan so da kauna da tarairaya da kulawa. Amman nata da haka yazo Mata, Astagafirullah Ubangiji ka yafe min zunubina daya janyo min irin wannan gararin rayuwar".
Ta dauki dogon lokaci tana shashhsheka a haka barci yaci karfinta ta sulale a gurin yayi awon Gaga da ita.
Bata farka ba sai kusan biyar da rabi cikin sauri ta tashi tana fadin "subahanallahi!"
Da sauri ta nufi toilet tana addu'ar tashi daga barci, a gurguje tayi uzurinta tayi alwala ta fito sallah tayi ta zauna yin Azkar da karatun qur'ani har gurin takwas na safe.
Mahmud Bai dawo gida ba daga sallar asuba gurin Sameer ya wuce, so yake yi suyi duk abinda ya kamata a Nan tunda kwaso jiki ya taho, shi yasa jiya yaqi yin komai yayi kwanciyarsa kawai.
Ba karamin mamaki Sameer yayi ba ganinsa da yayi a irin wannan lokacin to ai ko lokacin da taye single baya Masa sakko haka. Amma sai gashi shida yake expecting dinsa gurin one-two haka shine ya ganshi haka kamar an koroshi.
Cikin zolaya yace "My man ya naga haka ka duba time kuwa? Ka fito kabar 'yar mutane ko dai da matsala ne na fadawa Babanka manya su shiga ciki, sun baka yarinya girma -girma kana neman ka bada musu yaji a ido duk Wanda ya ganka a irin wannan lokacin daya Kamata ace kana can kana Shan kafi tea, ai sai mutane su dauka fanko aka kawo maka, gaskiya ka yiwa Allah ka koma ni zan shigo mu karasa aikin a gidanka daman meke kawo mu Nan? ba bukatar privacy ba? to yanzu muna dashi kaga no need sai munzo Nan Kuma kasan yanzu ba da bane ".
Ya fada ba alamar zolayar yanzu, ikon Allah Mahmud ya tsaya yana kallo kafin yace "ka Gama Alhaji muhammadu tunda Naga alamar roll din tsohona kake playing, to Wai Ina ruwanka da harkar Nan Ina cewa Mata dai tawa ce yanda nayi ra'ayi haka zan tafiyar da abina, ai dalilin daya kawoni kenan kazo mu ida duk Wani aikin da zamuyi kaje kayi sallama da malam ka kama gabanka".
Ya zauna Yana dauko laptop din Sameer Yana operatin dinta.
Kusa dashi Sameer din ya zauna Yana fadin "Allah ya huci zuciyarka angon Zahra da Safnah....." wani kallo Mahmud ya watsa Masa wanda yasa Sameer yayi shiru ba Shiri, shi kansa baisan sanda bakinsa ya furta sunan safna ba ko alama.✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨
✨✨
Story
&
Written by
Maman Fatimah.
💎 Page twenty three 💎 (2 3)
________Zahra ba ita ta farka b sai gurin bakwai da rabi, sai lokacin ta tuna ta cewa Musaddiq ya fadawa Ammah ta bar kawo abinci zata dafa tunda ba komai take ba, toilet ta fad'a ta Dan sakarwa kanta ruwa Bata jima ba ta fito Riga da Wanda na Pakistan ta saka tayi rolling da gyalen ta saka plat shoes na daki ta nufi falo Amma zuciyar ta tana ta dar- dar kada suyi arangama da Dodon nata, falon ta shigo shiru sai sanyin A/C da daddad'an kamshin da yake ga curtains din duk a sake ga fitilu masu qarancin haske a kunne saiya bada wani irin yanayi Mai saka nutsuwa.
Dan waige-waige ta Fara Kamar tana neman wani Abu gurin sai Kuma ta nufi gurin tv ta tsuguna tana hada socket din adapter din tv ta kunna ta kamo tashar Almajid, kokacin sun saka Qira'ar Muhammad Saddiqul minshawi a cikin suratul ISRA'I sai da ta dai daita volume din sannan ta nufi kitchen din a nutse da takunta Wanda da yawa suke ganin yangace da jiji da Kai alhalin ba haka bane naturally haka Allah yayi ta.
