Showing 162001 words to 165000 words out of 236322 words

Chapter 55 - Gidanmu Book 1 & 2 Complete Hausa Novel

Janafty   

28 Oct 2025

752

zaki ce wani nine..?
Inteesar najan majina kamar gaske tace"To ba kai bane..Kana Ta Fushi dani nayi ta kiranka baka Dauka ba na Tura maka sako ba adadi kaki kulani kuma..kuma!
Tafada fada tana wani kara Goge Hanci kamar kuka Dariya ta kamasa ya kanne kafin yace"Ina jinki..kuma me..? Imran sarkin Laifi..?
Inteesar Da ta Fakaici idonta ta Debi Miyau ta goga i donta saboda yaga da gaske take tunda na gasken yaki zuwa batasan yana kallonta ba Dariya ta kusa Subucemai acikin Ransa yace"Yaro yaro ne..Yaro man kaza..!
Cikin Shagwabbiyar Muryanta tace"Kuma baka bari ina ganinka kafin na fito ka tafi aiki in kuma ka dawo da Daddare ne kana cikin Dakinka ni fa kuma na baka Hakuri kaki Hakura..?
Yana Mirmishin Saman baki yace"Au ai kin gama naki Fushin ne ni na Dauka ba shikenan ba..?
Fito da idonta yaga Hawayenta Tace"Ai nace kayi Hakuri fa..!
Tafada Tana kara Tura baki Yana Danne Dariyansa yace"Ok naji..Yanzu kin Hakuran ne na Rika zuwa Wajen Sajidan..?
Kallonsa Tayi kyam Ranta Tuni ya Baci Mood dinta ya Sauya kanta ta Kauda gefe ta Murgudamai baki ya ganta Sarai shiyasa ya Hade rai yana Fadin"In kika kara Juyamin baki sai na Bike Bakin yayi jini..? Am i ur Mate..? Saboda kinga ina Miki Dariya shiyasa Kika Rainani ko..?
Tana shirin mgana ya Dakatar da ita da cewa"bana son jin Wata mgana..Bana son Raini ni bana daga Ciki yayyinki wadanda kike rainawa kina ma Sangarta yadda kikaga Dama Ina nan a Imran din da kika sani Wlh ban Sauya ba u better Behave ur Self kuma ma naje wajen Sajidan ke kin isa ki Hanani ne..!ke ce zaki bani Umarni ko ni ne zan baki..?
Baibata Zarafin mgana ba ya cigaba da Fadin"Ni namiji ne Mijin Mace Hudu..Zan iya auran mata uku nan gaba Bayan Sajida kuma infact ma ke Matatace da zaki hanani zuwa wajen wata..?
Yafada yana kallonta Saurin Sadda kanta tayi kafin Cikin cikin Sanyinta Idanuwwnta sun ciko da Hawayen gaskiya"Kayi hakuri bazan kara ba..!
Sai ta bashi Tsausayi wani abu na yawo acikin Ransa kai ya kauda yana Fadin"Is ok..Tunda kin bani Hakuri nima na Janye Fushin..!
Kallonsa ta dago tanayi ido Cikin ido Hawayen kishin Sajida suka Zubo mata Karamar Dariya yana Duba agogon Dake Daure a tsitsiyan Hannunsa yace'"Sai yanzu kukan gasken yazo..?bakya Bukatar saka Miyau bakin kii ko..?
Kunya ta kamata ta Rufe Baki Tana yar Dariya Cikin shagwaba tace"Duk ba kai bane..!
Nishadinsa ya kasa Boyuwa yace"Ni kuma..?laifi na baya karewa..Kedai Kazama ce kawai..!
Yafada yana yar Dariya ganin Zata faramai shagwabanta ne ya nuna mata agogon Hannunsa yana Fadin"8am na kusa..Kada ki sakani na Fara abunda ban saba ba plz ki goge wannan Hawayen naki ki koma gida Zamu hadu in na Dawo wajen aiki..!
