Showing 39001 words to 42000 words out of 108220 words
Chapter 14 - Tantiriya A Gidan Yari Book 3 Complete Hausa Novel
tana tuka tuwon danyar shinkafa,shugowa Haneef ya sake yi ya bude fridge ya dauki lemon gongoni,ya sake cewa kawo na gwada tukawa ya ajiye lemon a gefe,ta bashi tana murmushi Yana farawa yaji tafiya kamar mutum na tahowa sakin muciyar yayi ya dauki lemonsa ya juya baya a zuwan budewa yake,Ihsan ce ta sake biyo sawu ta ga me yake yi wai.Khadija bata kulata ba haka ta gama girkin ta kaiwa Mama,taci itama sai yabawa take yi sosai.
Mero ta dawo ta gyara wajen bayan ta gama ci tace Mama kina bukatar tausa? Mama tace a'a Yar nan na gode kawai dai ga magani na shafa min a Kafafuna,Haneef Yana zaune Khadija tace Oga ga aikin Lada kazo ka samu Ina Maka fatan samun wannan ladan, tashi yayi ya karbi maganin,Mama sai murmushi take yi tace kaji yarinyar kirki me Ankarar da bawa hanyar samun lada,murmushi Khadija tayi,Wallahi kin birge ni Kuma duk Wanda ya aure ki yayi dace Khadija,Haneef da sauri ya tambaya yace Allah Mama? tace duk Wanda ya aure ta ya samu macen kirki,Ihsan tana gefe baki ta tabe ta dauke kai,Mero tace Mama na gode za a miki wani abu ne? tace a'a an gode jeki uzurinki yarinyar kirki,Mero ta shige dakinta ta dinga sheka dariya tana tsalle a Saman bed tana cewa na ninke Mama bata Yar iska bace ni,babu wani ta gari,wai nice nutsatsiya dama ba Tinkiya aka yanka min ranar suna na ba.
Washe gari Arham kin fitowa yayi Sam kar Basma ta ganshi ta fada tace ya taba ta,Basma kuwa tunda ta tashi take zuba Ido ko zata ganshi ita hirar jiya tayi mata dadi kwana tayi tana tunawa,Mima ta tambaya a Palo tace Mima tana Sosa Kai,Mima tace ya aka yi? tace dama jiya ya manta abinsa zan bashi Kuma ban ganshi ba,Mima tace bai fita ba ai Yana nan zai fito ne,naje na Kai Masa? Mima tace a'a ki bari ya fito,tace to ta zauna,Maman Rafeeq tana zaune tace karki sake naga kafarki a part dinsu ba a zuwa wajen namiji ki dinga taka tsantsan,Papa ne ya shugo da alama fita zaiyi ya samu Maman Rafeeq suna yiwa Basma fada karta je part din Maza,Mima tace ki bari ya neme ki da kansa,yaran zamani sai addua kuwa,Basma tace ai kuwa sai dai kar a Kuma jiya zip ya bude min yace kwaro ne a ciki wlh ya taba min kirji na,Amma karki fada Masa yace kar na fada,Ran Papa ya baci yace yanzu auren da za ayi Masa bazai iya hakuri ba,Basma tace ba haka bane ba fa yace kar na fada Dan Allah kuyi hakuri na yafe Masa nidai,Papa ya fusata,Mima tace Dan Allah kayi hakuri,yace ba ruwanki a gabanki yarjejeniya muka yi da shi da sharadi idan ya sake sai ya bar gidan Nan yace ya yarda,Kuma yanzu ya Maida ni dan iska,Mima tace to yanzu in kace ya bar gidan Nan Ina zai je? Kuma wa zaka yiwa auren? Papa yace na fasa bashi ita sai ta auri Shaheed shi ya bar min gida.
