Showing 42001 words to 45000 words out of 108220 words
Chapter 15 - Tantiriya A Gidan Yari Book 3 Complete Hausa Novel
ganin Kuna abinda kuka ga dama na zaci baza a Maka komai ba shi yasa,amma ai gaskiya tana da zaki Kuma tana da daci ko baka yi ba? Baza ma ki bani hakuri ba? Da kayan sata ka kamani da zan baka hakuri,nifa mijin Naila shine dai dai ni dai dai shekaru na ba Kai ba Dan ma ka samu Ina kula ka,alfarma nake Maka fa,Arham yace na gode zaki San kina min alfarma, dariya tayi tace hmm ta mike tace na tafi,tashi yayi ya mike ta ganshi da tsayi tace kana zuba saurin girma a duniya,kullum sai ka Kara tsayi,ki bari sai an daura aure ki fada min haka.
Fitowa suka yi Yace kar a zargeni tunda ni yanzu na zama abin zargi a wajen mutane akan nono,abinda ma kowacce tashi tayi taga ya fito ba roka tayi ba Taga an bata shike nan sai a damu mutum sabo da anga mu bamu da shi sai mata su dinga wulakanta mu.
Sai dare su Basma suka tafi tare da Spark da Arham,Arham sai buya yake a bayan Spark Yana cewa Papa ko bai hakura ba wa ya sani wlh Allurarsa ta motsa,part din Papa suka shiga matan suka wuce bangarensu,Papa Yana Palo shi da Mima suka shugo,Arham yace Ina yini barka da dare,Papa yace zo nan Arham,Arham ya ja da baya yaki zuwa,Kazo nace rigar Spark ya rike,Spark yace baza ka sake ni ba,Dan Allah Papa kayi hakuri wlh bazan sake tabawa kowa ba nayi alkawari,dama wannan ma sharrin shedan ne ji nayi an ja hannuna ban San dalili ba,bana cikin hankalina nidai kawai sai Jin Abu nayi a hannuna ban San komai ba,please Papa dama ni shedan ya dade da yi min fitsari a ka,amma yanzu zan dage da Azkhar na Kore shi,Papa mikewa yayi yace zaka ga shedan ya Maka fitsari a ka,Arham ya rike Spark zai gudu,Papa yace ai ba abinda zan Maka ni,da zan Maka da tuni nayi tunda nasan gidan da kake kyaleta kawai nayi,ruwa ya dauka ya zauna,Spark ya fisge rigarsa ya zauna,Yana cewa Papa kayi hakuri mana haka ya tuba bazai sake ba cewar Spark,Arham yace wallahi tallahi in sake tabawa sai na halak,baza kayi shuru ba kenan? Mima ta furta,shuru yayi ya zauna a gaban Papa Yana bashi hakuri,Papa yace ai na daina yi Maka fada Arham na gaji,Arham yace a'a Wanda ya rasa mafadi ya shiga uku ai sai na tabe,Kaci gaba da yi min na daina wlh,dama rashin hakuri nane amma Shekara biyu Ina Shan na uwata,Yaya Rafeeq ne ya zugani yace kar na bari kaina ya kulle Shima haka yayi,Misam ma Yana wajen lokacin yace Shi da yayi Bariki ma ya tuba ba abinda ya faru da shi bare ni,shine na kama zancen su suka kaini suka baro ni,to sarkin karya cewar Mima,tace haka fa ya fadawa Basma yarinyar da zata zama surukata yace wai ni na zuga shi ya aikata mata haka,Papa yaso yayi dariya ya boye yace ai Allah ya Kara tunda bakya son laifin su,Arham gobe yaushe? Yace Friday ka shirya gobe daurin aurenka,idan aka daura daga baya ayi bikin sai a Kai Maka Amaryar,Arham yace a bari Papa in aka gama shiryawa sai ayi bikin a Kai Amarya lokacin kaga maybe na fara sonta,baka sonta ka taba ta,Spark yace gaskiya a bari sai an gama shiri wannan sai a kaita tana laulayi,Arham yace a'a da kunyata ni ba ruwana da ita ni,Papa yace na gama shiri wlh gobe ana Sallah za a daura yanda nace haka za ayi tunda shi baya Jin magana.