Kallonsa Tayi kafin tace"alkawari..!
Tare da Mikamai karamin yatsaanta bai Rike ba yadai murmusa yace"Cikawa..!
Sai Lokacin Hankalinta ya kwanta ta Share Hawayenta ta Bude Motar ta Fito Lokaci Daya tana Rufomai Murfin Motar,Tana Tsaye a wajen Tana Dagamai Hannu har yayi Hon iro megadi ya Budemai get ya Sulala Waje,sannan ta koma Cikin Gida Cike da Wani Farinciki Tana shiga Falon Taga Ya yusuf da Anty Safiya suna karyawa Gaishesu tayi kafin ta shige ciki Anty Safiya na mata mganar Karyawa tace sai tayi wanka Lokacin Munari ta Farka Daga Barci in bata Farka ba ita zata tasheta.

*****

Shikenan Fada tsakanin Inteesar da Imu ya kare suka koma kamar baya Yawancin sunfi mgana ta Test Messages,Tunda bai da wani ishashen Lokaci,waya sai Lokaci bayan Lokaci in Bukatar hakan ta taso.
Suna Haduwa yawanci a Haraban gidan ko kuma aa kitchen in yaje Daukan Ruwa ko Zai Hada Tea ko Zai Dibi abinci Wani Lokacin kuma yanzu in yana Daki yana Bukatar wani Abu ita yake kira takaimai.
Koda basu yi wata mgana ba They are ok Tunda suna ganin juna Koda yaushe sun dai yima Mama yaji sai dai suje da wuni badai da kwana ba Tuni Inteesar ta kusa kwshe kayanta Duka Zuwa Gidan Abba Mama bata isa ta Raba Kaunar Munari da Inteesar ba,Shiyasa bata Damu ba Tunda suna kusa kuma nan din ma Gida ne ba wanda ya kawo wani abu sai Munari Domin ita tasan komai Abba bai Fara zuwa Offife ba sai Farkon Wata Lokacin komai ya Daidata Harta Motar da sukayi Shawara da Imu zasu siya ma Abba da Sauran kudinsa da na Marigayi Nura zasu siyama Abba Mota mai rai da lafiya da Direban da zai Rika jansa batare da sun Fadamai ba sun fi so yaga komai kwatsam
Karshen Wata nayi Daada ta Kira Duka ya"yanta ta Fada musu tana son ganinsu bazata mtsa sai da ya"yansu ba ammh wanda ke da Hali yazo,ta kuma ce Mami Tazo da Sajida Khamis yazo,Imran Daman suna Waya daya Kirata ta gayamai daman Wannan Lokacin yake jira ya shirya ma Hakan

Mami Asma"u dataji labarin Ta Dauka mganar Khamis ne da Tarewar Sajida Lalle Lokaci yayi da zata Tauna aya Domin tsakuwa taji Tsoro sai Imran ya Raina kansa Sajida na makaranta Baffa ya Kirata yace in ba mtsala tazo Gida zasu da ita Dukku ne Daada tace taje,Tana jin haka bata tsaya wasa ba Ta Tattaro ta dawo gida Daman Damar nan take jira Tunaninta itama ya Tafi kan mganarta da Imran Allah yasa mganar Biki ne da Tarewa da sai tafi kowa Murna.
Su Inteesar dai zasu fara Test Monday sukace bassu je ba,su aka bari agida Da Anty Safiya su Sadam su kadai suka Tafi sun bar iyalansu agida.
Ranar Jumma"a Abba da Ya Yusuf da Sadam suka tafi a Motar yusuf din Imu yana Wajen aiki yace sai asabar da Safe zai taho
Baffa Kabiru ma sai Ranar asabar yace zasu zo su Daddy ne chan su Abba suka iske su shi da Umma da Basheer Inna Bintalo ta iso ita da Inna Maimunatu wannan karan ba yaran kowacce ita kadai tazo,Sa"id ma Aranar da Daddare ya iso Daga Dutse.
