Showing 24001 words to 27000 words out of 108220 words
Chapter 9 - Tantiriya A Gidan Yari Book 3 Complete Hausa Novel
dazakiyi daga gida da kuma baya bukatan jari?
Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?
Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara Miki extra source of income?
Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?
Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din
https://wa.link/49vn47
Spark yaji Naila a jikinsa,narkewa yayi Yana shagwaba kamar yaro Dan yaye,duk ya makalkaleta Yana cewa Mummy ta tana can,Naila tana lallaba shi tace kayi hakuri zamu je ko gobe ka ganta normal,zata saba inshaallah,Yau zata yi Kwanan wahala ya furta,Naila ta gaji da korafin Spark yaki yayi shuru,ta hau romancing dinsa tace a ranta bari na gwada maganar su Misam,na tafi ace baka damu da miji ba, daga Dan fara kiss sai ga Spark ya zake,Booby daya aka sa Masa a baki tuni ya manta da wata Mummy a prison kamar Wanda aka Masa Allura ya watsake,Naila tace eyya bama ka Jin karfi a bari later kwanta ka huta kaji,muryarsa taji yace da karfi na zan iya komai ma,dariya tayi tace au da karfinka? Yace sosai .
Mero tana Isa gida sai Ganinta aka yi tsidik a cikin gidansu na bulon siminti ne amma kamar kango haka yake,wani tsohon rubabben gini ne tun ya zaman,dakuna uku ne a gidan sai kitchen din langa langa na karfe sai toilet,Inna ta iske a kitchen tana aikin soya awararta ta yamma,Mero tayi Sallama ta shiga,Jummai ta leko tace ya naji kamar Khadija,Baki ta bude duk taji kunyar yarta ta kasa zuwa su ganta a gidan yari,tace wani satin muke cewa zamu zo Khadija Ashe kina tafe,Munnir da ya fito daga daki yace wlh da kudi Yaya Khadija cewa tayi baza su ba tsada tayi yawa.
Mero tace ai gani na dawo,Jummai ta fito daga kitchen tace ya akayi na ganki Kuma? gudowa kika yi? Mero tabarma ta dakko ta shimfida ta zauna tace a bani abinci naci tukun naci na huta sai naji dadin labari,Ina Abbu? ya fita kasuwa,Jummai kitchen ta koma ta zubawa Mero shinkafa da wake da Mai da yaji ta kawo mata ta kawo mata awara a plate tace Kai Munnir ebo mata ruwa,Khadija ta zauna ta fara cin abinci sai da ta cinye komai tas ta Sha ruwa sannan bakinta ya bude,Abbu ne yayi Sallama ya shugo suka amsa,Baki ya bude ganin Khadija a gida,yace ya aka yi haka ta faru? Farin ciki ya kama shi ya washe baki yace Khadija kece?
Mero tace nice mana da baku zo ba gashi na fito,wai ku haifi 'ya a cikinku amma bakwa sonta haka ake rayuwa,kudi yafi da,Kun San bakwa son yara baza ku iya kula da su ba kuka haifo mu,Allah ya dube ku ya Baku yara biyu kacal amma baza ku iya rike su ba,sabo da son kudi,Abbu Murya a sanyaye yace wallahi tallahi Khadija ba laifi na bane laifin Jummai....Jummai itace mijin ko Kaine Abbu,ka zauna tana gara ka kamar tayar mota" ka karo kishiya mana kayi aure,yo magana ta Allah fa,Jummai baki ta bude tace Khadija ni kike cewa a karo min kishiya? Abbu yace kwantar da hankalinki Jummai bazan ma iya yi miki kishiya ba,Mero tana jinsa takaici ya kamata sosai na halin mahaifin su,Jummai tace tunda halinki zaki dawo da shi na fito na fito da ni akan ke sai kin koya min zaman rayuwa to wallahi ki koma aikatau,ya zama dole aikatau zan kaiki tunda samarin ma ke ba kula su kike ba bare ace za a miki aure to dole ki koma aikin wanke wanke da shara domin ki samo mana kudi,idan ba haka ba wallahi da katifa za a kaiki gidan miji,Khadija tace a kaini da abinda Allah ya hore,Abbu Yana ji Yana gani yayi shuru baya ko magana.
