Showing 12001 words to 15000 words out of 122700 words

Chapter 5 - Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novel

07 Feb 2025

857

idonka ya koyi kunya? Naga sai wani sadda Kai kake, nifa lamarinka ya Fara bani tsoro na rasa wace alkibla ka kalla kazo garin mutane ka Mike kafa kana wata irin rayuwa a takure nace zan dauki mataki ka aje min sharadi, da kasan bazan it's tsallakewa ba, yanzu Kuma Rana tsaka a tarko aure Kai kadai kamar marar gata sai walagigi kake alhalin kana da madafa".
Tsaki yayi " kana da matsala wallahi ko me zance fada maka bazaka Gane ba, amma idan lokaci yayi zaka fashinmta,yanzu duk bayanin da zanyi maka ba fashinmta zakayi ba, kawai mu bar maganar kawaai"
Kanshin turaren ne ya alamta musu zuwanta. sallama tayi cikin siririyar muryarta.
Sameer ne ya amsa Mata sallamar a zahiri Dan shi Dan gogan a saman lebensa ta amsa sallamar. Sameer din ne ya Dan Mike Yana fadar.
"Masha Allah jiki yayi sauki kam, "Bismillah". Yana nuna Mata kujerar gefen Mahmud. Kai ta dangirgiza Masa tana dan murmushi kasa kasa.
A Nan kan carpet ta zauna daga gefe tana gaishe da su a jimlace.
"Lafiya kalau"
Sameer ya amsa Yana fadin "ya jikin naki?"
"Alhamdulillahi" ta amsa masa.
Sai Kuma duk sukayi shiru, ganin lokaci Yana qurewa Sameer ya Mike tare da kallon Zahra Yana fadin " To madam bako zeyi halinsa Allah ya bada zaman lafiya. Amma fa sai kina hakuri da halinsa gaskiya ba kirki ya cika ba Ina son idan na dawo Naga canji na zahiri a tare dashi, sunan Sameer Sa'ad koko, zeyi miki cikakken bayanin koni waye a gurinsa Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a mai..albarka Allah yasa next year by now muna bkin suna"
Da sauri Mahmud ya kalli Sameer a zuciyarsa Yana fadin "Allah ya shiryeka Sam baka girma".

A hankali tace " Mun gode kwarai Allah ya tsare ya kiyaye hanya".
"Amin" ya amsa Yana kallon Mahmud.
"Ni zan wuce saina sake shigowa ayi kokarin ganin aikin Nan ya kammalu".
Ya fada Yana nufar kofar fita.
Sai lokacin Mahmud din yayi magana "pls ka jirani minti biyar Dan Allah".

"Idan ya wuce haka Kam...."

Ya fice ba tare daya karasa fada ba.

Tunda Sameer din ya fita take wasa da karamin zoben da yake hannunta. Bata dagon kalle shi ba shi Kuma Bai tofa tasa ba amman idonsa Yana kanta, Kare Mata kallo yake Yana fadar "Masha Allah tabarakakkahu ahasanil kaliqin".
Tsam ya taso daga inda yake ya sauko kasa inda take zaune.
"Ya jikin naki?".
Ta tsinkayi maganarsa kusa da ita daf Sam bataga lokacin daya taso ba.
Cikin daburcewa saboda kusancin nasu yayi matukar yawa ji tayi kamar ma iskar gurin ta tsaya sai munfashinsa take shaqa kawai.
A mamakance taga yasa hannunsa ya dago fuskarta suka hada Ido hudu dashi. Da sauri ta runtse idanunta zuciyarta na wata irin bugawa.
"Bude idon Kona Baki mamaki".
Marmar ta Fara da idon tana budewa a hankali Amma taki kallon nasa idon.
"Ya jikin?".
Ya Kara maiamaitawa, a hankali ta bude bakinta tace "da sauki"
Gamshin Lister mint ne ya daki fuskarsa. Banda Yana daf da ita ba yanda za'ayi yaji abinda ta fada.
"Allah ya Kara lafiya".
"Ameen"
Ta fada.
Hannunsa ya cire daga fuskarta yana Dan furzar da iska daga bikinsa ya Mike tsaye, a hankali ta sauke wani numfashi.
A bazata taji yace "bani wayarki"
Ba musu ta Mika masa, aljihu taga ya saka Yana fadin "ki shiga gida ki kwanta kiyi barci sosai kada ki yawaita hayaniya ki samu hutu sosai, zan tambayi magaji idan bakya hutawa yanda ya kamata ni Ina da inda zan kaiki ki samu isolation, tashi muje ki shiga gida ana jirana".
Saida ta shige ciki kafin ya juya ya nufi gurin da Sameer da Abdul Hakeem suke suna Hira.