Kitchen din ta shiga Kusan shigowarta ta uku Kennan, lokar da taga kayayyakin aikin ta bude ta dauko roba mai Dan Fadi ta nufi store ta debo Irish ta fito wanke shi tayi ta fere ta zuba a tukunya ta kunna gas, sai kuma ta dauko kaza guda ta yanka ta wanke ta zuba seasoning da spices ta rufe, ta jona egg boiler ta zuba kwai hudu a ciki.
A gefe kuma ta dauko attarugu da Albasa ta yanka kananu ta aje a gefe Irish din ta Fara dubawa taga yayi ta sauke ta zuba a container Mai zurfi tasa fork ta murje ta dora frying pan ta zuba Mai kadan ta saya attarugu da albasar ta zuba a Kan irish din ta zuba magi da curry ta fasa ta yanka dafaffen kwan a ciki sannan ta fasa danye ta zuga ta juya ta aje ta duba kazar itama tayi Nan da Nan ta hada pepper chicken sannan ta jona tanda electric ta Fara zuba hadin Irish din Nan tana soyawa Kamar masa, tana gamawa tayi pepper chicken. Dora ruwa tayi a karamar tunya kafin ya tafasa ta dauko madara ta bude ta diba a wani bowl ta dama sannan ta dama corn flour a cup, jikin kitchen cabinets din ta tsaya tana bin karatun da yake shigowa daga parlour har sun kai suratul D'AHA.
Madarar ta zuba taci gaba da tafasa sannan ta zuba corn flour din ta daure da yayi dai dai yanda takeso ta sauke ta Kara Masa condensed milk a cikin ta juye, hadesu tayi a babban tray tayi ta nufi falon, Nan akan dining table ta jero komai sannan ta koma ta dauko sauran tarkacen su cups.
Kitchen din ta koma ta gyara gurin tas, sannan ta koma daki wanka ta shiga, tana fitowa ta shafa lotion dinta tayi simple makeup ta saka saka turarikanta na jiki dasu humra Nan da Nan jikinta ya shiga fitar da wani fitinan Nan kanshi, doguwar rigar Dubai Mai kananun stones pink mai duhu ta saka rolling tayi dan Vail din
rigar milk colour sai ta fito balarabiyarta sak Dan idan ba kaji tayi maka Hausa ba bazaka taba cewa tasan ko zo da Hausa ba, tayi kyau matuka yarintarta ta fito sosai idan ka kalli fuskarta very cute sai wani annuri take fitarwa.
Parlour ta fito gurin dining din ta nufa cikin takunta das das. Tana mamakin Ina ya shiga Dan ko motsinsa babu har yanzu ita kuma bazataje bedroom dinsa ba, idan ya gaji da zaman dakin ya tunda ba yaro bane yunwar cikinsa ta fito dashi. Kunun madarar ta zuba da masar Irish din kwara biyu kawai ta dawo main parlourn ta zauna tana ci tana sauraren karatun, sai da ta gama ta Kai kayan kitchen ta wanke sannan ta dauko Wanda ta zubawa baba Mai gadi ta nufi kofa a hankali take tafiya a cikin harabar gidan iskar bishiyoyin da sauran shuke shuken suna kadawa gwanin sanyi can gurin gate taga baba Mai gadin ya nufa da sauri da alama budewa zeyi.Dan tsayawa tayi daga gefe idonta Yana kan gate din Dan taji dirin mota zata shigo cikin kankanin lokaci motar ta shigo ido cikin ido sukayi da shi shine yake driving din gabanta ne ya bada ras ras Kuma ya kafeta da fitinannun idanunsa cikin gwaninta ya nufi parking lot, Sameer kuwa Kamar wani sakarai haka yake kallon zahrar Yana tsarkake suna Allah a zuciyarsa ya ganta har kusan hudu Amma da alama ganin tsoro yake Mata sai yau yaga zahirin zahrar, da sauri baba Mai gadin ya karaso yana gaisheta ta Mika Masa Dan Karamin basket din ta juya da sauri ta nufi kofar falon har Kamar tana dan sassarfa ta shige ciki, harta wuce idanun Mahmud suna binta Nan da Nan yayi kicin-kicin da fuska daman ga Sameer ya tabo shi ga itama da kalar nata shirmen, cikin zafin nama ya kashe motar ya Kama kofar ze bude Sameer ya kamo hannunsa ya rike Yana girgiza masa Kai kafin ya dungule dayan hannunsa irin na roko din nan yace.