Mima ranta ya baci tace yanzu...dakatar da ita yayi yace shi yasa suka gagari kowa,ke baza a yiwa yaranki fada ba baza a hora su ba,ya isa in zauna inyi yarjejeniya da shi sannan ya sake gwadawa shi din banza,Ina Arham ya tambayi Haly da shigowarta kenan,Yana part din su,yace kira min shi maza,ai Arham Yana ji ance papa na kiransa yasan ba lafiya,Haly tace da alama Basma ta fada Masa,Salati Arham ya saki Wanda ke shiryawa wanka yayi dama,yace guard room zai sa a sani ko ya kaini Barack a gana min azaba,Haly tace wlh kayi ta kanka Kai kasan ba iya korarka zaiyi ba kasan kalar korar Barack za a kaika kayi sauri na bude ma kofa ta baya,Arham ya kwashi takalma a hannu Suka fice a hankali ta bude Masa kofar kitchen ta baya yabi ya fita,ta waccen gate din na baya ya bi ya bar gidan Yana fita Papa Yana kiran securities sojoji yana bada sanarwa a rufe gida kar a bari Arham ya fita.
Suka kulle ko Ina suka hau zaga gida da bindigu,sama ko kasa an rasa Arham,Haly tace na duba ko Ina baya nan,karya kike papa yayi kanta da jibga,Basma ta mike ta gudu tana cewa nidai bakuwar ce kar a hada dani ta arce daki,Haly da kyar ta Sha a hannun Papa ta kulle kofa tana kuka,Mufee tace Allurar Papa ta motsa ta sojoji,Arham kuwa Spark ya kira ya fada Masa,Spark yace me kayi to? Yace Basma fa kawai na rungume,karya kake Arham wlh idan baka Fadi gaskiya ba bazan rufa Maka asiri ba duk Inda kake sai an Nemo ka,Arham yace to abin na taba,Kuma wlh ni kawai ji nayi akwai ko babu ba da iskanci nayi ba,shine ta fada,Spark yace tab yanzu karka je gidan abokai Dan za a bika kana Ina? yace gani a taxi? zo Office dina kayi sauri,Arham yace na tabowa kaina masifa nonon Basma ko Masifa,Yana zuwa" Office din Rafeeq Spark yakaishi ya sa key ta baya ya kulle su har Rafeeq a ciki,Rafeeq yace ni a bude ni na tafi gida, ni ba da iskanci ba a kulle da ni,Spark bai ko kula shi ba.
Rafeeq ya Kalli Arham yace kwarto,Ka taba me tsada yau dubunka ta cika,Arham yayi dariya yace bana dana sani Kuma ban Jin na gama tabawa, samun lafiya a daura auren nan,an lasa min zuma,yace wai Shaheed zai bawa ita,wlh bani ba Shaheed matukar ya karbi auren nan mun raba gari,Dariya Rafeeq yayi yace daga taba abu,yace ba haka bane,ai cin fuska ne wannan a bani mace ace za a canja ai ba daidai bane,ni har naji ma Ina Jin haushin Shaheed din.
Rafeeq ya Kalli Arham yace baka Jin magana Arham,muga hannun ya canja tunda an Sha Laushi,Arham dariya yayi yace Kai da ka kwana a gidan surukai wa yasan me kayi, a gidanmu kowa Yana da abin fada ba Wanda zaiwa wani gori tun daga kakanni manya har yaran,Rafeeq yace Allah? Kaka Zeenatu ma karuwanci tayi,ai ance shahararriyar Karuwa ce da,harda kasa kasa da Murya yace Shima Maleek din ai a can suka hadu a Bariki suka yi aure,Rafeeq ma yayi kasa da Murya yace Allah Kai? Allah da dadironta ne ya aure ta daga baya,ta nace masa ai ance Zeenatu tayi Zuma ta more,duk Wanda ya dandana sai ya koma ta tara abin duniya da Bariki,Misam ne dai da ya shiga shi haka ya fito ba uwar komai sai nasa da ya kashe,Ashar Rafeeq ya dura Masa yace Dan iska munafuki duk a Ina kaji labarin nan Kai? Suna dariya Arham yace zancen duniya Yana buya ne,Mamanka ma uwar goyonka ai ance tayi Uhum Uhum kadan,Wlh zan tona ma asiri Papa yazo ya tafi da kai.
Papa kuwa yasa aka dinga neman Arham basu San Yana Office ba har gidan abokansa kaf sojoji sunje ba a ganshi ba,aka je gidan su Spark duk an bincika baya nan,Mima ranar fushi tayi da Papa ko kulashi bata yi ba.
