Showing 87001 words to 90000 words out of 108220 words

Chapter 30 - Tantiriya A Gidan Yari Book 3 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

689

mike tana shafa bayansa tace Allah ya Maka baiwa, Spark yace Alhmdllh,toilet ta bishi suka shiga tana wayo tace inyeeee Spark din ba jiki duk kyau dumi dumi da kai,Yana boye dariyarsa yace Dan Allah cije ni ki huta ki daina damuna kamar mayya,da haka kawai yace mata kamar mayya cewa take ya mata kazafin Maita sai ta saka kuka,amma yanzu harda cewa ni ba ruwana wanka kawai zan Maka,mu Kwalbe a nan kaji please tana shagwaba,yasan manufarta Yana cikin Kwalbewa zata cije shi shine burinta,wayo ya mata yace to ai kuwa kin kyauta min ya jawota jikinsa suka fara sarrafa juna,sai da ya shigeta hannu yasa a dai dai wajen bakin ya toshe yace karki min ihu da yawa nasan halinki,ni ka sakar min bakina..zanyi ihun dadina...ta fara kokawa da shi tana Fisgewa,gashi tana enjoying sosai haka ta hakura suka kwalbe iya Kwalbewa sun Dade suna abu,wanka suka yi suka tsarkake jikinsu,Spark yana wani jinsa zam zam ya manta da batun cizo ta zagayo ta bayansa tare da cizonsa a baya ta arce da gudu tana dariya,sabo da sauri ma ko zafi bai jiba kadan ta cije shi,Yana fitowa tace fyade yayi mata bayan dadin da taji abinta ta manta.

Suna shiryawa tace ni yau Hijab zan saka har kasa Spark yace ai Yana miki kyau,tace to Allah kwalbewar yau tafi ta kullum dadi idan mun dawo a Kara,yace ai ke kullum dadinki na daban ne,sai naji kullum kamar sabuwar Amarya na aura daban, kullum dandanon na daban ne,Naila tace tunda aka yayeni nake Shan madarar shanu me zafi, Spark yace ai kuwa gashi Ina ta Shan tawa nima ta jikinki,so nake fa mu bar kasar Nan Kwanan Nan in samu International water in baki International milk,dariya tayi ta Dake shi a kirji tace Allah da sa'ana nane kai yanzu sai nace shege mutumina amma mijina ne kafi karfin haka,sai dai Kai a zageka da bado ko?,Spark yayi dariya kamar ba gobe yace ai kin zage ni ma,ambola zan na Maka da bado yanzu in ka bani haushi,Spark yace kice akwai kallo,ni Ina so wlh a dinga min kullum.
Spark jallabiya ya Sanya suka tafi da girkin Naila kala biyu.

Suna zuwa a can suka iske Misam da Chika da tsohon cikinta,gidan Maman Rafeeq daki guda aka ware,me jego da Mijinta suna zaune ga Arham da Amarya an kame a gefe,Spark Yana kallon Arham ya tuntsire da dariya,shi dariya yake bashi a dole me mata yayi aure ya zama babba,Naila ta haye Saman gado tace to mufa yanzu sai an mana uzuri Kuma,Ikhy tana zaune ta Sha kyau cikin Abaya ta saka hula peach kalar Abayar,Naila tace ga tuwo me jego,Rafeeq yace Allah miki Albarka shi take nema yanzu ko? ya leka fuskar Ikhy,Arham yace mu gani da yawa?

Ya bude flask din ya Gani da yawa ya Kalli Basma yace ya miki? tace mu Gani miyar mece? ya bude Taga kubewa Danya tace an sa man shanu sabo da ni nafi so da man shanu,Kiyi manage haka ya dauki plate da spoon ya zuba mata tace yayi haka ma,Rafeeq ganin kanin su ne da matarsa kar su disga shi suka yi shuru, ya ishe ki? Rafeeq ya tambaya, tace ya isa haka,Naila tace Arham Ku na dafawa na me jego ne ai ka bari ta fara ci kawai Kai matarka ka sani.