"Pls Dan Allah cool your temper kada kaje mata a haka kayi Mata uzuri Batasan Kai ko waye ba, Kuma infact ma laifinka ne ka tafi ka barta a gida har zuwa wannan lokacin Kuma tana ganin hakan da tayi shine dai dai koni nayi supporting dinta hakan shine dai dai ta nuna maka tasan haqqin abinda ka bar mata amana" .
A Dan fusace ya kalli Sameer.
"Nine na Bata amanarsa da izuninwa ta fito nan wato. ya kalleta yanda yakeso ko? Matata take kaiwa Mai gadi abinci wannan wane irin zubewar aji ne a gurina? Dubi fa yanda ta fito? Ko baka gani ba?"
Ya fada yana kallon Sameer.
"Ni banga wani Abu na rashin kyautatawa ba a shigarta, kawai dai idonka wani Abu ya nuna maka na daban gaskiya".
Hannunsa ya zare daga cikin na Sameer din ya bude kofar a hankali ba Kamar dazu ba zagayowa Sameer yayi ya rufe motar yabi bayansa Dan Idan ya Bari ya shige irin na jiya ze masa ya ajeshi a waje, kofar ya bude wani sanyi da kanshin girki Dana turarikan daki sukayiwa Sameer sallama Bata Nan sai tv a kunne ana karatun har lokacin.
Direct gurin dining Sameer ya wuce yana fadin Bari na Fara da Nan Idan na gama ma gaisa tunda ba bako nake ba ya Fara budewa Yana kallon Mahmud Yana fadin.
"Tab da alama Allah ya tarfawa garinki nono irin wannan delicious".
Gaba Mahmud yayi Bai tanka Masa ba ya shige ciki.
Kofar bedroom dinta ya kalla har dariya take bashi bilhaqqi da gaske tsoransa takeji bare Kuma da jiya ya Dan motsa mata Jamiyya.
Ta Dan Dade a bedroom din nata daga baya ta bawa kanta kwarin Gwiwar ta fita ko banza bazata bada kofar da wani na waje ze gane da 'yar tsama a tsakaninsu ba Kar a Raina Mata wayo, fuskarta ta Dan Kara shafawa powder kadan ta Dan Kara fesa mouth freshner Mai kamshi apricot ta nufi kofa tana budewa saura kadan yau ma suyi karon, da sauri taja Baya. Shigar kananun Kaya yayi as usual dan zaman da sukayi ta fashimci kamat ya samu wani freedom ne na sakewa, trouser black da milk T-shirt ne a jikinsa hannunsa daure da agogo sai waya a hannunsa. Baya tayi da sauri tana Dan zare idanu Dan ba Karamin tsoro taji ba, Shima kallon ta yake Kamar ya rungumota ko yaji relief na abinda yakeji a zuciyarsa, amma sai ya share ya Mika hannunsa ya kamo nata ya natso da ita kusa dashi Sosai Yana Fadin "kin tashi lfy?".
Ya shafi gefen fuskantar, cikin siririyar murya tace masa
"Ina kwana? Shiru yayi Kamar beji ta ba, ya janyo ta suka Fara tafiya a cikin corridorn, sai da suka Fara gangara steps din taji yace waya Baki izinin fita gurin watchman din can?"
Ya Dan matse hannunta dake cikin nasa.
"Wash!!! Allah ta fad'a ba tare data shirya ba. Dan da gaske matsewar ta shigeta dago Kai tayi cikin narke fuska Kamar zatayi kuka dai dai lokacin Sameer ya dago Kansa daga daddana wayar da yakeyi Jin maganarta Sam beji tahowarsu ba wani irin perfect match couples ya gani sun masifar dacewa da juna ya Dade bega ma'auratan da suka burge shi kamar su ba, a zuciyarsa yake Fadin.