Sai dare Spark yazo ya bude su,Rafeeq ya fice yayi tafiyarsa gida,Arham suka tafi da Spark gidansa.
Naila tana Palo tana dariya ganin an taho da Arham,Naila tace to Ina kayan sawar? Na mijinki zan saka,kaga dai ka jawowa kanka kana zamanka lafiya,Arham ya ce ya zanyi nazo a dan gidan Soja,yanzu in ba Soja ba wa zaiyi haka,to ya Basma din? Na San mata shegen baki kamar na tsuntsu,Allah ya kaimu ayi bikin sai na saita mata bakinta wlh,sai na ladaftar da ita Yar iskar yarinya,Naila tana ta dariya tace ga abinci can,yace ni zan iya cin wani abinci ne hmm ya mike ya shige bedroom.
Wanka Spark ya fito Yana danna waya Naila ta shugo yace wai dollar ta sake tashi,Naila ta sheke da dariya tace ai dollar a kasar Nan Bata San Inda zata tsaya ba,anjima ta tashi anjima ta sauka,Naira Kuma tayi haka Naila ta lankwashe kafarta tana dingishi tace Baby kaga Yar Gurguwa to haka Naira ta koma,Dariya Spark yayi yace ta karye baras,kamar a kasar Nan aka kirkiri dollar,ya kamata dollar ta koma kasarta ta gado.
In kina so Kiga murna sai kin hadu da mutane baka San halin da ake ciki ba?,kice me dollar ta karye ana washe baki ana baki labari,anjima kadan dollar done High,Kuma ko wanne farashin kaya ya karu,Yan kasuwa sun rasa hankalinsu basu San me suke ba,yanzu ka mika kudi bani kaza ance Dari uku kana komawa anjima za ace dollar ta tashi dari biyar,har yaushe ya siyar da kayan suka kare ya dakko wasu,Naila tace ni da nake so in na haihu a yanka min sa da raguna to dollar tana ta hauka ya kenan? Spark ya kalleta yace wannan yaron na cikinki wai shi zan yankawa sa? Tunda aka same shi yake bani wahala ai Yana zuwa zai ga tsiyar Uba,dariya Naila tayi tace amma fa nayi kokari har yanzu ban fadawa kowa Ina da ciki ba,Spark yace karki fada rabu da kowa in ya fito sa gani kar ayi Masa baki kambun baka ya kama shi a haifo shi Dolo,tunawa yayi da Sunan surukinsa ne,Naila tace cin mutunci,yace sorry ba haka nake nufi ba,zata fara fushin yace Dan Allah yi hakuri,yi hakuri yi hakuri,yanzu sai Naila ta fara fushi ba gaira ba dalili.
Bayan wasu kwanaki Beauty an hada mata gidanta chas,an gama furniture ta zuba musu na gani na fada,gashi ta shiga watan hauhuwarta ma,suna Palo Mohsin ya rike Beauty tana motsa jiki irin na masu ciki yanda aka koyar da su a asibiti,Beauty ta rike kugu suna dariya tace wlh na gaji,riketa yayi tare da zaunar da ita tana yatsina tace Marata ciwo take,to ko haihuwar ce? Murmushi tayi tace Edd ma sai Nan da 25days zai cika,da saur.....mararta ta rike tare da dauke wuta duf Bata sake magana ba sai da aka dauki minti daya taji ciwon ya saki,Mohsin Yana kallonta yace ya dai? Ko a kira Umma mu tafi asibiti? Ai na daina ji ma na warke,okay haka nake so.
Kafin ta rufe Ido ciwon ya dawo da karfinsa tace Kai muje asibiti gaskiya ciwon nan ba na sauki bane ban taba Jin irinsa ba,sakkowa tayi kasa ta rike mara,tashi yayi yace tsaya na duba ki idan haihuwa ce sai mu tafi asibiti,da kansa ya duba ta yace to nidai haihuwa na gani,wayar Umma ya kira ta daga,yace asibiti zamuje ki shirya zan biyo na tafi dake Beauty ce Bata da lafiya kamar dai haihuwa ce,Umma tace to,Bata fadawa Hashimu ba kar yace zai je,tana shiryawa ta barwa Zarah karamar Yar ita muka fito,a shago ta samu Abba tace zanje unguwa,ko tambayar Ina baiyi ba yace a dawo lafiya Allah ya tsare ki siyo min tsaraba,murmushi tayi ta wuce.