Imran sai Ranar asabar da Safe shida Sagir suka hau Motar Haya zuwa Dukku agida ya bar Motarsa








*Shakira*
3/23/22, 12:02 - Ummi Tandama???i: *GMB2??T??15*


*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Basu isa da wuri ba,Sai wajen 12pm na rana duk da sun fito da wuri,Sagir dai nashi dan bi ne domin baima san da Tafiyar ba,ana gobe Tafiyar ya kirasa a waya yace mai ya shirya gobe Zasu tafi Dukku ya zata ma amotarsa Zasu tafi Imran din yace A"a saboda bai wani san hanya ba Yusuf ne yasan Hanyar sosai,infact ma bai yi niyyar zuwa da Motar tasa ba.
Sagir kallon Imran kawai yake Ko da bai gayamai komai irin Mirmishin Dayake ta saki na kasan Lebe yasan na mugunta ne irin Mirmishin Imran naci Nasara shifa Bai taba ganin mutum mai sa"a kamar Imran ba Komai ya sama gaba sai yaga bayansa komai yace zai yi to tabbas Zai yi ne yana da kyawawan Halayya da ba kowa ke sanin haka ba sai kana Tare dashi,Mashin dinsa Halak malak ya mallakamai Sagir din Saboda ai ya Chanchanta shi Sagir din ma yaki amsa Daga Farko Imran din ya wurgeshi da key din yace in bayaso to ya Bada ita yadai san In Imran ya Fadi mgana baya sauya mgana Mashin dai ta Zama nashi sai dai shi yayi abunda yaga Dama da ita.
Koda suka isa Tuni bakin Abuja sun iso,Hatta Khamis ya iso,Daman jiya da Daddare ya sauka a Abuja da Safe suka kamo Hanya Harda Sajida Umaima Tana gida Saboda makaranta.
Imran bai yi wata Shiga ba kamar yadda ya saba haka yayi sanye yake da Riga da wando,Rigar mai ruwan kasa ce Mai Hasken wandon kuma Shima mai ruwan kasa ne sai dai yana Duhu sosai,Wando daga kasa ya Tsuke kadan Ya kamasa.
Sun shigo Har falon Daada inda su Umma ke Zaune ita da Mami Asma"u da su Sajida dasu Sa"id da Basheer,Su Abba suna Dakin Daada tun da suka Shigo Sajida idanuwa??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????nta suka Kafe akanshi shi Wlh bai ma ganta ba yaga dai Uwarta wacce ko kallo bata isheshi ba Umma kadai ya gaisar Kadahan kadahan,Sai ya karisa wajen su Ya Yusuf suka gaisawa ta Hanyar yin Musabaha,Abun mamaki Da kansa yau ya mikama Khamis hannu suka Gaisa suna kallon Juna ido Cikin ido.
Imran kallon kayi kadan yake yi ma Imran irin na Riga na gama Dakai shi kuma Khamis Kallon Au ka Tuba ne..?Irin dai dole dai ka dawo Hanya yaro.
Daganan Dakin Daada ya Shiga ya gaida su Abba,Da Daddy sai Inna Maimunatu,Yana kallon Goggo Bintalo da Baffa Kabiru yaki gaishesu da Abba yayi mgana sai yayi Shuru ciki Ciki ya gaishesu kamar bai ganesu ba,Abun yayi ma Inna Bintalo Ciwo sai dai bata mgantu ba Kada yaron ya Zageta tasan Tsab zai iya Tunda bai da kunya,Baffa Kabiru kam bai Damu ba Domin yasan Daman yaron baya Darajasa kuma bai Dauke sa a Uba ba.