Lokacin data shiga dakin ta Samu Aunty Hasana dasu sajida sunzo har da yaran duka.
Da guda ta karasa cikin suka rungume juna da Sajida Nan da Nan sai hawaye itama sajidar kukan ta fara.
Ammah ce tace "Naga abinda ya isheni meye haka zaku tasa mutane a gaba Kuna kuka, to kukan maganin me ze muku aikin Gama ai ya Riga ya Gama Saida hakuri da addu'a kawai".
Uwar dakin Ammah suka shige.
Magaji ne yayi sallama ya shigo da manyan ledoji guda biyu niqi-niqi da kaya Auntyn Hasan na tambayar"daga Ina?"
Ya fice da sauran Yana fadin "ina zuwa Aunty"
Wata ledar ya shigo da ita Yana fadar"kayan dubiya ne aka kawo Mata" ledar daya kawo daga karshen ya bude rafar 'yan dari bibiyu hura biyu ya dauko daga saman kayan, Aunty Hasana ya
Mikawa yana fadar "gashi nan inji abokin mijinta Wanda suka shigo dashi dazu".
Godiya su Inna maimuna sukayi tayi kamar Yana nan a gurin suna ta Saka albarka.

********* Bayan tafiyar Sameer can gurin aikin gidan suka wuce, ba karamin mamaki Habib yayi ba har ya kasa hakuri ya tambayi Bilyaminu lokacin Mahmud Yana ciki. "Dan Allah wane irin kudi gayen Nan ya bada haka Nan da Nan gidan ya juye ya Zama kamar daukowa akayi daga wata kasar".
"Wallahi Nima bazance ga abinda ake kashewa ba, iya kudin aiki Dana abinci kawai suke a hannuna, bakaga wash bakin fuska ba su biyu?'
"Eh nagansu"
Habib ya fada. "To ai tun jiya sukazo da komai na aikin bakaga Nata'ala ba shima lebura ya koma kaga ai da malam shi yasa a Kira saboda 'yan gyare gyaren amman da masu iyawar sukazo shima yaronsu ya koma".
Ya fada Yana dariya.
"Wallahi Bilya sai a kyaleka Kai kowama sai ka tab'a".
"Gaskiyar kenan ni wallahi burgeni ma yayi tunda baiyi zuciya ba ya tafi, ko banza nasan Yana lure da koma Dan gyaran nasa aikin".

*****A bedroom din ammah Zahra ce da Sajida suke tattaunawa akan abinda ya faru,sunyi iya nasu hasashen amma sun kasa gano bakin zare Sajida ce tace "nifa Zahra Ina hasashen wani Abu akan lamarin ki"
"Kamar me kenan?"
Dan Jim tayi kafin tace "Anya ba asiri ake yiwa duk wani Wanda yazo da niyyar aurenki ba? Ki tsaya kiyi nazarin abun Mana ko mafarkan da kike yi duk lokacin da maganar aurenki ta taso abin dubawa ne"
Dan murmushi Zahrar tayi "kin jiki kema bestie wane irin asiri Kuma,ana zaune lafiya to waye har ze bata lokacinsa da kudinsa gurin yi min wani Abu kawai daga Allah ne kinsan kowa da yanda Allah make jarabtarsa ni tawace tazo a haka".
"Eh na yarda daga Allah ne bana inkari Amma akwai sanadi, inaga gobe ma zan wuce duk da nacewa Umma sai Wednesday Amma na fasa wallahi Rimi zanje gurin Baban Umma na fada Masa ai kinsan shi farin sani Kuma zeyi duk abinda ya kamata tunda ke wani lokacin kanki ba Maths".
Kwarkwar tayi da ido Dan Allah Saji kada ki tafi ki Bari a Gama komai saiki tafin".
Wani kallo tayiwa Zahra "tafiya dole na tafi Amma zan dawo kwana kusa in Sha Allah, kinsan Zama da Baffa yasa Ina Gane wasu abubuwan tunda Yana fadw min ire -iren abubuwan da suka shafi sihiri Kinga yace min duk wani ciwon da yake da lokaci misali ace kullun sai dare mutun yake kasa barci kinsan da matsala, ko ace mace duk ranar girkinta Bata da lafiya ko duk ranar girkinta tana zubar da jini amma idan ta Gama aikin shike nan sai ya dauke babu, ko kamar taki matsalar sai an saka Miki ranar aure sai ana gaf da biki abun yake lalacewa, Kika sani ko Abban naku ma ya Fara irin wannan tunanin ne yasa ya yanke wanna hukuncin cikin sirri ki tsaya kiyi tunani Mana"
Sosai magungunan Sajida sun sakata a tunanin da Bata tabayi ba.
Sauke zazzafan numfashi tayi tana fadin "Allah ya kyauta ni duk kin sakani a tunani wallahi"
Haba "Bestie ai kinsan ruwa baya tsami a banza me ake nema a gurin mace Allah Bai Baki ba Amma sai an Yi abu kama-kama ya lalace zance da muka Dade munayj da Aunty Hasana kenan jiya Kuma ta bain go ahead na naje na faduwa Baffan rimin, tace ma zata fadawa Ammah, ma".
Kiran da Aunty Hasana tayi wa Sajida ne ya katse musu tattaunawar, ta tashi ta fita.