Jummai tace to gidan aiki zansa a sake samo miki,Mero tace na samo ma wlh a Kano Inshaallah gidan me kudi ne har gida za a zo a dauke ni,Inna sabo da sakaki ko a jikinta babu ruwanta da waye za a je gidansa burinta a samo mata kudi,Baki ta washe tace Allah ya kaimu Khadija Allah ya miki Albarka,ki bari ki huta ki murmure tukun,Kai Munnir zo kaje ka siyo mata kifi taci taji Dan dadi dadi,Sani uban Khadija Yana kallo Yana Jin haushi amma bazai iya magana ba,da kyar yace Jummai da dai an barta a gida ai Ina ga zai fi ko? Shawara na bayar ba umarni ba a dai duba,na yarje mata ta tafi baza ta zauna a gida ba mene amfanin Hakan,to shike nan Khadija Allah ya tsare ki kula kinji,ki tsare mutuncinki a duk Inda kike tunda kinji dai Hajiya Jummai ta gama magana.
Khadija takaicin Abbun su ya kamata ayi mutum kamar ba mutum ba,a ranta tace anya kuwa Abbu mutum ne? Suna haka wata bazawara ta shugo gidan Zuhuriyya Yar babba ce haka amma ba can ba baka ce kyakyawa Yar Fulani,kawar Jummai ce kut da kut,Abbu Yana kallon Zuhuriyya ta shugo ya mike Tare da gyara sallayarsa a bakin kofa ya tada Sallar Nafila ta dole ya dinga Sallah ba ji ba gani,har sai da Zuhuriyya ta gama abinda take ta tafi sannan ya sallame,Khadija tace Abbu meke nan Hakan? yace hanyar lafiya a bita da shekara Khadija kar ma mace tace ni Sani na kalle ta,ba ruwan Sani da mata,Mero shuru tayi tace ita Aunty Zuhuriyya din ai Abbu ta kirki ce,kana gani kullum shawara take bawa Inna tana nuna mata hanya Ina ruwanta da Kai,Kai da ake so ka zama mijin mace hudu,Abbu yace mace hudu Khadija? Jummai Kuma inyi ya da ita? Itama tana cikin matanka Abbu,a'a Khadija barni da ita din kawai,uhm uhm Abbu yanzu yayin mata biyu ake shine gayu shine cinyewar,yace a'a ba ruwana ,Innar su Khadija tana kitchen bata San me suke ba.
Mero tunda ta dawo mutanen garin suke cewa Yar mace ta dawo, taki aure ta gandame a gida bata da me aurenta,ko ta kansu bata bi" haka tayi sati guda duk kauyen ya isheta tace ga Inda zan ta kallon Yan gayu da wanka ko ta Ina,ko ban samu samu miji hadadde ba ai yafi min akan zaman kauye.
Waya ta samu ta Nemo karama ta siyeta dubu hudu ta sa layi ta kira Haneef,tana shiga amma ba a dagawa, yini tayi tana kira ba a dagawa,da dare ma da ta kwanta haka ta dinga gwadawa amma ba a daga ba.
Bangaren Haneef kuwa tunda gidansa suka nufa direct matarsa Ihsan ya samu a katafaren Palonsa tana zaune ta Sha gayu cikin kana Nan kaya riga da wando tight milk and brown,ta Sha hular gashi me kyau tare da Dora Yar facing cap a kanta,tana latsa wayarta me tsada,ganin mutane Bai Sa ta canja kaya ko ta saka Hijab ba haka tayi zamanta,aji take ja da kyar tace sannunku,barka da fitowa,Su Hajji suka zauna Haneef ko kulata baiyi ba ya haura sama,kin tashi tayi ta bishi sai da Hajji ya gaji yace ke wacce sakarai ce ne? Wacce shashasha ce ke ne? Mijinki guda ya fito daga prison amma ba farin ciki ba komai,Sai lokacin ta mike ta bishi sama,tana zuwa ta samu ya shiga wanka,zama tayi a gefen bed dinsa hadadden gaske tana ci gaba da chat dinta,tayi mugun Dadewa kafin ya fito daga wanka,Yana fitowa ya ganta me ya kawo ki nan? Ihsan tace Hajji yace nazo kasan in ba cewa aka yi nazo ba bazan zo ba,ka sani ba wai niyyar kaina bace abinci yana dining Kuma me dafa maka abinci ce tayi ba ni ba" tana fadar haka ta mike ta fice.
