Showing 93001 words to 96000 words out of 108220 words

Chapter 32 - Tantiriya A Gidan Yari Book 3 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

694

jariri Nima sai kazo,Papa yayi dariya yace zanzo Inshaallah,na Arham dai in za a haihu har asibiti zanje,dariya suka yi har Arham Dake ya fito shi da Basma zasu tafi,shi yasa Papa yayi zancen ma,Arham yace Allah ya kaimu,ai Bata da ciki wata nawa Amarcina nake Sha kawai ai haka yafi,Papa yace Allah ya bada na gari,yace Ameen yaushe zaka zo muyi hira ne?Papa yace sabo da yana son yayi hira da Spark da Arham,in suka zo ko banza yayi dariya,Rafeeq shi in yaga dama ma yaji yake ya daina zuwa,Misam ma basu Shaku ba,in yazo ma basa hira, Arham yayi dariya yace yau ma dan na gaji ne amma da tuni na zance ka da magana sai na dawo zanzo weekend ai Papa Soja sarkin fara'a,irin wai yasan baya fara'a sosai shine yace sarkin fara'a,Basma tace Papa mun tafi yanzu munyi hankali,Yace to Basma Haka ake so ayi ta hankali,tace to suka tafi, Papa yace a ransa Ina kuka ga wani hankali ai sai dai gaba kuyi hankali tare.

Naila tun a mota ta kira Yan uwa ta fada musu,Mohsin ta fara fadawa,ta fadawa Umma ,ta kira wayar Abba sai da yaji ance ta haihu ya daga wayar Yana murna,tace Abba na haihu,yace Inyee su Naila an girma za a fara koya tarbiyya,Allah ya raya bisa sunna tace Ameen,yace yawwa karki biyewa su Goggo da kauyenci baza a amsa addua ba, kowa yace Allah ya raya kice Ameen, kanki tsaye ki amsa Ameen idan ance kinyi fitsara kice ni na saki kakan yaro ne,Naila tace Nima dai shine na Gani,yace yawwa karki yarda da kauyencin su Goggo,Sannan karki matsawa mijinki da maganar kashe kudi akan kin haihu nasan ku mata in kuka samu waje sai Kun Kai mutum bango ki bari duk abinda ya siya kiyi godiya,Naila tace ai dama Abba ai ba kullum ake kwana a gado ba,Abba da sauri yace a'a Banda ni" Naila kullum a gado nake kwana tun Ina jariri akan gado karami na babata ake dorani" babata Kuma da Mijinta babana kenan suna kan babban gado ni Ina karamin gado,har na girma aka mayar min da gadona dakina gashi har na auri Yar Inna yau shekaru kusan arba'in ban taba fashin kwana akan gado ba,Naila tace gaskiya ne tana murmushi,yace sai bayan suna zamu zo da Yar Inna,su Hidaya dai da su Zarah zasu zo kafin suna,tace to Allah ya kaimu.

Suna komawa gida Naila tace yunwa nake ji da bacci,Spark wanka ya shiga yayi wanka sosai ya fito tare da saka sabuwar jallabiyarsa da Mohsin ya kawo Masa,Naila a dakinta Goggo ta sake yi mata wankan yamma,bata shirya ba sai da taci abinci dare yayi sannan kaya ta sake canjawa ta saka rigar baccinta doguwa me kyau me gajeren hannu Orange color, Goggo tace sai an daure ciki,Naila tasa abin daure ciki na Yan gayu Wanda a kasar waje ma aka siyo mata kala nawa da kyar ake matse ciki da shi na rage girman ciki,sai da ta saka sannan ta shafa turaruka ta Maida rigar Baccin kamar ba ta sa komai ba ciki ya lafe ya dame.