"Masha Allah".
Zahrar Tace masa.
"Ba kowa, Dan Allah ka sakar min hannu wlh zafi...."
Ta fada cikin shagwabar da Bata San tayi ba.
Murmushi Sameer yake ta saki daga inda yake Dan ba karya yasan muhmud yayi dacen da Basu zata ba abun kamar a film yake ganinsa. Dan lokacin da suka Fara ganinta da Kuma furucin da shi Mahmud din yayi ashe Allah ya karbi addu'ar.
Dan gyaran murya Sameer yayi Yana kallon Mahmud din tare da fadar.
"Yallabai a bar madam ta karaso mu gaisa Mana ni ba mazauni babe gaba nayi daga Nan"
Ya fada da sigar zolaya duk yaga har yanzu kamar Yana Jin zafinsa tun maganar da yayi masa na Safnah.
Sassauta rikon hannaun yayi suka ida gangarowa directly dining area ya nufa yana zuwa ya ja Mata kujera ya zaunar da ita sannan Shima ya janyo ya zauna.
Gurinsu Sameer ya karaso daga inda yake zaune Yana fadin.
"Madam barka da Asuba kingan ni sai yau ki?".
Ya fad'a yana Zama kusa da Mahmud.
A kunyace ta amsa da "lfy kalau Ya Sameer ya kaje gida? Ina madam?"
"Komai lfy ya hakuri damu?".
'yar dariya tayi kafin ta Mike ta Fara bude abincin Wani daddad'an kamshin ne ya doki hancin Mahmud har Saida ya lumshe idonsa, Dan kallonsa tayi sannan ta kalli Sameer tace "me za'a zuba?".
Kai Sameer ya girgaiza Yana fadin "ai ni na riga ku ci tun shigowarmu naji bazan iya jiran masu gidan ba saina shide Ina jin kamshin delicious Amma ace saina jira".
Ya fad'a Yana dariya.Dan murmushi Mahmud din yayi.
"Wato ko Ina saika nuna halinka ko?".
"Pls zuba min kawai".
Kallonsa tayi kasa-kasa, tace "Toh"
Masar dankwalin turawan ta zuba sannan ta zuba pepper chicken din ta tura Masa sannan ta zuba kunun Madarar sannan ta koma ta zauna a darare.
Wani cup din ya zuba kunun Madarar ya dauko da fork ya matso kusa da ita da plates din abincin yace.
"Oya saka hannu muci".
Ya wani hade gabas da yamma alamun ba wargi Kai ta shiga girgaizawa alamar ta koshi Shima ture abincin yayi Yana duban Sameer.
"Muje kawai"
Ya fad'a yan Jan kujerar baya.
"Zanci".
Ta fada a gajarce.
Komawa yayi ya zauna Yana fadin "fine tunda zakiçi gara Idan mutuwar zamuyi mu mutu tare Dan naga abinda Mata suke yayi kenan Idan aka Basu Wanda ba shine zabinsu ba su kashe shi su auri wanda sukeso".
Tunda ya Fara Kora bayani Zahra tayi masa kur da ido tana Mai maita.
Kai Sameer ya shiga girgaizawa Yana mamakin wani sabon hali da Mahmud din ya tsira, yaga alama nema yake ta Hana yarinyar Nan sakat.
Ita Kuma tunda ta furta zanci Bata Kara tofa ko kalma daya ba, sai kawai ta dauki fork ta cako Irish din ta Kai bakinta ta tauna ta hadiye, pepper chicken din ta dauka taci ta dauki kunun Madarar ma ta Sha duk Yana kallon ta shi kuwa Sameer Yi yayi Kamar Allah Bai halicce shi a gurina ba.
Tana gamawa ta tura kujerar da take Kai baya sannan ta dubi shi ido cikin ido tace.
"Gashi naci idan kana tunanin zan zuba maka poison a abinci kayi kuskure lalacewar tawa Bata Kai haka ba, Idan na kasheka wace riba zanci? wato ka tafi lahira free ko? duk lodin zunuban daka dauka niga sakarai na lodawa kaina, to Bari na fad'a maka ba saina aikata zunubi irin haka zan rabu da Kai ba A'a salin alin kowa ze kama gabansa ni da Kai tunda daman masu iya magana na cewa tsintacciyar magen Bata mage nasan komai Daren dadewa zaka koma inda ka fito".