Ita Ihsan tunda auren zumunci aka musu ba wai sonta yake ba itace ta damu da shi har aka yi bikin maimakon ta kwantar da Kai tayi biyayya baza tayi ba,tunaninta kullum shi Haneef sai ya gaji ya sakko da kansa ya kawo kansa da kansa,gadara take tana da kyau da komai da namiji zai so a jikinta sabo da haka ba sai tayi biyayya ba,itace mace itace take da aji,sai dai namiji yayi fadanci a wajenta ba ita ba,sannan tana ganin tana da babban aiki,babban matsayi ne da ita a company tana samun kudi sosai ba ruwanta da kudin namiji bata ga dalilin da sai tayi biyayya ba,shi yasa take abinda taga dama,yanzu ma company ne ya dawo da ita branch din Kano shi yasa aka ganta ta dawo gidan Haneef a nan amma ita a Adamawa take can gidan Haneef na can,sanda Wuta ta Kone Khairat ba karamar murna tayi ba a haka wai duk bata son kishiya Kuma,bata aikin fari bare na baki sai dai aikinta in tana gida Kuma chat ta fesa wanka ta zauna tayi Kallo,Bata fiye fada ba Kuma ita sabo da ajinta zai wahala kayi hayaniya da ita,tana da aji ita dole me aji ce,sai dai ta guma Maka takaici ta wuce.
Tunda Haneef ya aure ta sun Kai Shekara kenan amma sau uku zuwa hudu ta taba kwana da shi,har wani Abu ya shiga tsakaninsu,tunda taga in Bata je ba bazai neme ta ba,sai idan taje wannan zai nemeta normal sai ta daina zuwa tace sai ya kawo kansa da kansa sabo da ta isa itace me aji ba shi ba.
Shi Kuma Haneef Yana ganin abinda take yi haushinta ma yake Kara ji sabo da duk wani Abu na macen aure bata yinsa shi yasa baya kulata,ya Kai kararta sau biyu duk dangi ita Ihsan suke goyawa baya ai shi zai lallabata sabo da suna ganin auren zumunci ne ko ya Kai karar ba a daukan mataki shi yasa ya gaji ya watsar da zancen ya watsar da ita kowa yake Uzurinsa.
Sai da ya shirya ya canja sutura me kyau cikin jallabiya fara me tsada dai dai shi sannan ya fito ya samu su Hajji su har sun ci abinci tafiya ma zasu yi,ya raka su suka shiga mota yace a fadawa Ummi ya bata zo ba Danta ya dawo,Hajji yayi murmushi yace zata zo ne a satin nan ko na sama tace,yace shike nan zan kirata a waya,in Kun isa lafiya ku kirani,yace to driver ya kaisu airport suka wuce shi Kuma Haneef ya dawo ciki,dining ya duba gaja gaja an lalata me aikin ya kwalawa kira Salamatu" fitowa tayi da sauri yace ki gyara dining sannan zan kawo wata me tayaki aiki,bana son Yan aiki barkatai zaki dinga gyara gidan nan ita zata dinga girki,Salamatu tace to Oga Allah ya kaimu, babbar mace ce ita Salamatu,yace me gadi fa ana bashi abinci? tace kullum sai ya koshi Oga,yace Good job yana murmushi yace zuba min ta zuba Masa ya dauki plate dinsa ya koma Palo Yana kallo yace Kai sai naga plasma din ta Kara min girma ko dan a can babu ne"
ya Kalli gidansa yace Allah na gode Maka Ashe dai ba karamin hadadden gida nayi ba,sai yanzu na gano haka da naje prison,ga ac ta a can kuwa Ina wata Ac ta kirki,uhmmm ji Parlo komai me tsada ga kyau ahhh nasha wahala,shi yasa nake ganina kamar a Aljanna nake yanzu.
