Showing 69001 words to 72000 words out of 122700 words
dalilin da Zaki shiga ko gidan daya daga cikin families din DANGE ne kiyo kallon duniya me Kika gani a Nan kedai Allah ya Kai damo ga garawa kawai, Dan dai a wannan zuwan da nayi sokoto naje yiwa zainab din barka naji wasu a cikin family din sunata hirar MM DANGEN Wai ko ya bar kasar ya koma turai tun bayan samun wata matsala Mai zafi a cikin family din wadda ta tada kura har rayuka suka baci".
Da ire-iren hirarrakin suka karasa gidan barkar.
...
Tana zaune a Nan parlourn ya fito cikin kananun kaya da karamar leda a hannunsa direct inda take ya nufo ji tayi gabanta ya Fadi.
"Ya Ilahiy" ta fada a zuciyarta.
Gefenta ya zauna Yana Fadin
"Wash!! I am tired wlh samo min ruwa Mai dan sanyi".
Yayi maganar yana dan matsowa jikinta. Da sauri ta tashi yabi ta da kallo Yana kissima abubuwa da yawa a kanta kunyar ta tayi yawa yasan sai yasha fama kafin ya rabata da ita yanzu dai most important thing ya samu shakuwa da ita sosai.
Ruwan da farm fresh yogurt da snacks ta bawo Masa, idonsa a limshe Kamar me barci Amma Yana kallon ta yanda take tafiya kamar me counting steps sai rausaya take.
Table coffee ta janyo ta Dora tare da bude Masa ruwan ta Zuba duk Yana kallonta.
Ajewa tayi ta juya zata wuce taji hannuwan mutum duka biyun ya zagaye k'ugunta ya mannata a jikinsa ta baya, yayi Mata bazata Dan ko motsin mikewarsa bataji ba ko alama, a tare suka sauke ajiyar zuciya juyota yayi gabadayan ta suna facing din juna Yana Mata wani duban kasa-kasa.
Narke fuska tayi Kamar zatayi kuka tace Masa.
"Menene Kuma? gafa ruwan Nan na kawo maka".
Fuskarsa ya matso da ita dai-dai tata yace.
"Haka ake tarbar miji? Ki bani abincin yunwa nakeji fa, tun safe banci komai ba tunda kika tada min hankali abincin ya fice min daga Rai, waini Kika kalli kwayar idona Kika gasa min maganganu son ranki ko?".
"Ni me nace, cewa fa kayi zanyi poison dinka ni banji haushi ba sai kai, kisa fa? To me kayi min, ni na daina abincin ma ba shike nan ba ban dafa ba bare na zuba maka guba".
Ta fada tana kokarin zame jikinta, Kara gyara rikon da yayi Mata yayi ya nufi two seat da ita a jikinsa kan cinyarsa yayi Mata masauki, ya Kai hannunsa daya ya zame veil din da tayi rolling gashin ya shiga shafawa yana fadin.
"Nifa da Wasa nake Miki dazun bada niyyar na bata Miki rai ba na fada, so I am very sorry Baby in Sha Allah bazan Kara fada ba, na Saba haka nake yiwa kakata Hajiya Inna a irin wannan lokacin na break shine na tunata da ita na fada Miki kema Ashe lefi zanyi, yanzu muje na tayaki ki Samar Mana light Abu muci bana son cin Abu Mai nauyi sosai da dare nasan kafin mu Gama anyi magariba ko"
Ita dai tayi tsumu tsumu duk ta takura fatan ta ya saketa ta fece tunda Allah yasa yanzu ba 'yan tabe taben bane a Kansa a iya gashi kawai aka tsaya.
Dagota yayi daga jikinsa ya rike hannunta kamar wata 'yar baby suka nufi kitchen, ledar daya shigo da ita ya dauko ya Dora a Kan cabinet din kitchen din Yana Fadin "zo ki cire wadan Nan daga ciki.
Kayayyakin amfanin gida ne masu yawa harda su biscuits su chocolate, sai da ta saka komai a muhallinsa sannan ta Fara hada abinda zatayi, kujerar kitchen ya samu ya zauna Yana kallon movement dinta friend spaghetti Mai vegetables tayi sai tayi gasmeat.