A gefen titi Mohsin ya dauketa suka nufi asibiti,Beauty tana salati a hankali tana cewa Allah ka zama gata na,Allah ka dafa mini,Allah ka sa min hannu a lamari na,Allah ka dafa min....a haka suka Isa asibiti,Mohsin hankali a tashe ya manta ma Umma tana wajen,zai fito da ita a mota sai rungumeta yake Yana cewa I'm sorry ni na jawo ko? Umma ta tace Dan ubanka ka matsa ka bani waje,Beauty tace jeka kayi min addua kaji,bazan iya tafiya na barki ba,Umma tace Mohsin zan bar Maka matarka na tafi wanne irin iskanci ne wannan,Karki yi fushi Umma gwara dai Ina ganinsa cewar Beauty.
Gado aka bata,sun dade tun yamma suke asibiti tana Shan wahala,Beauty sai da haihuwa tazo ma'aikata suna wajen suna cewa yi Nishi...push....Beauty Bata ganewa sosai a wannan halin amma Taga yara ne Yan mata mace daya ce babba,tace a karance kuka gani Shegu Yan iska shi yasa kuke cewa nayi Nishi Ina naga karfin Nishi yanzu ni,baku San aure ba bare haihuwa kuce na dinga nishi,kawai Kunga Abu a rubuce kuzo ku dameni Nishin uwarku....tana Jin ciwo tana bala'i tace ban San me yasa Mohsin ya jawo wannan asibitin na Yan koyo ba,duk Yan koyo ne a ciki basu iya komai ba gashi Nan da wani asibitin ne da tuni na haihu,dama tunda aka sa Masa suna Aminu Kano teaching hospital,teaching ne fa na Yan koyo ake nufi ai bazan haihu da wuri ba,duk yara sun dameni ni,wayyoooo.....Ma'aikaciyar dattijuwa tace haihuwa tazo amma Kinga Yar iskar yarinya tana matse kafafu za fa ki kashe danki,Umma tace daina zaginta wahala ce ku har abada a kasar Nan bakwa girmama mutane,sai ku dauki mutum kamar wani Dabba,da iliminta wlh ta fiki Ilimi ma,kice ta gyara sai ki zage ta,Allah wadai da halinku wasu ma'aikatan lafiya marasa Imani mutum Yana wani hali Kuna zaginsa da hantara,sai lokacin likitar tayi shuru taji Umma ta fita masifa.
Umma ce ta taimaka itama a nutse har aka samu Beauty ta haifo Danta namiji katon gaske, duk abinda ya dace anyi mata ita da jaririnta suka canja mata dakin hutu,Mohsin ana masallaci Yana ta addua Bai San ta haihu ba,har sai da Umma taga wajen 11pm sannan ta kira shi a waya tace ta dade da haihuwa fa Ina ka shiga, Alhmdllh ya furta yace tana lafiya? lafiyarta kalau gashi har Hidaya sunzo ma abinci take ci,fitowa yayi da sauri ya je dakin,a zaune ya samu Beauty tana cin faten doya Wanda Hidaya ta kawo,tare da Iman suka zo, Annoor ne ya kawo su, Mohsin sai murna ake taya shi baki yaki rufuwa an yiwa Amal kani,addua yayiwa Jaririn sannan yace an fadawa Naila? Umma tace Naila ka iya tunawa kawai? Murmushi yayi yace itace besty na,ban fada mata ba kuwa,Kiran Naila yayi yace kinyi da Your love ya haihu,murna ta fara tace me muka samu? yace me Hallare,dariya tayi tace Allah yasa ba Yar mitsil bace,ni ya gado ai,Kai Yaya ko kunya,Mohsin yace ke kika koya min ai, wa ya kaiki iskanci, kasa hakuri tayi tace zan fada Maka wani sirri karka fada tukun ciki ne dani ya kusa wata uku,Mohsin dariya yayi Jin Naila har rada rada ake fada,congrats kunyi kokari,Naila tace na gaske ma idan ban samu ciki ba kamata yayi a kama Spark ayi yamma da shu'umi kawai,dariya Mohsin yake sosai yace baza ki nutsu ba Naila,Naila tace to magana ta Allah baya hutawa da Kwalbewa Yaya ai idan ban samu ciki ba kawai ayi can da shi Inda ake cin mushe,Naila tana gama wayar ta juyo taga Sparka a bayanta wayar ta Maida kunnenta tace ai Dan Albarka ne ayi gabas da shi,Allah dai ya Masa Albarka Ina sonsa wlh,mijina ai duk duniya bani da kamarsa.