Yau da wuri ma zan kwanta sabo da na hau katon bed Dina naji dadi in more rayuwa ta,da ace waccen Yar iskar mutuniyar arziki ce ai da sai ta zo ta Sha madarar Nido Inji Scola,tunda tafi so a bar mata abinta haka kullum a lullube taje da abinta ta Shekara tana rufewa,Dan ta ni in taje wanka ma kar ta bude,ita kuwa Ihsan tana garden tana hutawarta Bata San me yake cewa ba.
Sai magriba yaje masallaci ya dawo Yana Sallar Isha ya kwanta abinsa,tunda ya dawo sai da ya kwashe sati guda Yana hutawa sannan ya koma aiki,Yana ganin kiran Khadija kullum amma bai San number din ba,yayi busy da yawa sai da ya cika 10days da dawowa sannan ya daga kiran Khadija,Yana dagawa yaji muryarta bai San ita ce ba,sallama tayi kana magana da Khadija ta gidan yari,Yana Jin Muryar ya gane dariya yayi yace wacce Khadija fa? Khadija me fasa gini mana dalla wacce kake ba Madara ta Yar kafa wai meye haka Dan Allah ka gane ni ka dinga wahalar da shari'a ,murmushi ya saki yace ohh Yar aikin da zan dauka?Mero tace duk Inda talaka yake sai me kudi ya nuna Masa rashin Kara kiri kiri ba komai itace ei itace Yar aikin,kin shirya ne? Mero tace tun yaushe Kuma na shirya na ma fada a gida sun yarda.
Har kin gama Shan kokon ya ishe ki da awarar taku,Mero tace na Sha mana Kuma na fika lafiya ba,yace to yaushe kika shirya? Nifa a shirye nake ko yanzu,yace to gobe da yamma ki shirya za a zo a dauke ki, Allah ya kaimu,ki bar wayarki a kunne kusa dake sabo da kwatacen gidanku,Mero tace sabo da rashin tabbas din karfen nasara bari na tura ma text ko da network yayi tsiyar kaga ai an San Inda nake,yace Alright Allah ya kaimu,badan yayi dariya ba sai Mero taji kamar bai San wace ce ba yanda yayi magana.
Washe gari sai da yamma likis mota hadaddiya tayi parking a kofar gidan su Khadija,Khadija babu suturar arziki 'Yan tsumman da suke a gida nata ta zabo kala uku masu dama dama,wacce ta dawo da ita daga prison a jikinta shi ta wanke ta goge Leshi yellow and Golden ta saka a jikinta,Mayafi ma tana so ta danyi too match amma ba dama haka ta dauki Hijabinta blue na yadi Dan Madina ta saka abinta ta fito dauke da ledar kayanta,Jummai sai murna take yi tana addua Allah yasa Khadija kije a sa'a Allah yasa wannan yasa shine silar arzikin mu,Allah ya zuba mana sugar a bakinmu Khadija karki bari ya zube bamu lashe ba,Dan Allah kiyi aiki me kyau Banda shiririta,Khadija tace to Inna baki sa min albarka ba,Inna tace Allah ya miki Albarka,Allah ya Bada sa'a,Abbun su Khadija Yana kasuwa tace ki cewa Abbu na tafi,zan fada Masa,Munnir Yana jinsu Yana tabe baki yace mutum yayi sana'arsa a gida bai fi ba amma ka dauki Yarka ka kaita wata uwa duniya baka San Inda take ba Allah ya kiyaye kar a yiwa Yaya Khadija Cikin shege,Harararsa Jummai tayi,har mota ta raka Khadija ta dawo tana ta tsalle tana murna a mota aka zo daukan 'yata,'yata tayi goshi,Munnir tashi yayi ya bar gidan gaba daya.