Lokacin data Gama komai an Fara Kiran sallah.
Tare suka fito ya mannata da jikinsa a haka ya nufi bedroom dinsa da ita suna shiga ya zaunar da ita Kan sofa ya wuce toilet.
Sai daya rufe kofar sannan ta tashi ta wuce nata dakin wanka take sonyi.
Koda ya fito Bai ganta ba beyi mamaki ba yasan za'ayi haka, lokacin daya leka ya fada Mata ya wuce masallaci tana toilet.
Saida yayi insha'i sannan ya shigo gidan abincin Mai gadi ya dauko ya futa ya Mika masa, daya dawo be nemeta ba,sport news ya kamo yana kallon labarun wasannin da akayi Bai gani ba.
Zahra Kuma da tayi sallah saita zauna tayi Azkar na yamma da Bata samu tayi ba, data Gama tayi shafa ta saka riga da siket English waars combination din milk da maroon tayi rolling da milk veil tayi kyau kamar ka dauke ka boye body mist kawai tayi amfani dasu kusan kala uku cikin Wanda ta gani a cikin locker din mirror dinta sai kamshin ya Bata wani irin Dadi Mai kwantar da zuciyar me shaqarsa.
Plat shoes tasaka a kafarta ta nufi falon,jin gidan shiru batayi tunanin Yana Nan ba Saida ta shigo sosai ta ganshi a kishingide da remote a hannunsa Yana kokarin canza tasha.
Tashi yayi daga kishingidar ya zauna sosai Yana binta da wani mayen kallon, tunda suka hada ido sau daya Bata Kara yarda ta kalleshi ba.
"Zo ga wayar ki Nan tunda Naga itama kinyi zuciya da ita kin bar min".
Ya fada yana Mika Mata hannunsa alamar tazo ba musu ta nufo shi cikin takunta na nutsuwa, shi komai yarinyar Nan tayi burgeshi takeyi ga uwa uba Kuma ya fuskanci tana da tarbiyya da biyayya sabanin yanda yake kallonta, Bai zaci zata kwantar da hankalinta haka ba sai yaga ta tattara komai ta aje gefe abinda ya fuskanta kawai dai Bata daukar raini.
Tana karasowa saita zauna kusa da kafafunsa a kasa taki zuwa gurin hannunsa da yake Miko Mata. Dan murmushi yayi Shima ya sauku Yana facing dinta da karamar ledar dake hannunsa, Mika mata yayi."Gata Nan ayi hakuri ki hada ta batirin ma yana da full charge da sim a ciki, duk numbers dinki important suna ciki.
Wayar ta bude sabuwa ce Kar jujjuyata ta Fara tafi wadda ya Fara Bata tsada nesa ba kusa ba kallon tuhuma ta Farayi Masa tana girgiza Kai tare da Mika masa wayar tana Fadin.
"A Ina kake samun irin wadan Nan wayoyin na mahaukatan kudi wlh ba ruwa na ka rike kayanka bana so ka maido min tawa ta asali kawai".
✨✨
✨✨
✨💎AUREN HUCE HAUSHI💎✨
Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Aminci su tabbata ga Annabin Rahama Muhammad s.a w.w.
Page 25
📖🖋️
________Dariya ya kama harda hawaye abinda bata taba gani ba.
Sororo tayi tana kallonsa, ita bataga wani abin dariya ba a maganarta, hannu ya Mika ya karbi wayar kunnawa yayi ya Mika mata Yana kashe Mata ido tare da d'age gira.
"Kina son kisan inda nake samun mahaukanta kudaden Nan ne?".
Kai ta gyada Masa.
"Good ki Bari sai ranar da Kika Zama ni na zama ke na mallaki kayana, a ranar nayi Miki Alkawarin sanin komai nawa na duniyar Nan, Idan Kuma yanzu you are ready za'a taimaki Dan Malam a lullubeshi da bargon ni'ima to? yanzu kuwa kisha labari har wanda Baki nema bama zan fad'a Miki, tunda ke inda nake samun kudi kawai Kika bukata baki son sanin waye ni?daga Ina nake?meya kawoni garinku? Gasu nan rab'ab'a da yawa, to ki rubuta ki aje har abada ni Mahmud bazan tab'a ciyar dake ko shayar dake ko wani Abu na jindadin rayuwa da haramun ba, duk abinda na Baki ki tabbata da gumin halalina na nema, kinga wannan wayar da kudina na saka na saya Miki,wato kina tsoron kada na Sato kayan mutane na kawo Miki ko?"