Arham yace sai muyi zuciya mu fasa ci Dan kin samu ma za aci,faccalanci zaku nunawa matata wato ku kun hade Kai Yan gidan yari akan wani tuwo,to tayi girkinta sabo da zamu zo nace kar tayi tuwon za a samu a nan,kayan Rafeeq ko Spark kayana nane,Naila tace na shiga uku au haka ka fassara min magana,kana jinsa dai ko to ya Kalli Spark,Misam yace to ku yanzu mene haka akan tuwo,kema da ya eba sai ki kyale shi mene a tuwo baza ta iya cinyewa ba,Chika tace to daga ta danyi magana sai yace faccalanci muke idan yarinyar ta dauka fa a ranta,Rafeeq yace ku bar maganar dai,Arham taci tuwonta Ikhy Rafeeq ma ga tuwonta,Ikhy tace ni yayi min ma yawa,Dan uwarki haka zaki fada min in zage in miki kice ya miki yawa? Cewar Naila dariya Ikhy tayi tace sorry madam.
Spark kuwa baice kala ba,ko kulasu baiyi ba sabo da idan yayi magana zata ce ya tarewa Dan uwansa ko Arham yace ya tarewa Naila shi yasa bai ma yi magana ba.

Sai da Arham ya ajiye tuwon yace ga abinki nan Me jego taci lafiya,shi kanshi Arham ba a fada da shi bai ma da saurin fada kawai wannan lokacin ne shedan ya shiga tsakani,Spark ya Harare shi yace in zata ci taci abinta bana son iskanci,Kai baza ayi Maka magana ba,dauka kici tuwo,Basma ta dauka tace dama ni Ina so wai bazan ci ba ai ba Dani aka yi fadan ba ta dauki tuwonta.
Spark ya Kalli Naila yace daga yau me Kuma bana so Dan kinyi Abu wani zaici kice ba shi kika yiwa ba,koma waye ba sai Dan uwana ba in zai cinye du ya cinye,Naila kamar jira take sai Kuma ta rufe fuska da hannaye,shi Arham ma dariya abin ya bashi,yace kiyi hakuri Aunty Nailan mu,munafuki sai da ka hadani fada da mijina sannan kaji dadi sai yanzu zaka bani hakuri,sabo da kayi aure,da kullum kana gidana ba abinda bana yi Maka shine yanzu akan tuwo na danyi magana shine zaka nuna ma kamar ban taba kyautata Maka ba.

Arham yace to ni da kitchen ma nake shiga kice na ebi abinda nake so har kudi kike bani kiyi hakuri ban San ma me yasa naji haushi ba wlh,Misam yace ai yanzu malamar kuka ce Naila idan Hallare kike so akwai waje ga Kuma Oga kusa,Rafeeq tace wayyo ni maraya ta kare min,Dan Allah bakwa Jin tausayi na? Uban wa zai tausaya Maka? Inji Misam,Ikhy tana ta cin tuwonta,Rafeeq yace Ina cikin wani hali na shiga tangal tangal Kuma,Spark kayi hakuri zaka yi asara da yawa a Office don baza kaga dai dai ba babu harka ba aiki asara kawai kamfanin zai dinga yi,Spark yana can Nailansa na kuka hankalinsa ya tashi ya dauki waya Yana mata text na bada hakuri ko kula su Rafeeq baiyi ba,Yana tura sako Naila tana goge hawaye tana shesheka ta duba wayarta taga ya rubuta
Dan Allah kiyi hakuri kece da gaskiya ba Arham,Arham ya nuna Rashi tarbiyya a Nan,ya nuna gidansu ba home training,haba my Baby,Yar Abbanta
Sweety na Naila Hashim

Text ce ta biyu ta sake shugowa ta duba yace
Hawayenki tamkar ruwan zafi ne ke zuba a zuciya ta Dan Allah ki daina kukan nan my Heart,haba Ruhina Auntyn Hidaya da Zarah.