Khadija kuwa tana mota a baya daga ita sai driver ba Wanda ke kula wani,duk surutun Mero shuru tayi har suka je unguwar Mero sai kallon hadaddun gidaje take yi,suka Isa katafaren gidan Haneef, ta Saba ganin gidaje masu kyau a Abuja shi yasa kalle kallen nata yazo da sauki,gidan Haneef ya hadu karshe ga motocinsa nan iri iri,Driver ne yayi mata iso har Parlo,tana bayansa Yana gaba,a Palo suka samu Ihsan taci shadda sky tana zaune tana Shan fruits,Mero gabanta ya yanke ya Fadi ganin Ihsan Masha Allah da ita son kowa kin Wanda ya rasa,a ranta tace Nima da kyau na ai ba fina tayi ba,ko haske baza ta nuna min ba sai gogewa da hutu kawai,fili Kuma tace Hajiya muna ta sallama Baki amsa ba,babu kyau wlh kaji sallama ka share a Islamiyya an koya mana,tuni Driver ya juya,Ihsan ta Kalli Mero sama da kasa a wulakance tace ke kama kanki,kece Yar aikin da Haneef yace an samo? Mero tace aka samo? Kamar kifi a teku Wanda babu me shi aka dakko dai ko Aunty, Ihsan Ido ta zaro tace Kinga bana son magana ta kwalawa Salamatu kira,Salamatu ta fito tace ga Yar aiki an kawo ki nuna mata komai ki kaita dakinta Dan Allah kuje bana son damuwa.
Salamatu ta ja Khadija bangaren masu aiki ta nuna mata daki da bed da mudubi harda sip dakin me kyau abinta ita kadai,Mero tace ko a gidan miji ka samu wannan ai soyayya sai ba za ayi ba,Salamatu tace ke dai bari Yar uwa kin ga sanda aka kawo ni gidan Nan Inda kisan Yar gudun hijira amma yanzu kalleni kamar takari a saudiyya,Mero tayi dariya tace ai Aunty sai ace ma kece uwar Ihsan din matar me gidan,Salamatu tace ke rabani da wannan ba mutunci ne da ita ba,Mero tace nima Ina da degree din nawa rashin mutuncin,nawa degree din na rashin mutunci dan Cotonou ne ma,Salamatu tace kar a Kore ki baiwar Allah yarinya kibi a sannu kina Yar aiki Ina ke Ina ja da masu gida,Khadija tace zauna ki zuba Ido Aunty Salamatu ni ba ruwana da matarsa Ihsan,shi fa zanwa aiki Kuma ma muna mutunci da shi Yana da kirki,Salamatu tayi murmushi tace ke akan ma'aikatansa bashi da wani sauki aiki kika zo aiki zaki yi Kuma zaki Gani zaki ce na fada miki.
Abinci ta kawowa Khadija tace sunanki Khadija ko? daga gobe zaki fara girkinki a kitchen ni ya Maida ni gyaran gida,Mero tace Allah ya kaimu.
Mero tana nan har dare Bata ga Haneef ya shugo ba,ta fito Palo ta samu Ihsan ta canja sabon wanka da key din mota a hannunta da alama fita zata yi,ko kallon Khadija Bata yi ba ta fice,Mero tace mu ai sai mutum ya bude baki ma yayi magana komai shariyarsa Ina nan dake sai Kinga na fara yiwa mijinki tausa tukun kina Nan,tana zaune a kasa tana maganganunta taji kamshi ya mamaye parlon dagowa tayi a hankali tsorata tayi sosai ganin mutum a gabanta,kirji ta dafe tace wlh na zaci aljani ne,kallonta Haneef yayi tace Ina yini,ya amsa da lfy Alhmdllh,kawai sai Taga ya shareta kamar Bai Santa ba ya zauna a kujera,Mero tace kai, Salamatu ta fadi gaskiya kuwa ba mutunci,wani film aka saka aka fara series ne American film suna ta kallo.
Khadija