A daren Umma ta fadawa Abba cewar Beauty ta haihu,Abba yace amma kin ci amanata da baki fada min tun wuri ba, Kubra wlh watarana in kika yi min wani abin sai naji kamar na ambato kakanki Sarkin gandu Tanimu na zage shi,Yar Inna tace ai ka riga ka zage shi Kuma tunda ka Fadi Sunan,yace da Kuluwa me Kwan zabi,dariya Kubra tayi tace sai kazo ta kashe wayarta,duk kakannin Yar Inna ya ambata, minti kadan Abba yazo asibitin.
Ya kalli Mohsin yace ya suruka ta lafiyar ta kuwa? Mohsin yace tana ciki zaka iya shiga,Abba yace o'o'o Yar Inna ce kadai zata shiga wannan dakin na gumurzu na iya shiga kowa ya ji da tasa tunda dai lafiya take shike nan in ta fito na ganta,ya kira Jauro yace kayi jika na biyu Jauro,Jauro yace Matar Dan namu ta haihu ne? ta haifi Da namiji,yace Allah ya raya tunda lafiya take ai anyi arziki,gobe zamu zo Inshaallah. Washe gari aka sallami Beauty fes da ita da Baby,direct gidan Umma aka kaita in tayi sati biyu sai ta koma gidanta.
Abba yace wai nan aka kawota? wato mu a bata mana gida su Kuma su koma nasu gidan fes wannan ai wayo ne,kunci darajar babban bako me sunana,tun lokacin Abba ya bawa jariri suna Hasheem,ya kankane yace sunansa za a saka Masa,Mohsin yace dama ai sunan zan saka da mace ce Naila zan sa my love,Abba yace ai dama nasan sai ka mayar da sunanta itama haka Allah ya muku Albarka ya sake hada kanmu gaba daya,Mohsin yayi dariya yace harda Kai? Ku iyaye ai dole Kuna son mu ba matsalar komai mu yara mu za ace Allah ya hada kanmu,Abba yace harda ni mana idan na fandare fa na daina yi muku addua ai kaga gwara ace harda ni kanmu ya hadu,Mohsin yace to shike nan Ameen Yana dariya,Abba yace Azo a shiryawa Me jego farfesu suruka zata ci kudina a banza Nan da sati biyu tattalin arzikina Kuma ya kare ai,to kullum Yan barka zasu cika gida ayi ta girki ana saukewa ana dorawa,Allah ya taimake ku Abba ba irin na da bane Yan barka da Kun yini da yunwa a gidan Nan sai dai Kubra ta ci da ku ko Wanda aka haifar wa.
Spark a waya ya kira Mohsin da Beauty ya kira su Umma ya musu barka,Abba ya kira Shima ya Masa barka.
Kudin auren Rahma da Nabeela aka kawo sun fitar da mazajen Aure,Rahma Wanda suke rage zafi da shi suna Tabesting shine yaga gwara ya aure ta kawai bazai iya rabuwa da ita ba Sam,Shima Likita ne matashi bai fi mate din Annoor ba,Nabeela kuwa wani Wanda suke School tare ne da kadan ya girme ta sa'anta ne tare suka yi secondary har university,iyayensa suna da hali sosai shi yasa suka amince da yace zaiyi aure.
Jauro sai murna yake zai rabu da wasu yaran nasa lafiya shi dai.
Kwanan Beauty uku da haihuwa Nabeel ya sake kawo Hidaya da kansa,Abba Yana kofar gida shi da Jauro duk me zuwa barka a idon su take wucewa ta fito,Jauro yace gaskiya Dana ya iya kiwo har tana ta zama gwazarma,Abba yace uhm gata nan dai wlh tsila tana ta kauri,Hidaya tace Abba sannunku ta durkusa ta gaishe su,Abba yace wato Hidaya kasa zaki watsa min a Ido,kin nuna a gidana kafin ayi miki aure wahala kike Sha wato baki da kwanciyar hankali,gidan miji yafi gidan Uba,Anya in na mutu kuwa zaki yi kuka? sai da kika je gidan miji kika nuna kinfi Jin dadi acan,Ina rabaki da gorin da namiji yace a gidansa kika yi kiba,Jauro yace ai mu kowa ya shugo gidanmu sai ya canja.