Naila aka gani tana duba waya tana faman zuba murmushi,kwanciya tayi a Saman bed din,ta juya tana facing din Spark,text ta tura Masa kazo ka share min hawayen to,Spark yaji kunya yanzu ya gama yi mata fada da muzurai sannan aga yazo Yana share mata hawaye ya nuna shike nan ba jajirtacce bane,Kallonsa tayi ta sake sabon kuka,ba shiri ya matso yace Arham Miko min tissue,suka kwashe Masa da dariya,Misam yace Dan iska kace baka ji Kai a dolo ka taba shiga Soja,na rantse da Allah nasan karya yake wannan fadan ai bazai iya ba,Spark yayi dariya yace Yan hassada,ya goge mata hawayen tas,Chika da Ikhy suna kallo suka ce ja zarenki Tantiriya,kina harka,Naila Bata kula su ba tace kayi hakuri idan na Maka laifi kaji,Misam yace ba sai kince ba ma ya hakura ai baya fushi dake,Arham yace tsumin kauye ce ai sai da aka hado ta tsaf aka kawota gidan,Rafeeq yace a dinga tausaya min Dan Allah ga Ikhy ta gashi ba damar Uhm uhm.
Spark ko kunya sai Lilita Naila yake.

Basma tace Aunty Naila Kinga dai rannan da kyar kika bani hakuri na hakura akan kyautar da mijina yayi min,to yanzu kinji an Kuma wata wai bazai bani ba Allah wannan karon bazan yarda ba,Rafeeq yace wacce kyauta ce? Arham da sauri ya toshe bakin Basma yace ba a fada,wlh dama nace na gaji da rufa maka asiri,Malama Ikhy tace dole na ganki Basma na jawo Aya na jawo hadisi,Arham yace yawwa Malama a taimakeni,sai Kuna janta a jiki,yarinya ce,Chika tace ke ba wani kyauta da za a baki ke baki San Kwalbewa bace suka sa Basma a gaba,wannan tace wannan tace.

Mima ce ta shugo da Maman Rafeeq da mata Yan barka,Mima tace ku kadai Kun cika daki,Shaheed ne ya shugo da junior tare da Mufee Amarya da Haly,Mima tace dalla ku tashi ku fita ku bawa mata waje,Kai Rafeeq kuyi waje.
Arham tashi maza ku koma daya palon,Rafeeq yace jikokin Zeenatu ne basa jin magana gado muka yi,Mima tace kasan Allah....tashi suka yi,ta Kalli Spark Yana gyarawa Naila hijab ta make hannunsa tace tashi idan ma da matan zaku tafi kuje,Arham yace to ku bamu danmu mu tafi dashi,Maman Rafeeq ce ta hayayyako Masa da masifa wannan yaron ni Sam ya fitar min Kai tunda rashin kunyarsa ta Kai karshe,Zeenatu wasa ce? Jikan Zeenatu ne fa cewar Misam,suna fita aka bar su Mima mata suna ta shugowa barka.

Tunda aka yi haihuwar kullum su Naila suna hanya har aka yi suna yaro yaci Suna Abdallah,Yan uwan Ikhy da matan Yahuza sunzo,Haidar ma yazo da gift,Ikhy ta Sha kyauta.

Sati biyu da haihuwar Ikhy, Chika cikin dare ta kasa kwanciya,ta kasa zaune ta ka kasa tsaye,tun tana daurewa tace Misam ka tashi mu tafi asibiti wlh bayana Marata,bayana zai tsage, wayyoooo Babana,kafin ya shirya su tafi ya dakko tarkacen haihuwar da ta hada har ta fara ihun kuka,Chika da bata da raki bata da saurin kuka amma ta fara sheka kuka ,gidansu ya kira matar Marikinsa ya kira Mima ya fada mata,suka tafi asibiti a can su Mima suka same su,a daren ana zuwa Chika ta haihu Bata yi doguwar nakuda ba sai kukan tsiya,ta haifi yarta mace santaleliyar gaske.
Sai washe gari da safe aka sallami Chika.