Ta fad'a Tana wurga masa harara ta wuce ta kyalesu batabi ko takan Sameer da yake fadin "Allah ya huci zuciyar amaryarmu".
Da ido Mahmud yabi Zahra har ta bacewa ganinsa "Wai shi yarinya kamar wannan zata saka shi gaba ta fada Masa son ranta amma yayi shiru Yana kallon ta".
Sameer ne ya katse Masa tunanin da yake.
"Dan Allah kada ka koya matsa tsiwa wlh da gani Bata Saba ba, bakaga jikinta har rawa-rawa yake ba".
Ya fad'a Yana kallonsa.
"Jikinta na rawa kenan Kare mata kallo kayi har kaga jikinta na rawa ni ban gani ba?".
"Subhanallahi! Wace irin magana ce haka wlh ba haka nake nufi ba, Bari naje kawai sai munyi waya".
Ya Mike Yana aje rafar dari biyar guda biyu Yana fadin "A bawa madam ace Mata na wuce tunda ka Hana muyi sallama".
Ya biya Kan center table ya dauki keys dinsa yayi gaba tunda yasan ba magana Mahmud ze Masa ba Dan da gaske yazo wuya yanda yanayin fuskarsa ta nuna.
Bayan fitar Sameer, Mahmud kasa ko motsin kirki yayi wai shine tsintacciyar magen? Da gasken gaske maganar ta dokeshi kwafa yayi Yana fadin zakiga tsintacciyar mage iya ganinki sai kin gane bakin rijiya ba gurin wasan makaho babe".
Ji yayi kwata kwata abincin ya fice masa raga Rai duk yanda yake jin yunwa ture abincin yayi ya Mike ya nufi bedroom dinsa Bai jima ba ya fito cikin shigar yari filtex fari dinkin boda da farar hula a Kansa Yana baza qamshinsa na Ibada, yayi waje.
Tunda Zahra ta Fadi maganar dake ranta taji zuciyarta wasai, gefen bed dinta ta zauna tana mita.
"Haka kawai saika wani ringa sakarmin magana ba control duk abinda yazo bakinka saika fad'a mini, Wai na saka wani Abu girkinma ba saina Kara yo da Kai ba sannan na Zama suspect daman saboda A kashedin Ammah ne yasa nayi, kwana biyu amma kamar na shekara duk ka matsa min ka karbe min waya nayi Shiru na Zuba maka ido Naga gudun ruwanka, na fita mikawa bawan Allan Nan abinci kace da izininwa? Haka kawai ka zamar min karfen kafa".
Ta fad'a Tana kwafa.
Tunda gari ya waye Ammah Bata zauna ba shirye-shiryen tafiyar Inna maimuna take wadda zata tafi yau, cikin Shirin fita unguwa Mama ta shigo lokacin Ammar na zubawa innar kilishin da Abba yasa akayi Mata zaunawa tayi tana Fadin "Inna yau zakiyi Mana ta Baki wlh ba dadi".
"Kayya Hajiya Rabi banda abun yazo da sammazi Aida na jima da tafiya gida daga zuwa biki na share our na zauna kinsan da Ardo Yana Raye hakan ba zata faru ba yaushe ze Bari".
"Haka ne Kam Allah yayi musu Rahama".
"Amin" su Inna suka amsa.
Leda mamar ta aje kusa da innar tana Fadin.
"Gashi Inna ba yawa Allah ya kiyaye hanya ni fita zanyi unguwa nasan kafin na dawo kin tafi".
Gdy innar da Ammah sukayi Mata ta tashi tana yiwa innar fatan sauka lafiya.
Sai bayan ta wuce ne innar ke tambayar Ammah ina Hameeda ne Naga tun she jiya da safe bata qara ganinta ba.
"Jiya kina barci tazo Nan Wai ta tafi Jos gurin yayar mamansu larai".
"To ba laifi