Nabeel ne ya karaso suka gaisa basu ce Masa komai ba anyi sa'a yau.
Mohsin shopping mall ya shiga Yana yiwa me jego wasu siyayya da tace tana so,Hanan ce ta tsaya a kusa da shi da Mijinta Jibson suna siyayya,Jibson Yana cewa karki dauki abinda yafi karfina fa,a'a mayar da wannan wallahi ko kin dauka bazan biya ba,Hanan tayi murmushi tace to da uwar kudi na ni zan biya,Jibson Yana rike da hannunta,Mohsin ko kallon su baiyi ba Kuma yaji Muryar ya gane Hanan ce,Sai da zai bar wajen Yana Juyowa suka hada Ido da Mohsin,Hanan wai tunaninta zata cusawa Mohsin takaici ganin tayi kiba da kyau harda sake makalewa a Jikin Jibson ta furta my love muje,Mohsin tuni ma yayi gaba abinsa ko a gefen takalminsa.
Yace a ransa dan kin auri me kwal kwal har wani birga zaki min ni da nake da me kayan arziki,aikin banza kin dameni a raina zan barki ki auri wani,ya biya kudi ya wuce da ledojinsa,Yana fita suma sun fito ya tsaya a Jikin tsaleliyar motarsa,Hanan ta saci kallonsa takaici ya kamata tace da tuni ni zan shiga motar Nan na cuci kaina,wai mene a kishiya da na zauna na dinga kishin hauka,gashi yanzu ni a Napep zamu koma gida mijina ko Lifan baida shi,kishin hauka baiyi ba na cuci kaina,anzo min da arziki na kasa hakura,matar tasa taso mu zauna lafiya amma naki" gashi yanzu ban samu ko Wanda ya kama kafarsa ba,Mohsin motarsa ya bude zai shiga ya juyo suka hada Ido da Hanan tana tafiya da Jibson zasu shiga napep Amma Mohsin take kallo,gwalo ya mata ya saki murmushi ya sake mata gwalo karo na biyu,da sauri ta dauke kanta kamar zata yi kuka,Mota ya shige ya ja sai ya Kara gaba sai dariya yake Yana driving yace kinyi asara Hanan yarinya yaro me kama da Nailan sa kyakyawa gashi yanzu gidana wow ga mota Alhmdllh,dama ni ba ajinki bane kuruciya ce ta sa na nace Ina sonki,sai da Abba yace ban iya zabe ba amma lokacin Ina yaro ban San ciwon kaina ba yanzu kuwa sai Beauty,wacce in ka kirata kace Beauty mutane zasu juya harrr kallon wace Beauty ana kallonta za a tabbatar da taci sunanta,ke kuwa da kika dace ma da suna Larai aka taimaka aka saka miki Hanan.
Kidansa ya karo Yana bin wakar da yake ji har da rawa da kai yace Hanan kin mutu kin lalace an kare a me kwalkwal ko banza sanda kina matata ai kina shafa gashina,yanzu kuwa me zaki shafa kina kamowa zaki ji kamar kin shafa bayan kwarya,Mohsin sai dadi yake ji Hanan bata ci gaba ba, Yana Allah ya Kara, wannan dabiar Maza ce dama.
Annoor Iman dinsa ya daga sama ya cafe ta tare da dorata Saman bayan motarsa ya tsaya a Jikin Kafafunta hannunsa daya a gefenta dayan ma haka suna karewa juna kallo suna Hira a cikin gidansu,ya dawo daga unguwa ta fito tarensa shine ya Dorata Saman bayan motar.