Beauty kuwa Mohsin Bai fada mata zai dawo ba amma ya fadawa Abba,yace kar ya fada mata,amma Abba ya shugo gidan sai da yaga Beauty ya dauki jariri yace an fada min wata magana ance kar na fada inji mijinki,Kamar na fada kamar kar na fada,Kubra tace ka fadi me? Dan Allah kazo dama Ina son magana da Kai duk wai Dan kar ya fada ta janye shi,da kyar aka samu Mohsin ya dawo Abba Bai fada ba sai Jin Sallamarsa aka yi da yamma Umma Kubra ta dakko Danta a airport cikin sabuwar motar Abba, Beauty murna kamar me amma a gidan sirikai ne wani abin ba dama,sai kallon juna suke ita da Mohsin kamar zasu cinye juna,suna magana da Ido,yaga ta Sha kyau,Abba yace mutanen Makkah dama yau suka je aka gyara ko Ina na gidanku gashi kayanta ko kunya duk ta kwashe ta Maida gidanku tana sa rai miji ya kusa dawowa sai ku tafi gidanku ai,dama haka ta dinga tafiya gyaran jiki duk sabo da Kai ake yi na sani,shuru nayi kawai ban nuna ma nasan Dan Kai ake yi ba,ta zaci wai ta kife ni,yau mun huta muma zan samu tattalin arzikina ya dawo,Mohsin yayi dariya ya zauna sun dade suna hira,sannan yaci abinci yayi Sallah,Kubra tace ga key din motarka normal an mata komai,ya karba,Abba yace ya labarin su kubri (Saman gada) da su dukkani(Kanti)? ya ka gane min idon takari a can ana korar su suna likewa?
Mohsin yayi dariya sosai yace suna can Abba,yace ya Darul tauhid ka ga Darul Salam a Madina ko? ai Yan biyu ne Hotel din,ya su bakiya anje ziyara? Mohsin shi dai Yana ta dariya Abba a dole yasan ko Ina,shi burin Mohsin a tafi gida ya gana da matarsa da dansa,Amal taga Abbanta sai murna take dama taje hutu wajen Hanan mamanta

Ranar Sunan Beauty yazo dai dai da auren Mufee da Haidar shagali kan shagali,Haidar yayi lefe na gani na fada.
Maryam kuwa kanwar Annoor sai da ta Sha jinya me tsanani ta fita a hayyacinta sannan ta warke a hankali,taci bakar wahala,maganin duniya yaki yi mata aiki.
Bayan ta warke a rame a kekashe tazo gidan Annoor suna Parlo suna kallon film ta shugo tare da zubewa a kasa ta fashe da kuka tana rokon gafara,Annoor Sam bai gane ta ba sai da tace Maryam ce Yaya baka gane ni ba,Annoor ya daka tsalle ya koma gefe Jikin Iman ya makale yace kece Maryam? tana hawaye tace nice,yace Allahu Akbar ko Dan wannan halin da kike ciki ai a yafe miki,na yafe miki,Iman tace ke kuwa ba Kya iya cin abinci haka? Sweet ka ganta sai hakoran kawai,skeleton a fili mun yafe miki duniya da lahira,tace na gode Allah ya saka da Alkhairi,yace Ameen ki daina fitowa haka ki boye kanki ki bari sai kin murmure Allah ya Baki lafiya jeki zamu zo gidan tace to ta mike iska na ibanta,yace zauna ki huta,Iman tace to Kinga dai duniya sai kiyi darasi,taje ta kawo mota abin ci da Sha,taci kadan,Annoor yace in zaki kici ki ci Nan ba wajen kunya bane
Sai da ta gama tace zata tafi,ta fita waje Wanda dama driver ne ya kawota shi ya Maida ta tana Jin dadi sun yafe mata.

Mero taji jiki tace yau sai dai a dauke ni yau ma ,ka gama ragargaza ni,yau na Sha wahala,yace sorry My Angel bari muyi wanka,Mero tace ka fara dai bani ragowar kaza ta naci da tea me zafi hadin Madara,dariya yayi ya mike ya kawo mata abinda ta bukata,ya shiga bata a baki tana korawa da shayi me kauri,gobe Kuma sai naci tsire, idan Allah ya amince jibi Kuma sai a siyo min nama me ruwa ruwa Shima ya Sha cabbage,Haneef yayi dariya yace za a siyo inshaallah,tace ya zama wajibi da yardar Allah,irin wannan wahala da naci ai sai da sinadari me kyau in ba haka ba sai na fara hakoran gaba,yau da kyar zanyi fitsari an min kaciya,Haneef Yana dariya a nutse yana bata tana lamushewa.



Ayi hakuri da wannan naje wajen aiki ne.