Dakin da suka sauka wanchan karon nan suka kara sauka shi da Sagir wanka Imu yayi ya sauya kaya saboda yana jin Zafi,yazo da karamar Laptop dinsa saboda aiki akwai aikin da Wani Ma"ikacin su zai turo mai Daga gyagyadi branch yau din so yana Bukatar ya Duba shiyasa yazo dashi Wayarsa ya Dauko domin yaji karan Shigowar sako Kamar yadda Ya zata Intee ce.
Tana Tambayansa ko sun issa Lafiya ya Tura mata da cewa eh suna Dukku,Daga haka ya maida wayarsa aljihu,agogon Tsitsiyan hannunsa ya Duba yaga lokacin Sallah ya kusa Daman ya Dauro alwala cema Sagir yayi alwala su tafi masallaci ba Musu ya tashi yaje yayi alwala suka Fita Tare koda suka fita duka mazan suna Waje suna alwala har da su Abba ya Hadu da Mami Asma"u a Falo bai ko kalli barayinta ba,Dariya yake cikin Ransa Domin har yana Hango irin yadda Zatayi in taji Hukunci da ya yanke akanta da ita da yarta.
Gabadayansu suka Dumguma zuwa masallaci sai da suka Tsaya aka Tada sallar tunda sunje da wuri bayan sun idar suka nufo gida.
Imran da shi da Sagir suna Baya sai Daga baya suka Shigo gidan Tun Daga Nesa ya Hango Sajida Tana Tsaye ko da bai sani ba yana da Tabbaci shi take jira zatayi mgana dashi Sanye take da wani material mai Santsi Dingin Doguwar riga ta yane kanta da karamin Bakim Vail kafarta Cikin takalmi baki sawu ciki a Fuskarta ta Rame sosai Idanuwanta duk sun Sauya Launi
Sagir na ganinta ya Zunguri Imran yana Fadin"Ga Amaryan ka nan..!
Ko kallonsa Imran bai yi ba sai ma kara Tamke Fuska da yayi kamar bai Taba Dariya ba Har suka kariso kusa da ita Sagir na Shirin Dakatawa Imran ya wuce Kamar ma bai ganta ba ganin haka yasa Sajidan da gabanta ke Fadi Saboda yadda Imran din yayi mata Kwarjini tace"ina yini..!
Imran yajita ammh yayi kamar bai jita ba ya cigaba da Tafiyarsa Sagir Daya ga haka ya Daga Murya yana Fadin"Imu tana gaisheka fa..Don Allah ka Tssya..!
Da kamar bazai Tsaya sai Wata Zuciyar tace ka Tsaya ai ba wani Sauran Rina Dake Tsakaninku.
Cak ya Tsaya Lokaci Daya yana juyowa Hannuwansa ya Haarde Saman Kirjinsa yana kallon Sagir irin gashi na Tsaya sai yaya..?
Sagir ne ganin haka yasa ya Kalli Sajida da kanta ke kasa jikinta ma ya fara rawa tana ta wasa da Kwalliyar Jikin Rigarta.
Ya sanyaya Murya yarinyar ta bashi Tsausayi saboda yasan wacce Zata iya gaba da gaba da Imu ba karamar Jaruma bace
Yace"Ki je ki sameshi in ba haka ba zai Tafi abunsa..!
Daga haka ya wuceta da sauri kusa da Imran ya karisa daidai kunnensa yayi mai Rada"Plz ka saki Ranka She is ur Wife..!
Sanda Sagir ya fadi haka sai yaji kamar ya Mangaresa da mari,sai kuma yayi Fuska kawai ya kara Hade rai ko kadan ba annuri ballatana Samun sukuni agame dashi Sagir dai Ciki ya shige yana Fatan kada Allah yasa Imran ya zabgama yarinyar nan Rashin Mutumcinsa.
Gajiya yayi da tsayuwa ganin Ta na nan Tsaye bata ma tako ba,juyawa yayi niyyar tafiya sai gata ta kariso Salau Salau kamar mara kuzari aransa yace ji ta kamar wata ta Allah.