Iman tana magana tana shagwaba kamar wata Yar yaye,tace Mamana tazo dazu wai kaji auren Sudan zata yi sun gama magana,yace mene na damuwa to yanzu ki gwada a kanki kice a ni da ke Hakan ta faru Dan na dawo baza ki aure ni ba? Iman tace da gudu ma ba wanda ya isa ya hanani wlh sai na aureka ba yara ba ko sabon gari market na Haifa dole na aureka,ai sai dai a sani a taskar labarai amma aurenka ya zama lahu,in aure abina in bar yaran suyi ta fushinsu,yace to ki kyaleta tayi aurenta duk abinda zai faru ya riga da ya faru,Haidar ya zama Yaya a gaske Kai jama'a Haidar surukina Dan iska ko gaishe shi bazan dinga yi ba,Iman tayi dariya tace Yayan guda,Juyawa yayi ta haye Bayansa suka wuce ciki abinsu.
Kwanan Babar Haneef biyu ta tafi,tana tafiya a ranar Mero ta Sha wanka ta shirya cikin Abaya me kyau ta fito,Ihsan tana Palo Shima Haneef Yana Palo tazo ta wuce ta tsakiyar palon ta wuce kitchen,gaba daya hankalin Haneef ya koma kanta,Ihsan ta kalle shi tana mamaki,Mero tana sani ta wuce kitchen ta fito da ruwa Wanda ba Sha zata yi ba,ta fito again Haneef ya kura mata Ido Yana so ya fuske amma ya kasa,zata wuce yace Dan taimaka min da juice,Mero ta ajiye ruwan a gefe ta kalle shi suka hada Ido kasa tayi da kanta ta dago da iya idonta murmushi suka yi a tare,har ta tafi ta juyo tace juice kace ko? yace yes,wanne kalar tana kashe Masa Ido,Haneef yace dole na Kara aure ba waliyyi bane ni wlh,a fili yace Apple,tace haba me za ayi da wani Apple gaskiya ni na Strawberry zaka Sha yafi dadi,kasa musawa yayi sai me cewa yayi Allah? yafi dadi ko? Mero tace sosai ma,kamar nafi son Apple din ni,shagwaba ta fara Allah a'a ni gaskiya strawberry pleassssssssse kaji....tsigar jikinsa ce tace wani yarrrrrrrrr.....yace okay it's fine kawo min to shike nan? Kai ta daga a shagwabe,Ihsan mikewa tayi tsaye tace wai meke faruwa ne a gidan Nan? Mero tace da aka yi me fa? Yar aiki ce ni nazo miki da shawara kika ki ji,ai mu indai muka Bada shawara aka ki dauka to mutum sai yaga tsiya wlh,bama son mutum ma da ya yake karewa damu bare yayi mana,abinda kika kasa nake miki a aikace Kuma Baki ga komai ba,duk kudinki da kike ji da shi da iliminki ni ba ruwana da shi aiki zan miki wlh.
Baiwar da Allah yayi mana ita ake fitowa da ita ana sarrafata tunda ke kin kasa kin wulakanta taki ta zama Bata da amfani,Ohhh kice dama son shi kike yi? ya halatta mana in ma Hakan ne ai ba haramun bane,wlh baza ki iya kishi Dani ba na tabbatar ko a kishiyarki nazo wlh sai kin sallami kanki,muke sa mutum yayi laifin dole fa,ki bar Raina mutun ko ya kika ganshi,ya kike so ayi miki? An fada miki gaskiya kinki ji,an miki fada an miki ta lallashi kinki to zama zaiyi yana jiranki ko me? bazai Mori kuruciyarsa ba jiranki zaiyi,so kike sai furfura ta fara feso Masa tukun,Yana da bukatar yara Yan dagwai dagwai,Haneef yace madalla da samun Yar aiki irinki wlh,ke Alkhairi ce,kina da hankali da hangen nesa.
Ihsan tace haka ka ce? Dama Amana ta kuke ci ka kawo min Karuwa a matsayin Yar aiki wlh Iyayenka sai sun San wannan zancen,Mero ta juya ta dakko lemo ta kawo Masa,ya karba Ihsan ta ja tsaki ta juya tace fasikai wlh sai ka sakeni bazan zauna da mazinaci ba,Mero tace ai kinji Illar baki San ma waye mijin ki ba zai iya Zina ko bazai iya ba baki sani ba har kin fara zargi.