Washe gari duk bakin Ammah suka tafi, Inna maimuna kadai suka Bari sai Amarya taje dakinta zata koma gida.
Part din da bakin suka zauna Ammah tasa su Zilai suka gyara sosai tunda Daman nasu Zahra ne, kafin yamma gurin yayi tas kamar ba'ayi wata dabdala a cikinsa ba.
Bayan sallar insha'i zahra da Sajida suka koma part din.
Suna zaune a kan gado Autan Ammah musaddiq ya shigo dakin da sallama hannunsa rike da leda fara Mai kyau ya mikowa Zahra yana fadin "gashi Aunty inji wannan na gidan Baba Malam din yace a kawo Miki Kuma yana duba ki, Kinga Nima ya bani".
Ya Mika nata 1 k din dake hannunsa.".
"To angode madallah".
Ledar Sajida ta dauka ta bude waya ta gani sabuwa kar a ciki.
"Wow gaskiya ba karya ke! Irin wannan babbar harka haka, Dan Allah Yi min bayani naji yace wannan na gidan Baba malam din waye ko angon namu ne da ake Raina mana ya Fara tsula Mana abun arziki haka?".
Baki ta Zahra ta zunbura.
"Nace Masa Ina bukatar sabuwar waya ne da zai kawo min, ni wallahi a mayar Masa".
Ta fada tana kokarin amsar ledar faga hannun sajidar.
"Ke tsaya da Allah yi min bayani yanda zan gane, Ina taking wayar naji kina wata magana".

"Tana gurinsa tun safe ya karba ni bansan abinda zeyi da ita ba, ya dai ce na bashi kawai ni kuma na bashin shine Kuma maimakon ya bani tawa shine ya Aiko min da wannan".

Musaddiq Sajida ta kalla 'kai auta maza kaje kace tace ta gode Allah ya Kara nudi"
Sai da ya fita sannna ta juyo gurin Zahra. "Amman wallahi kin bani mamaki Allah ya tarfawa garinki nono ki nemi ki Bata rawarki da tsalle to kici gaba har ki nuna b'araka a gaban 'yan uba, Koda wasa kara ki Kara ba'a yiwa miji haka ko bakaso Abu baka nunawa a gabansa, kika san da Yaya yayi sawo Miki danya faranta Miki Rai Amma Zaki wani kwasale shi kice a mayar Masa kina son tun yanzu ki kashe Masa Gwiwa ko".
💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI💋❤️

JINJINA TA MUSAMMAN GA MALAMAN MAKARANTA ALLAH YAYI JAGORA YA QARA BASIRA DA JURIYAR SAUKEN NAUYIN DA AKA DORA MUKU NA AMANAR YARA QANANA👫👫👫👫👍👍👍✍️
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
This page is deducted to you Families of late Alhaji Isah Musa Bakin kasuwa kazaure jigawa state.
🔷PAGE SEVEN🔷