Kai shiga gigizawa.
"Ni ba cewa nayi kayi sata ba, gani nayi kana ta abubuwan da sai Mai wadata ne ze iya yinsu Kai Kuma Naga...." Sai kuma tayi shiru tana kallonsa.
"Oya continue Mana,kinyi shiru wato Kinga bana aikin komai ko?".
Shirun tayi Bata Kara cewa komai ba.
"Tashi ni ki bani abinda zanci idan na biye Miki da wannan yarintar taki sai yunwa tayi min illah kisa a Fara gulmarki ace kina barina da yunwa, ganshi kin sani azumin da Babu lada".
"Ba Kaine kayi zuciya ba ka tafi kabar abincin"
Ta fada a shagwabe.
"Ki tashi ki bani kada lissafin ya canza fa"
Ya fada yana matsowa jikinta sosai, da sauri ta Mike ta nufi dining inda ta jera abinci.
Table mat ta shimfida a Kan carpet din sannan ta dauko abincin ta aje.
Plate biyu ta dauko dayan ya janye.
"Ki Zuba Mana a plate daya ya Isa ai Kuma indai Ina gida plate din mu daya tunda Kika yimin horon yunwa yau daga Wasa Dan kawai kewar Hajiya ta ta kamani shine Kika horani duk ranar dana kaiki gabanta saina fada Mata tasan irin zaman da zatayi dake, ni Dan gata ne a gurinta bana laifi zakiga yanda take sona".
"Ko?" Ta fada tana zuba abincin a plate, Dan tura Masa plate din tayi kusa dashi "Gashi Nan ni bana Jin yunwa".
"Ashe zan Miki dura wlh, sai kinci kuji min yarinya da kinibibi Wai so kike da karfi sai kin koya min surutu ne? Kin iya kalato abin magana da wani bakinki chut".
Ya fada yana shafo pink din lips dinta.
Taci Amman ba wani na kirki ba da gaske abinci Bai dameta ba barta dai da 'yan ciye-ciye.
Bayan sun gama ne ta kwshe kayan ta gyara gurin duk Yana kallonta komai tayi kyau yake mata gata ba wata babba ba sai dai akwai Sama da kasa masha Allah.
Lokacin data gama ne ya yafito ta da hannu,a hankali ta nufo shi kamar me counting steps sai rausaya take, wani yawu ya hadiye, Dan risinawa tayi a gabansa duka hannuwanta ya kamo ya zaunar da it kusa dashi.
"Zaki rakani unguwa?"
Ya fada Yana zame Mata veil din da tayi rolling gashinta ne ya bayyana biki sidik dashi sai walqiya yake yasha gyara ga kamshin hair spray Yana tashi.
"Eh zani Bari naje na shirya".
ta fada Tana kokarin zare jikinta daga nasa. Duka hannuwansa yasa ya riko kugunta ya hade ta da jikinsa.
"Ina zaki?wane irin Shiri zakiyi kinsan inda zamu ne kike sauri?".
Lakwas tayi a jikinsa da karfi da yaji so yake ya Saba mata da Zama a jikinsa gashi baya ko Jin jauyin taba Mata jikin sai dai idan Bai soba.
"Bazaki tambayi inda zamu ba, kina Neman sake canza Kaya".
"Nasan gida zamuje Mana".
"Ai kece gidan, kinaji da so nake muje gidan da gaske mu roki alfarmar a bamu aron me aiki daya Wadda zata zauna min dake kafin na dawo".
"Kafin ka dawo? Ina zakuje?".
"Au Ashe ban fada Miki ba, aikin NGOS din Nan ne ya taso suka gayyace mu zuwa meeting da zasuyi a UK Kinga ai bazan zauna ba da dollars ko stalling founds suke biyan mu, idan Allah yasa na samu da Dan auki Kinga na Kara jarina tunda Naga Nima Ina sha'awar siyar da materials har munyi magana da Abba yace ze bani rumfa daya a Muda lawal market na gwada ko ina da nasibi a cikin sana'ar, sannan Habib ma munyi magana zamu Fara siyar da spare parts na motoci a nan Muda lawal market din dai".