Goggo ma wanka tayi ta fito ta hau Naila da fada yanzu dama da nace ki bashi nono Baki bashi ba? tunda aka haife shi sau daya kika bashi nono sai zam zam kawai aka bashi fa,wannan wacce mugunta ce,boyon nono ya kare yarinya cewar Goggo,Naila ta dauki Jaririn Yana ta cin hannu Yana zare Ido, Goggo tace tsaya na koya miki yanda ake yi,sai da ta koyawa Naila sannan tace to kiyi Bismillah,Naila tayi Bismillah ta juya baya ta fara bashi wai Goggo baza ta kallar mata nono ba,Goggo tace a gaban mu fa kika yi nono har ya girma me zaki boye min shashasha,naga dazu ni nayi miki wanka,Naila tace naji ga Abinci nan Goggo ki ebi abinda kike so,Goggo tace mijin naki fa? Na zuba Masa nasa kina wanka na Kai Masa,Goggo tace Iyye kaji kula da miji,dariya Naila tayi,Naila bayan ya Sha daya ta juya shi yanda Goggo tace ta bashi dayan,Yana Sha Goggo tace ai ya koshi haka,to rike shi a hankali karki hantsila shi zaiyi amai,Naila tace Kai wannan yaro haba ace wannan ace waccen,sai da ya huta tace bari na kaiwa Daddyn sa shi ya ganshi,Goggo tace kwaji da shi munafukan banza wlh ki dawo a nan zaki kwana,Naila tace to,ta fice da danta cikin showel ta shiga dakin Spark Yana cin abinci Yana kallo ta shigo

Ya kalleta Yana Jin dadi a ransa yace fada ya kare tace ae mana,kallonta ya sake yi yace wai dama idan an haihu kyau ake yi ne? duk naga in kuka haihu sai mace tayi wani kyau fatarta tana shining,Naila tace ai haka yawanci ake yi sai zuwa arba'in ake dawowa normal,Naila ta juyo fuskar jariri tace ka ganshi fa Kaine babansa Kai ka haifi wannan,Spark yace duniya sabuwa SparkNaila kamanninsa biyu,Naila tace Nima haka nace kamanninsa biyu,sai da ya gama cin abincinsa ya dauke shi,wanne suna za a sa Masa ne? Naila tace oho ka zaba,Spark yace Papa Ahmad in yayi miki a saka idan kina da zabi ki zaba,tace a'a Banda da zabi Kuma ai suna me dadi ne na kololuwa Ahmad fa,Allah ka raya Ahmad bisa sunna,Allah kayi Masa Albarka kasa ya zama mahaddacin Alqur'ani,Allah kasa yayi koyi da fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW),Allah kasa duniya ta amfane shi,muma iyayensa ya amfane mu ya zame mana Alkhairi dukkanmu da Yan uwa da Al'ummar musulmai Baki daya,Allah yasa yayi suna ta hanya me kyau,ya shahara a duniya ta hanya me kyau,ba shaharar Dan Boko Haram ba,Bata Dan kidnapping ba,Bata Dan daba ko wani Dan iska ba,shahara ta hanyar abin Alkhairi,Allah yasa Shahidi ne,Allah ya Masa Albarka,Wannan Dan nawa Ahmad Allah ya sa Masa Albarka,Allah ya bashi lafiya da tsawon rai,Allah ya azurta shi ya raba shi da talauci,Allah yasa Dan Aljanna ne,Allah ya bashi mata ta gari Irina kyakyawa,Spark Yana ta amsawa da Ameen Ameen Yana dariya yanda Naila ta dage take surfa addua ta daga yaro sama tana cewa Allah ga Dana Ahmad,Allah ga Dana Ahmad,ya Rab ya Rab,ya Rab ka amsa addua ta.

Tana gamawa Spark yace well-done uwa ta gari haka ake so wlh uwa ta fara yiwa danta,Shima ya karba yace kawo shi Nima nayi nawa Shima ya tallafe jariri ya Dan daga sama kadan ya fara zubo addua tana amsawa Ameen...Ameen..Ameen sai da suka gama sannan Spark yace yaushe zan dauke shi ne ya tsula min fitsari? Dariya Naila tayi,yace to ai ya kamata ace Danka ya Maka fitsari,Naila tace saurin me kake yi zaiyi ne ai bari a fara barin duwawunsa Yana hutawa ka gani,har Kashi ma zai Maka watarana,yace Ina maraba indai na dana nane,spark da baya daukan yaro amma shi yake neman fitsarin dansa yanzu.
Naila ta dauki Baby tace bari naje sai da safe,sai da safe Ina?wai Ina bed din Baby ne,Goggo tace tare zamu na kwana,yace muje wajen Goggon ni zan mata bayani akan mene haka zamanin da ne wannan.