_______Mika tayi tana salatin ma'aiki s a.w.w sannan ta Zoro kafafunta kasa, tunda ta farka tasan tabbas karfe biyu tayi na sulsulin dare har ya zamar Mata jiki. Dubanta ta kai inda Sajida ke kwance barcinta take sadidan cikin kwanciya hankali, sai taji Ina ma ita ce haka, wasu hawayen ne suka ciko idanunta a hankali tace "Ya Rabbi ga baiwarka Mai rauna ka jibinci lamarina dan Isar Manzon Allah s a.w.w. kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka kada ka Bari makiya su yi min dariya ka bani rinjaye ka dorani akan duk Wanda yake son Hawa kaina".
Ta Mike tsam ta nufi toilet din cikin dakin sai Kuma ta fito saboda shaf ta manta kafin su kwanta taga famfon ya dauke Kuma da alama ba'a kunna layinsu na tanki ba. Cikin rashin tsoro ta bude kofar ta fita zuwa bayan part din Mama don ta kunno ruwan, gurin ta dosa gadan gadan sai Kuma tayi turus, magana take jiyowa daga wurin da sauri ta koma baya dan bata San abinda zata gani ba. Tana tsuma ita fa duk da Bata da tsoro amma tana tsoron ganin abinda yafi karfin idonta ko Kuma wani mugun abun.
Dole tayi hakurin yin sallar a koma ta kwanta tana ta sake-sake har kusan Asuba, ba Kuma taji motsin wani na tada hankali ba.
Saida Sajida ta tashe ta lokacin har an Fara sallah a masallacin gidan nasu.
A gurguje tayo alwala da alama Sajida ce ta shigo da ruwan.
Bayan sunyi sallah zaman Azkar sukayi har lokacin da gari yayi shahhh alamar wayewa, sannan suka koma suka kwanta. Dukkan su ba barci suke ba, Zahra ce ta danyi tsaki kadan ta tashi zaune.
Kallonta Sajida tayi.
"Yaya Bestie akwai damuwa ne?"
Dan juyowa zahrar tayi tana kallon sajidar tana Kara wani tsakin "nifa wallahi na fada Miki tsoron mutumin nan nakeji tun ranar Dana Fara ganinsa a gidan Baba malam nake Jin wata irin shakkarsa. Dan Allah a haka zamu rayu bana ko son kallon idanunsa? Kinsan wani tarin abin haushin jiya fa hannu yasa ya dago fuskata Wai dole saina bude idona na kalle shi ko Kuma ya bani mamaki, Kuma fa ranar Nan a asibiti har wani shafar min fuska yayi Yana fadar nayi hakuri da wannan hadin shima ba so yake ba, kawai yayi biyaya ne tunda baze iya yiwa su Abba musu ba, amma ni Ina iya fada musu bana so".
Baki Sajida ta rufe tana kunshe dariyar ta. Kai ta shiga girgizawa tana fadar Babbar magana ki fadawa su Abba bakyaso! Wato ke ga marar ta ido ko? Shima har yasan kimarsu da baze iya yin musu dasu ba saike ce marar kunya Zaki Fadi Baki so, ki rabu dashi kwaai abinda nake so dake yanzu ki koyi dakewa a gaban nasa sannan ki daina tsoron idanun nasa, Wai tsaya fada min menene a cikin idon nasa da yake firgitaki duk girmanki da wayonki da wayewar ki?"
Wani shagwabe fuska tayi kamar Mai Shirin fasa kuka.
"Bazaki gabe ba, ni kaina bansan ya zanyi ba saboda shi fa na daina zuwa gidan Baba malam tunda lokacin kullum Yana tare da shi kuma sai yayi ta kallona yana tsareni da wadannan idunuwan nasa kamar Mai jin barci".
Yanzu dariya sosai Sajida keyi harda kwalla tana fadar Babbar magana tab kice abin asali ya Samo shi ai kaya ne suka tsinke Masa a gidin kaba kece dai kike bulayi"
"Kamar yaya?"
"A'a bazakiji mutuwar sarki a bakina ba ai tunda an hada anyi Mai walahar...".
Sautin kiran waya ya dakatar da shegantakar da sajidar ke mata.
Wayar da aka kawo Mata jiya ce ta dauki kida, Sajida ce ta Mika hannu ta dauka M.M DANGE ta gani Yana yawo akan screen din.
Zahra ta mikawa tana fadar oga ne da alama a Sha soyayya lfy. Tayi waje tana fadin Bari naje nayiwa Ammah shara.
Bata daga Kiran ba har Saida ya kusa katsewa kana ta daga tasa a kunnenta. Daga can taji Yana fadar "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
A zuciyar ta a amsa Dan da gaske in dai zata ganshi ko taji maganarsa kasa samun nutsuwa take.
Sake maimaita sallamar yayi, da kyar ta amsa masa tare da fadar " Ina kwana?"
Shiru taji ba'a amsa ba kamar ma an sauka daga layin, amma ga mamakinta tana dubawa sai taga Yana nan, itama shirun tayi kudin sunata tafiya saita saka handsfree ta aje wayar kusa da daga gefe tana kallon ikon Allah.
Saida ya mula Dan kansa "yace ya jikin naki I hope kin shan maganinki?"
"Eh" ta fada a takaice.
"Fine"yace shima a takaicen.
Ita mamaki ma yake Bata har wani turanci yake jefawa a magana kamar gaske.
"Sai an jima ta fada tana kokarin katse Kiran.
"Kada ki kuskurs ki kashe min Kira" ya fada in serious tongue.
Shiru tayi tana mamakinsa sai wata izza yake Mata kamar wani abin azo a gani.
Muryarshi ta tsinkaya Yana fadin ki bude data na turo Miki sako idan da abinda kike bukatar ayi ko a Kara sai ki fada min, take care".
Kit ya kashe kiran.
"Kutt!" Ta fada "amman gayen nan yama Raina ni wlh Wai kada na kashe Masa waya"
Kwafa tayi "zakaga na kiraka ganin idon ka" ta Jafar da wayar tana mita.
Taso yin barci Amma ta kasa dole ta hakura, wayar ta Kara daukowa tana kare Mata kallo.
Number din Hameeda ta Fara sakawa tunda taga sabon layi ne ya dauke natan, ga mamakinta sai taga sunan Hameedar ya bayyana ba bata lokaci ta kira.
Tana ta ringing kamar baza'a dauka ba sai Kuma ta daga da sallama ai tana jin muryar Zahra ta Fara mita "yanzu Dan Allah kin kyauta tun jiya nake neman layinki Amma shiru na Kira Mama nace ta Baki tace min bakya Jin Dadi kina barci, wallahi Kinga yanda hankalina ya tashi kuwa ki Bari lokacin da Sajida ta fada min halin da ake ciki wallahi daba final muke ba Allah da barinta zanyi c/o na taho gida har fada mukayi da Salma Wai ai sai inje na baiwa Mushahun hakuri ya dawo ya aure maganganu dai gasu nan ki Bari kawai ai jibi zamu Gama in Sha Allah komai dare a gida zan kwana".
"Allah ya yarda ki Bari kawai wallahi Ina cikin yanayi akwai damuwa Dan Allah kizo ko naji sauki abubuwan".
Ta fada tana share hawaye, sukayi sallma Dan it ma Hameedar kukan take.
Wai ita Mushahu ya yiwa haka, duk wadanda suka fasa aurenta Bata taba Jin Wanda ya Bata Mata Rai ya Kuma tsaya Mata kamar wannan ba ai ko wace irin matsala ce ita ya kamata ya Fara fadawa ba ya yanke mu'amala da ita ba a lokacin da take matukar bukatarsa ya manta shakuwar dake tsakanin su da alkawarirrikan da suka yiwa juna.