Kanta na kasa bata son Hada ido dashi Tace"Ina yini..!
Tafada Lokaci Daya gabanta na Faduwa,Saboda bata son kallonsa kwayan idonsa yana bata tsoro matuka yana saka taji duk wani Comfident dinta ya tafi indai tana gabansa gabanta sai Fadi yake in da Zai lura har rawan jiki dana Baki take yi alokaci Daya.
Kallonta yake Daga sama Har kasa so yayi ya sakin mata Tsaki sai kuma ya fasa cikin Dauke kai da Dakuna Fuska yace"Lafiya..!
Yafada yana kallon Fuskarta acikin Ransa yace irin Fuskar uwarta ya"yan nagada ba na haya ba.
Gajiya yayi da tsayuwa yasa yace"Ammh kinsan dai ba wasa tsakanina Dake da zaki Tsaidani ki tasani agaba kuma kiki mgana ko..?
Yafada cikin Kaushinsa kamar ko yaushe.
Jim haka yasa ta kara Sadda kanta Tana Fadin"Dama..Dama!
Wani Haushi ya kamashi yace"Dama What..?ke kinga ni ina da abunyi yanzuma Da kika ga na Tsaya Wlh ba wai domin darajanki bane ke har kin Isa..? Ba macen data isa ta sani ni Imran nayi abunda ban yi niyya ba Darajan Abokina kikaci..So in baki da Fada on my..!
Bata bari ya karisa ba,Tunda taji mganarsa Cikin Kaushinsa kafin tace"Dama ina ta Kiranka a waya ne baka Dauka ba Daga baya kuma sai na Daina Samun ka..!
Karamin Tsaki yaja kai Tsaye yace"Nayi Blooking dinki ne..!
Batasan Sadda ta Dago rinannun Idanuwanta Tana kallonsa ba Cikin mamakin kalamansa Duk da tasan dai Ya kulleta ne ammh bata Zata zai iya gayamata haka ido Cikin ido ba.
Ganin irin kallon Datake yimai ne yasa ya Daga mata gira guda Daya yana Fadin"Yes..Saboda bana son Wata mu"amala ta shiga Tsakanina Dake Infact ma bamu da wata alaqa..!
Bai bata Zarafin mgana ba ya cigaba da Fadin"Nasan zuciyarki na Fada miki ba an Daura mana aure ba..? Auran Dan iska dan Shaye shaye bai Dace da Sajida Kabir Dukku ba Diyar Lauyoyi jikar Lauyoyi Diyar na gada ba na Haya ba..To u better wake up..kinga kuwa ni ban Dace dake ba..Ke ba Matata bace bamu da wata akala!
Gabadaya kalamansa sun rikitata Bata san Sadda ta dago kanta Tana kallonsa ba sanda yace ita ba Matarsa bace Kara Dakuna Fuska yayi kafin yace"Eh nace bamu da akala ko muna Dashi ne? Nasan zaki ce to ko ba aure ai ni yar"uwarka ce u ara mad in kikayi Tunanin haka akaina ni Imran Wlh wanda keyi dani sai ma naga Dama Zanyi Dashi acikin Dangi ballatana Wanda basan da wanzuwarsu ba So plz and plz ki Rabu dani kada ki kara Kirana am not ur mate kada ki kara Kirana In baka ba Haka zaki san Oder Side dina!
Tsaki yaja mai karfi yana Fadin"Rubbiish kawai..!
Daga haka ya juya ya shige cikin Gida,da kallo ta Bisa Hawayen da suka cika mata ido suka zubo mata masu Zafi da Tsananin kaunar Imran Kuka Take so ta fashe dashi ammh Zuciyarta ta Chuse waje Daya Meyasa yace ita ba Matarsa bace ko ya saketa ne?
Saurin dafe kanta Tayi jin ya sara mata da wannan Karamin Tunanin a Fili ta Furta"A"a bazai taba sakina ba..Bazai sakeni ba bazai sabama mganar Baffa data Daada ba..Wlh ina sonsa inajin kamar in na Rasashi Zam iya Mutuwa..!