Spark tashi yayi suka tafi da Naila yayi yayi akan Goggo ta fahimta amma Goggo taki yarda,fita yayi Dan yaji haushi,Naila tace Kinga yaji haushi in haka ne mene amfanin yace bazan zauna a wajen Mima ba,wlh ba wani Abu zai min ba,kin sani kema ba halin yin komai,sabo da haka yasa aka taho dake,kullum muna tare dake da jaririn ace bazan kwana a can ba,Goggo tace wlh bari na kira uwarki na fada mata tunda baki da kunya tafiya zanyi,Naila ta kwanta a gadon ta ajiye Baby a gefenta,Spark shi kadai ya kwana ya hakura Kuma da safe ma bai ce komai ba bai nuna fushi ba ko a fuska har wasa suka yi da Goggo,washe gari haka Goggo tayi komai na gidan ta gyara ko Ina ta kula da Naila da Baby,girki me aiki tayi,haka Naila ta sake kwana da Baby da Goggo har kwana uku,kwana na ukun ta kira Abba a boye ta fada Masa,Abba yace kyaleta bari na kira ta,Abba ya kira Goggo ta daga waya,yace wanne dalilin zaki je ki Hana su sakewa daga ganin sarkin fawa sai Miya tayi zaki,birni ba haka ake yi ba yanzu,ki kyale yarinya,Goggo tace so take ayi mata wani cikin da wuri,ayi mata mana ke Ina ruwanki a jikinki yake,ana ta murna a kira Goggo sai kizo ki watsawa mijinta kasa a Ido ki kyaleta,iya aikinki kiyi Dan Allah.
Goggo tace shike nan tunda ku birni Kun lalace babu kunya taje ta kwana,idan yaro Yana kuka ai tayi sintiri a hanya zuwa dakina, yace ba komai tayi sintirin ya kashe wayarsa.
Naila tana shugowa Goggo tace munafuka har da fadawa ubanki kije kiyi ta kwana ai mayyar miji,dariya Naila tayi tace naji.

Yau da dare bayan Yan barka sun tafi tayi wankanta ta saka riga da wando blue na bacci ta Sha kyau ta dauki Danta ta yiwa Goggo sai da safe,ta shiga bedroom din Spark,baiyi tunanin kwana zata yi ba,yace Goggo ta ishe ni da nasan haka ne bazan kawo ta ba wlh,Naila ta fara hada gadon Baby a gefen nasu hadadden bed fari tas da shi,Spark yace ta yarda ne ki kwana? Naila tace tun yaushe na fadawa Abba ya kira ta a waya kuwa yace ba ruwanta da mu,Spark yaji dadi yace yawwa tsohuwa ta ishe ni haba,Naila tayi dariya ya dauki Baby,yace yaron nan ya bani wahala kafin yazo duniya,Naila ta bashi nono ya Sha ta kwantar da shi.

Yayin da Maryam kanwar Annoor ta samu miji bayan ta murmure tayi aure abinta itama,suna ta zumuncinsu da Annoor.
Ihsan tana yin Idda ta samu saurayinta da take so tace tana sonsa bayan ta bashi jari ya kama business babba,ta kashe Masa mugun kudi,ta siya Masa mota bai taba cewa Yana sonta ba sai dai ya nuna shi kawai birge shi take yi,tun tana jira yace Yana sonta har ta gaji ta fada Masa da kanta,kowa ya gansu zai ce masoya ne yanda suke mu'amula,suke waya,yake zuwa gidanta da sauran su,yaci kudinta matuka,Ashe shi Yana kama kasa ya koma wajen Tsohuwar budurwarsa da aka hanashi sabo da baida sana'a Yana komawa aka ce ya turo Kuma ya Kai kudin aure,a ransa tayi tunanin ko ya auri Ihsan din sai yaga tafi karfinsa ita tana da kudi baza ta juyu a wajensa ba kawai ya nemi dai dai shi,sai da Ihsan tace tana sonsa yace ai shi an saka ranarsa da wata,Ihsan ga aji tace ba komai ba damuwa kamar gaske ta nuna bata damu ba, Ashe Kara ta shigar kotu ta kashe Masa kudinta ya yaudare ta zai auri wata.