"Allah ya bada sa'a, Kuma idan ka tafi sai yaushe zaka dawo? Ko kaima shike Nan abinda yake faruwa Dani ze faru a kanka kaima, kada ka tafi ka barni Dan Allah tunda nasan ba Sona kake ba baka ni akayi sadaka, Dan Allah ka taimaka ka kaini Jordan tunda Ina kudin flight kawai ka taimaka ka fitar Dani daga kasar da sunan Kai zaka tafi dani, bana son Ammah ta qara shiga cikin damuwa a kaina wlh Batasan tashin hankali ba Sai Dana isa aure Kullum idan kaga Ammah a cikin tashin hankali to a kan lamarina ne ni Kuma yanzu bana fatan na qara ganinta cikin bacin rai ta dalilina, kaje ka fada musu zaka tafi Dani ko Kano ne ka Kaini na zauna gidan su bestie kafin na samu visa, nagaji da Kasar nan wlh Ina da gata Amma sai walagigi rayuwa ta takeyi anan Dan Allah kayi min wannan alfarmar Koda ita kadai zakayi min ta karshe a zamana da Kai".
Ta kifa kanta a jikin kafad'arsa ta saki wani kuka Mai tsuma zuciya.
Bai hanata ba ya dai Kara matseta a jikinsa Yana shafa bayanta yasan abin Yana cin zuciyarta ne bata rasa komai ba amma an dabaibaye Mata Jin dadin rayuwa kamar yanda Baba malam ya fada masa. Sai da tayi Mai isarta ya dago kanta daga jikin kafadar tasa.
"Kiyi hakuri kowa da irin tasa jarabawar ke taki a haka tazo, Kuma waya fad'a Miki zan tafi na barki bazan dawo ba? Waye kuma yace Miki bana sonki? Kinsan tun tsawon lokacin da nake dakon soyayyarki kuwa? Tun Baki san meye son bama yarinya share hawayen ki Mahmud naki ne har abada, dole kije Jordan ke me gida sukutum a can.Amma yanzu kiyi hakuri nema zani idan Kuma na zauna bakya son tafiyar saina fasa Sameer yayi komai kawai nace madam ta Hana".
"Kaje kawai idan baka dawo ba nasan abinda zanyi".
"Keh! kina da hankali kuwa me zakiyi wlh zan turaki gurin Hajiya Inna duk da ban shirya zuwa yanzu ba kawai ki Kira min ruwa, zaman Allah nakeyi zamanki nakeyi badan ke ba Dana Dade da barin garin Nan".
" Ni Kuma?"
"Off course"
Ya fada da karfin gwiwa.
"As how?"
Share ta yayi kamar bai jita ba.
"Tashi ki rakani kada dare yayi, dauko Mana key din motarki na dana kada na tafi ban Sanya albarka ba, ki canza shiga kada a kalle min kayana" fada Yana mikar da ita daga jikinsa.
Duk kin haye min cinya kinsa sai ciwo take min".
Ya fada Yana Mata wani smile.
Bata kula shi ba tayi gaba abinta duk zuciyarta ba Dadi sannan tana jujjuya maganganunsa a zuciyarta, kinsan tun lokacin da nake sonki? Danke nake zaune a garin Nan gasu Nan dai da yawa.
Saida ta sakarwa Kanta ruwa sannan ta shirya agurguje ta saka wata Riga da siket na atamfa super dinkin ya zauna das a jikinta ta saka mayafin da yayi matching da atamfar ba tayi amfani da turaren kaya ba body mist kawai tayi amfani dasu a jikinta kusan kala uku, sai ya bada wani sansanyan kanshi Mai dadi. Tana gyara gyalen ya shigo dakin tsayawa tayi tana kallonsa shida yace unguwa zata raka shi sai gashi da Riga armless da wandon ta farare tas na kamfanin Adidas sai taga kwata kwata ya canza Mata ya koma irin 'ya'yan hutu din Nan na gaske wadanda Jin Dadi ya gama ratsa su yayi wani irin fresh da shi.