Dariya Spark yayi yace ba laifinki bane Dana nane yake min zai zo duniya ne Allah ya kaimu,zanga me biya Masa school fees,Arham ne ya fito har yau yana gidan Spark Papa yaki hakura an kwashe kwanaki.
Naila tace gobe su Basma zasu zo gidan Nan inji Mima,Arham yace Allah ya kawo su ni Ina ruwana da ita,Spark yace tana sonka fa wlh yarinya Mima tace tunda aka Kore ka ta kasa sukuni kullum sai taje Wajen Papa tana cewa ta yafe Maka a dawo da Kai,rannan ma kayanta ta hada tace zata tafi tunda dai ance Shaheed za a bata,Arham yace ita taga duhu wa yace ta tona min asiri,duk abinda za ayi da Yar kauye sai ta nuna hali yanzu da Yar birni ce waye ma zaiji kullum sai na taba kuji shuru Kuma kamar na biya sadaki amma dake ita ba a abin arziki da ita sai kuka wayyo ya taba min Dan iska sai na fada
Naila tace a Yan kauyen ma taka ce haka Arham mu ba muka yi ba,Spark ne ya dingure mata Kai yace ka fadi Alkhairi ko kayi shuru,wannan cikin harda tone tone yazo,Arham yace au har anyi sabon? Naila tace tsokanata yake,Arham yace ni Ina ruwana ko cikin ne ma,Spark yace ciki ne da ita Arham almost 3mnths duk fushin nan da take yi da fada ai duk cikin laulayi take,Arham yace Allah ya raba lafiya,Spark yace Ameen wlh na matsu ta haihu na gaji da wannan mood din da take shiga,yanzu aka fara fa cewar Arham,kafin ta haihu nasan sai na dawo tsinke sabo da rama cewar Spark,dariya suka yi,Naila tace ya batun business din naku Arham? Shaheed ne yake ta aikin business din ai muna waya.
Mima dai tace in Arham yayi tafiya baza ta damu ba ko kiranshi baza tayi ba amma kullum itace take fara kiransa,a rana sai ta kira shi yafi sau uku,yanzu ma kiransa tayi ya daga yace kika ce idan nayi tafiya ko nema na baza kiyi ba amma gashi yanzu kullum ke kike fara kirana,Mima tace ai ba wani missing Dinka nayi ba kawai dai Dan na tabbar da kana gidan Spark dinne kar ka tafi wani wajen,dariya yayi yace to na gode Ina Nan ai,ya fara hakura ai Basma tace zata bar gidan ta tafi baza ta hada Da da Uba fada ba,shine ya sakko yace ka dawo gida gobe,Arham yace ni nafi Jin dadin nan ma sai abinda naga dama a nan,to dai in ba so kake ka sake bata komai ba ka dawo gobe yace,Sai dai mu taho da Spark,to koma dai mene ta kashe wayar.
Washe gari da wuri su Basma suka zo,Arham Yana bedroom abinsa Yana kwance Yana danna waya,Yana Jin surutun su,Basma taji ance yana nan amma bata ganshi ba,gajiya tayi tace Aunty Ina Arham din? Naila tace Yana bedroom waccen room din,Basma ta mike taje ta kwankwasa yace come in,ta tura kofar ta shiga,Ido ta zaro tace bleaching kayi? Naga ka sake haske,wlh saurin girma ne da Kai kwana nawa da barin gida amma har ka Kara girma,Arham yace me zaki ce dani kin Sa an Kore ni daga gidanmu,a gefen bed din ta zauna tace ban zaci haka ba