Sai da suka je kotu sannan ma yaji labari ta taba aure duk lokacin da take kulashi tana da aure,Nan yayiwa Allah godiya da bai aure ta ba, Alkali yaji ma kudin ba roka yayi ba babu manufa kawai ta dinga kashe Masa kudi,Alkali yace ficika bazai biyaki ba tunda yarjejeniya kuka yi ba,haka kawai kika bashi kyauta Kuma kin amsa,Ihsan tace Dan me bazai gane sonsa nake ba shi Dabba ne,Sadeeq me kurkura yace nasan gaibu ne ni da zan gane,Alkhali ya dakatar da su yace Allah ya azurta Sadeeq ta hanyarki,ki hakura ki nemi ladan Allah sai Allah ya baki wani na gari,Ihsan tace ni ban yarda ba,Alkali ya Kori Kara yayi rubutu matukar ta takurawa me kurkura sai an yanke mata hukunci,Ihsan ba nasara ta rasa Inda zata sa kanta gashi ta bari an sake ta,gidanta na Kano ta dawo ta kwana tana kuka da Dana sani,washe gari da safe ta nufi gidan Haneef.

Gidan ta gani komai ya canja ya Kara haduwa,sababbin motoci ba Wanda ta sani ba,ta danna door bell,ba a Dade ba Khadija ta bude kofar wow,ta zama wata Yar gayu da ita,ta Kara kiba da haske ta zuba kyau cikin kana Nan kaya,Ihsan mamaki ya kamata kamar ba Khadija ba,fuska ta bata tace uban me kike a gidan nan har yanzu,Khadija tace ubanki nake yi,an sake ki me ya kawo ki nan gantalalliya,Khadija ta kalla sosai taga ciki a jikinta bakin ciki ya tokare Ihsan a makoshi,Honey Mero ta shiga kwalawa kira ya fito yana cewa na'am Beb,yaga Ihsan da mamaki yace ke me ya kawo ki ya bata rai,Ihsan tace Baby Dan Allah kayi hakuri,Babyn ubanki dalla fitar min a gida,rungume Haneef zata yi Khadija ta fyalle mata Mari, tace dama haushinki nake ji an sakeki ban sani ba,Haneef yace fitar min a gidana Ihsan,ni kake kora Haneef Ina Yar uwarka yace an Kore ki,karki zubarwa da matata ciki da fada,ya fisgi Hannun Ihsan ya bude kofa tare da jefata waje ya kulle kofarsa,Mero ta harda goge masa hannu hannu kamar ya taba Kashi ta goge masa tace muje.

Haneef ya dakkowa Mero me koya mata karatun Boko tana yi sosai sannan zata zana waec Nan gaba ya sata a makaranta,gashi ya siyawa Jummai gida madaidaici a birni tare da danta Mummir,ya saka Munnir a makaranta sannan ya bude Musu katon shagon cosmetics,Munnir Yana juyawa,Jummai tana siyar da kayan kanti shago guda ya mata a gidan,abinci da komai basu rasa ba,sannan da su za ayi aikin hajji badi harda Mero da shi zasu tafi gaba dayan su.
Mero tace ya kamata naje har gida na gaida Spark da su Mima suga ci gabana,sannan naje prison na nunawa Mummy da tace ban dace da suna Khadija ba sai dai Mero,Ina ji ina Gani ta rada min Mero,sabo da banyi Ilimin Boko ba bamu da kudi mu Yan kauye ne,gashi yau ita ta kare mata ni Kuma Allah ya daga ni,Haneef yace ya kamata kuwa muje gaskiya.
[3/9, 9:38 AM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