Matsowa yayi kusa da ita Yana Dan watsa hannu irin dai na isassun yaran. Mayafin ya kama ya ida rufa Mata a kanta.
"Kallon fa na menene? Kona canza Miki ne?".
Kai ta girgiza Masa.
"Baba son body language fa ki bude Baki kiyi min magana".
Yana janyo ta jikinsa.
"A'a kawai dai da naji kace unguwa zan rakaka kuma na ganka da......"
Sai tayi shiru.
"Karasa Mana sai Kika ganni da shigar nigas ko?"
Shirun dai tayi.
"Idan Ina tare da iyalin dole na sake, kema da nace ki canza ai na Shan iska nake nufi ba Wai irin wannan ba, zo muje ki canza yawon Shan iska zamu ki min hira ki bani labarin ki tunda ke bakya bukatar nawa ki bani happiness a wannan Daren yanda duk inda nake na rinqa Tino da abubuwan su zamar min kamar kina kusa Dani".
"Ni dai Dan Allah ka barni haka muje kawai"
"Dauko key din to muje dare nayi Kuma Ina son ganin Baba malam da Abban mu, ko ba namu bane?"
Ya fada Yana kallon ta, an samu cigaba, tunda ko banza tunda ya mamnatse ta take iya kallon idanunsa ba kamar da ba da Bata yarda ta kalleshi.
"Namu ne". Ta fada a hankali, badan Yana very closer to her ba da ba lallai yaji me take fada ba.
"Oya let's go".
Ya fada Yana nufar kofa, saida ya kashe electronics na gidan sannan suka fito Yana time da karamar luggage a hannunsa,Kati ya curo daga cikin wallet dinsa ya saka a kofar ya rufe, daga nesa Mai gadi ya hangesu sun nufi parking lot din gidan inda motar daya take ajiye, a ransa yake fadar "duk inda wannan Dan ya fito Dan mafita ne ba irin yaran Nan bane lalatattu kamar yanda aketa surutun abun masu kushe da ganin rashin kyautatawar su Alhaji nayi masu gani kyautatawar nayi".
Yana can Yana tunani Bai ankara ba yaji Karan Horn alamun har sun karaso Yana can Yana nashi zarafin.
Da gudu ya tashi Yana fadin Ayi hakuri nayi zurfi gurin tunani ne, a dawo lfy Allah ya tsare".
Horn ya yi Masa suka fice daga gidan.
Suna barin gidan sun hau babban titi sosai motar su mama ta doso kofar gidan. Dan saida suka hada turaren wutar ya kammala aka zabga Masa turarika masu mahaukatan kanshi da mazubai Wanda dole yayi attracting mutum.
Daga Dan besa direban ya tsaya Mama da Asabe suka fito Asabe na rike da ledar Mai tambarin gurin Saida turarukan wutar dasu humra suka nufi gate din gidan, Asabe CE tayi knocking ta 'yar karamar kofar jikin gate din ya leko ya gane Mama tunda ya jima a unguwar sai dai ita ba lallai yasan shi ba.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin. "Hajiya kune haka barka da zuwa ina wuninku".
Ta rusuna ya gaishe su.
'yar dariya Mamar tayi tare da amsawa kafin tace masa.
"Munzo Kara duba Zahra ne tunda tazo ban samu mun shigo ba sai yau"
Cikin nuna girmamawa malam Sani yace. "wallahi kuma anyi sabani yanzu ba dadewa suka fita da Mai gidan da kun lura ma inaga kunyi kiliya dasu a lokacin da zaku shigo su Kuma sun fita".
Turus sukayi wannan ta kalli wannan.
"Ina suka fita daga kawo yarinya ko sati Bata rufa ba?" Ta fada da alamun bacin rain a maganar ta ta.
"Wlh nima ban Sani ba tunda ba hurumina bane sanin hakan ba, sai dai ko Zaki Kira ta a waya idan basuyi nisa ba sai su dawo".
Mama Bata taba danasanin rashin karbar number zahrar ba irin yau.
"Ba komai ga sako Nan ka aje mata idan Allah ya kaimu gobe Asabe zata dawo tayi Mata bayaninsa"
Ta fada tana kallon Asaben, Wadda ledar ke Hannunta, da