Take Fada tana Sharan Hawayenta kamar Wata Tattabiya soyyaya Ta sakata Zatayi hauka kafin ta Dibi Sauri Zuwa Cikin Gida.
Tana shiga Taga ana ta cin Abinci Mami Asma"u dake Faman nemanta ta Tsareta da ido Cikin Tuhuma Tana fadin"Ina kika shiga Tun dazu..!?
Cikin kame kame tace"Na fita amsa waya ne Mami..!
Tafada Tana kallon Imran Dake kusa da Yusuf suna cin Alalan da Baba asabe Tayi a Filet Daya,Ko barayin Datake bai kallah ba kansa na kasa ya bada natsuwasan kan abun ke gabansa.
Hararanta Mami Asma"u tayi Tana Fadin"Waya ko..? Ita kuma wannan ta waye..?
Tafada Tana Daga mata wayarta da ta barta gefen Mami Asma"u din bata sani ba.
Kanta ta Sadda kasa batace komai ba Hankalin kowa baya kansu Ba wanda ma yabi ta kansu su Abba suna Dakin Daada achan suke cin nasu abincin.
Mami Asma"u kure Sajida da ido take yi,Tana Nazarin wani abu acikin Ranta Taga shigowar Imran kuma ba Dadewa Taga Sajida ta shigo Allah yasa ba ajinta ta Zubar taje tayi mai mgana ba in ko hakane da sai taci Uban Sajida in ta kuskura tayi mata wannan Shirmen.
Abinci tace tazo taci bata cikin good Mood yasa tace bazata ci ba wucewarta Tayi Dakin da suka Sauka ita da Mami Asma"u ranta duk ba Dadi Mami Asma"u ta bita da wani kallon yarinyar nan Tana Hauka ne..?
Ba a dauki Lokaci ba kowa ya gama cin Abincinsa nan mazan suka Zauna suna Hirarsu Imu ma na cikin su sai dai baya mgana Sai dai yana jinsu kawai in abun mgana ce aka Sako sa sai da ya gyada kai ko ya Rage Daure Fuskar Wayace a hannunsa Mgana suke da Intee Tana mai shagwaban gida ba kowa duk ba Dadi tana Missing dinsa,Sakar mai da kasala Take duk da ba Waya suke ba Massages ne bai biye mata yace ta wuce taje ta Dauki Littafanta Tafara Karatu baya son Shirme.
Suna nan Zaune sai ga su Abba sun Fito Dukkansu sun taso Tsohuwa Daada agaba Tana Tafe sanye da Hijabi mai ruwan kasa,Bai da Tsawo sosai Carbi ne a Hannunta tana ja Inna Bintalo da Inna Maimuna suna Kafada kafada da ita sun sakata a Tsakiya.
Kan kujera suka Taimaka mata ta Zauna Gabadayansu suka Zauna a kasa Umma Dake saman kujera ta Sauko ta zauna akasa,Daman Mazan duk suna Malale zaune ne saman Cafet din Daya malale Falon.
Mami Asma"u dai Bata sauko ba sai ma kara gyara Zama datayi akan kujeran ta kara gyara Zaman Siririn Gilashin Dake idanuwamta Khamis na gefenta a kasa yazauna wajen Kafafunta.
Tuni Falom yayi Tsit sai Sautim Muryoyin su Sa"id da suke ma Daada Barka da Fitowa amsawa take cikin kulawa,Tana Bin Kowa da kallo Daya bayan Daya sai ta sauke kallonta kan Mami Asma"u wani abu na cin Ranta Uhm Lokaci yayi da Asma"u zata gane Kuskuranta Juyawa tayi Tana kallon Baffa Kabiru kafin tace"Ina Sajida..?banganta ba ko bada ita kuka zo ba..?
Kai ya girgiza mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login