BOOK 3
~TAIMAKO~


81-90


Official

By
AsmaBaffa


SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM


PAGE NAKI NE
Yar Gatan Annabi



Mohsin tun a mota Beauty take Masa korafi yanzu da ba'a gyara gidan ba fa? ai sai ka fada min,ni naga Umma tace Inzo muyi girki ana ta shirya girki na musamman Ina ta mamaki Ashe Kaine zaka dawo,surprise na miki, a'a ni bana so wlh ka daina min haka,sai da ya shiga gidan da motarsa ya rufe gate zata fito yace ki zamanki a mota a ciki zan bare sabuwar Amarya ta,Beauty tace ikon Allah mutum da bedroom da komai sai kace Yan iska,yace ba wani nan na gaji kullum Abu a daki,daga bedroom,Palo,toilet shike nan fa ai a dinga samun canji,yanzu wasu ma'auratan a duniya tunda aka aure su a waje Daya suke Abu daya,wasu basu taba barin bedroom ba,kullum a waje daya ba chanji,ai yanzu ma zamu fara yawace yawacen mu gari gari ko ba kudin fita waje ko su Lagos ai ma dinga zuwa,ga su Kwara state mu kwara kauna a can,Beauty tayi dariya yace ai kune wasu mata bama Kwa so a fita da ku,mijinki Yana da Dan budi ko katsina ai Kwaje kawai aci Aya ayi kauna,Beauty tace ai ni kasan ko nan da inane zanje indai da Kai,suka ajiye Baby a gaban mota suka shige bayan mota kamar Yan iska mota sai Lilo take a compound suna Kwalbewa.

Ranar Sunan Chika Yana zuwa yarta taci Suna Nasreen,an Sha suna anyi shagali.
Naila ana kan gaba har da wani Dj suka kawo sabo da bikin Mufee da Haidar, Iyalan Jauro Maza Abuja suka taho daurin aure,abokan Ango,Mohsin da Abba duk sun zo,Naila tayi tayi su Abba su kwana sun ki,Mohsin ya kawo mata tsaraba sosai,Chika ma an bata da Ikhy Abaya,harda kawowa Spark jallabiya kala biyu masu tsadar gaske fara da coffee color da turare me kyau.
Washe gari aka Kai Amarya Mufee hadadden gidanta kusa da su Iman abinsu sharr, su Iman sune masu tabbar Amarya gaba dayansu yara da su,bayan mutane sun watse Haidar Allah Allah yake ya fada dakin Amaryarsa,ga Mufee Jinin su Zeenatu ba wata kunya ce da ita ba,tayi tunanin wani dadi ne da first night din.
Sai da Haidar yazo suka gabatar da duk wani abubuwa na farkon aure sannan ya goge mata hadda gaba daya,Yar rashin kunyarta data kwaso daga Abuja duk ta Maida abarta cikinta ta hadiye,sai dai bata Sha wahala irin wasu ba,ba yanda ake tsammani ba,washe gari ma da kanta tayi komai tayi girki abinta,Mufee an dage an koyi girki kafin aure,Haidar har wani Santi yake yace daga Jin wannan girkin na tsohon hannu ne tun kina karama kike koyon girki? Mufee ta shararo karya tace ai mu tun muna Yan yara Mima take siyo mana Yan tukwane na yara muna gwada girki,tun muna yin na wasa har muzo ta kaimu kitchen,tana nuna mana zuba Maggi kaza,zuba curry,zuba gishiri kamar haka"a haka har a fara barin mu muna girki da kanmu abinmu.
Haidar Yana Jin dadi Yana washe baki yace ai da gani Kun samu tarbiyya sosai,haka ake son iyaye,Mufee tayi dariya a ranta tace shiryuwa kawai muka yi muka ga rayuwa haka baza ta kaimu ko Ina ba muka canja,a fili Kuma tace gaskiya sai dai mu godewa Iyayenmu,Haidar yace bazan taba godewa nawa ba sai dai Kawu Jauro da Umma Habiba,suyi min laifi na gode musu a wanne dalili,Ina dai ganin girman su Ina mutunta su a matsayinsu na iyaye,Kuma bazan yarda wani ya wulakanta su ba amma na gode musu akan me,me suka yi na bajinta a kaina, Allah ya kyauta dai,Mufee tace Ameen ai ba laifin mama,yace to da sauki dai,dariya tayi suka koma hirarsu ta kauna.

Bayan wasu watanni Naila cikinta ya tsufa sosai bata da karfin masifa yanzu sai kuka da fushi,yau da dare ta kasa kwanciya ta juya gefen dama taji bata Jin dadi,ta tashi zaune ta juya gefen hagu,Spark Yana ta latsa waya abinsa bai San ma tana yi ba Yana kwance a gefenta,Naila tace ayi bawa idan zai juya ma ba dama sai ya mike zaune kafin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login