AsmaBaffa
[3/9, 9:21 AM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

BOOK 3
~TAIMAKO~


81-85


Official

By
AsmaBaffa


SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM


PAGE NAKI NE
Yar Gatan Annabi



Mohsin tun a mota Beauty take Masa korafi yanzu da ba'a gyara gidan ba fa? ai sai ka fada min,ni naga Umma tace Inzo muyi girki ana ta shirya girki na musamman Ina ta mamaki Ashe Kaine zaka dawo,surprise na miki, a'a ni bana so wlh ka daina min haka,sai da ya shiga gidan da motarsa ya rufe gate zata fito yace ki zamanki a mota a ciki zan bare sabuwar Amarya ta,Beauty tace ikon Allah mutum da bedroom da komai sai kace Yan iska,yace ba wani nan na gaji kullum Abu a daki,daga bedroom,Palo,toilet shike nan fa ai a dinga samun canji,yanzu wasu ma'auratan a duniya tunda aka aure su a waje Daya suke Abu daya,wasu basu taba barin bedroom ba,kullum a waje daya ba chanji,ai yanzu ma zamu fara yawace yawacen mu gari gari ko ba kudin fita waje ko su Lagos ai ma dinga zuwa,ga su Kwara state mu kwara kauna a can,Beauty tayi dariya yace ai kune wasu mata bama Kwa so a fita da ku,mijinki Yana da Dan budi ko katsina ai Kwaje kawai aci Aya ayi kauna,Beauty tace ai ni kasan ko nan da inane zanje indai da Kai,suka ajiye Baby a gaban mota suka shige bayan mota kamar Yan iska mota sai Lilo take a compound suna Kwalbewa.

Ranar Sunan Chika Yana zuwa yarta taci Suna Nasreen,an Sha suna anyi shagali.
Naila ana kan gaba har da wani Dj suka kawo sabo da bikin Mufee da Haidar, Iyalan Jauro Maza Abuja suka taho daurin aure,abokan Ango,Mohsin da Abba duk sun zo,Naila tayi tayi su Abba su kwana sun ki,Mohsin ya kawo mata tsaraba sosai,Chika ma an bata da Ikhy Abaya,harda kawowa Spark jallabiya kala biyu masu tsadar gaske fara da coffee color da turare me kyau.
Washe gari aka Kai Amarya Mufee hadadden gidanta kusa da su Iman abinsu sharr, su Iman sune masu tabbar Amarya gaba dayansu yara da su,bayan mutane sun watse Haidar Allah Allah yake ya fada dakin Amaryarsa,ga Mufee Jinin su Zeenatu ba wata kunya ce da ita ba,tayi tunanin wani dadi ne da first night din.
Sai da Haidar yazo suka gabatar da duk wani abubuwa na farkon aure sannan ya goge mata hadda gaba daya,Yar rashin kunyarta data kwaso daga Abuja duk ta Maida abarta cikinta ta hadiye,sai dai bata Sha wahala irin wasu ba,ba yanda ake tsammani ba,washe gari ma da kanta tayi komai tayi girki abinta,Mufee an dage an koyi girki kafin aure,Haidar har wani Santi yake yace daga Jin wannan girkin na tsohon hannu ne tun kina karama kike koyon girki? Mufee ta shararo karya tace ai mu tun muna Yan yara Mima take siyo mana Yan tukwane na yara muna gwada girki,tun muna yin na wasa har muzo ta kaimu kitchen,tana nuna mana zuba Maggi kaza,zuba curry,zuba gishiri kamar haka"a haka har a fara barin mu muna girki da kanmu abinmu.
Haidar Yana Jin dadi Yana washe baki yace ai da gani Kun samu tarbiyya sosai,haka ake son iyaye,Mufee tayi dariya a ranta tace shiryuwa kawai muka yi muka ga rayuwa haka baza ta kaimu ko Ina ba muka canja,a fili Kuma tace gaskiya sai dai mu godewa Iyayenmu,Haidar yace bazan taba godewa nawa ba sai dai Kawu Jauro da Umma Habiba,suyi min laifi na gode musu a wanne dalili,Ina dai ganin girman su Ina mutunta su a matsayinsu na iyaye,Kuma bazan yarda wani ya wulakanta su ba amma na gode musu akan me,me suka yi na bajinta a kaina, Allah ya kyauta dai,Mufee tace Ameen ai ba laifin mama,yace

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login