Haneef tv ya canja channel yace sun fara film din nan,Mero tace ai Bata mutu ba? Bata mutu ba yarinyar to tunda bata mutu ba zanci gaba da kallo,Mero ta zauna suna Kallo abinsu,Ihsan ta shige daki tana kuka tana faman kiraye Kirayen kawayenta tana fada musu halin da take ciki.
Haneef yace Khadija Aure fa zanyi na dauki shawararki, gaban Khadija ya Fadi dam,tace wace zaka Aura din? yace akwai wata Yar kawar Mamana ta Dade tana son na nine naki yarda Kuma har yanzu tana nema na a waya,Mero tace ba irinsu zaka nema ba ai sai ka Kuma auro irin Ihsan,yanzu karka nemi kowa addua zamu tashi a tsaye mu fara Allah ya kawo Maka ta gari to daga nan Kuma ko kawarka ce kaji baka so ku rabu sai ka aure ta,Haneef yace Kawa? Ni bani da Kawa sai ke kadai fa,Mero tace ko nice ba addua za ayi ba kan wacce ta fada ayi da ita,Nima ko ba na so zan taimakeka,harka ce ta taimako kana cikin wani hali,Haneef yayi dariya a ransa tunanin Mero zata iya Masa wayo,kawai kallonta yake,ta kwanta Masa a rai ne kawai,yace to shike nan Allah ya tabbatar da Alkhairi,tace Amin ni Yar taimako ce abokina nane Kai zan iya taimaka Maka a ko wanne irin lokaci,yace da gaske tace to in Kuma wata ce Allah dai ya baka ta gari ni bana bakin ciki,dama Ina da saurayina a kauye,Haneef yace wanne irin kauye ana zaune lafiya kina da aboki kamar ni.
Ihsan ce ta fito a fusace ta haura sama ta shige bedroom din Haneef tayi Shirin bacci ta kwanta a Saman bed dinsa,Mero tunda taga ta hau sama tasan da dalili,dariya ta dinga yi a ranta tace tun ba a je ko Ina ba kenan.
Haneef sai da ya shige dakinsa ya samu Ihsan a bed dinsa a kwance tayi mala mala cikin rigar baccinta me kyau.
AsmaBaffa
[2/23, 8:35 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI
BOOK 3
~TAIMAKO~
36-40
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM
PAGE NAKI NE
~aminaidriskafe
Baiyi tunanin dakinsa ta shugo ba ya ganta a kwance haka,guntun tsaki yaja sannan ya kalleta yace fitar min a room,kin kulashi tayi,yace ba da ke nake magana ba,idonta ta bude a hankali tace na dawo ai,ka daina turo Yar aiki tana damuna dole sai na dawo kwana a dakinka,ka fada min ni da Kai ba wata Yar aiki ba,ka daina nuna min kana sonta dan wai nayi kishi,yanzu so kake nazo na dawo,ba matsala zan na kwana da Kai ka daina zancen sirrin mu da ita,tsaki Haneef ya ja yace baki da hankali amma naga alama,fitar min a daki,tsawa ya mata ta gaske ba arziki ta mike ta fara tafiya sum sum ta bar dakin yace stupid,ba aikin fari bare na baki iya sex ne aure an fada miki ya ja tsaki,Shirin bacci yayi
Ya Kwanta tare da fara tunanin Khadija,yana tuna abubuwan ta Yana murmushi,Ihsan ce ta dawo ta sake haurawa Saman bed ta kwanta a gefensa,tashi yayi Yana masifa nace bana bukata dole ne,kin Raina min hankali ma,1yr da aurenmu tun farko Ina binki sabo da mu samu mu shirya mu zauna lafiya,ni ke kin sani Umarni nabi ba wai ni nace Ina sonki ba,amma duk da haka na danne na nemeki akan mu zauna lfy nan gaba zamu Iya fara son juna amma ke tunda aka yi aure ba wani Abu na kyautatawa da kika taba yi min.
Prison naje baki taba zuwa ba ko sau daya,daga aikinki sai yawace yawace,sabo da kina da kudinki,wlh shi yasa Maza suke Hana mata aiki,suke karya su idan sun fara samun kudi sabo da wasu irinku mahaukata da