Kwantawa tayi tana tunanin baya a haka wani wahalallan barci yayi gaba da ita.



**********Tun Yana tsammanin ganin ta bude data ta duba sakon har ya cire Rai da hakan.
Lambar Abdul Hakeem ya Kira sun jima suna waya kafin suyi sallama.
Laptop dinsa ya janyo yaci gaba da aiyukansa sai kusan azzahar ya Gama. toilet din cikin dakin ya shiga ya dauro alwala,a masallacin hotel din Yaya sallah lokacin daya fito Kiran Habib ya shigo Masa "Wai Dan Allah kana Ina ne tun dazu muke nemanka kazo masu aikin hada furniture's din Nan ne suka Gama da cabinet din kitchen".
"Ok gani Nan inaga kada kayi nisa zuwa an jima su Aunty zasuzo suga gurin"
Ya fada.
Yana nufar gurin da ya saba aje lifan din Habib.
Wayar Ammah Abdul Hakeem ya Kira ya fada Mata Mahmud yace a turo a gano gidan an Gama gyaran, dakin Mama Ammah ta shiga ta fada Mata sannan Kira Aunty Hasana ta fada Mata kafin ta wuce gurin Alhajin ta fada Masa tunda shiya dawo daga gidan gonar sai su Abdul Hakeem ya baro suna yiwa shanu Allura da Basu magunguna.
Wurin karfe biyar Aunty Hasana ta debesu a mota harda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login