Showing 39001 words to 42000 words out of 223329 words
ita kaɗai tasan yanda takeji a ranta akan wannan al'amari mai rikitarwa da matuƙar ruɗani. Tunda take bata taɓajin labari irin nataba. Tayaya zaka haifi ɗa na mutum batare da kasan yanda ka samu cikinsa ba. Anya kuwa yaron nan baɗan wani aljanin baneba?......
Shigowar Alhaji da Maman Sadiq da gayyar yaran gidan gaba ɗaya har da ƴaƴan Maman Sakina ya katse mata tunani. A take kuma ɗakin ya kaure da hayaniyar yaran. Dan bayan sun mata yaya jiki gaba ɗaya hankalinsu suka maida ga ɗan jinjirin suna yaba ƙyawun da ALLAH yay masa. Sai da Maman Halima taga kukansa na ƙara ƙarfine ta amsheshi cikin tilastawa suka saka Zinneerah bashi abincinsa tanata kuka.
Alhaji da Maman Sadiq ne kawai suka iya fahimtar kukan Zinneerah saboda sune sukasan labarin tushen samuwar yaron. Dan ita kanta maman Sadiq konawarsu gida tasha kuka, a yanzu hakanma kukan zuci takeyi. Su Maman Halima kuwa da basusan dawan garinba sai tunaninsu ke basu Zinneerah tana kukane saboda tunawa da mahaifin yaron da akace rasuwa yayi.
Da ƙyar aka samu ta bari yaɗan kama na wasu mintuna. Dan kuka take sosai tana yarfa hannu wai zafi. Maman Halima ta ɗaukesa tana mata faɗa akan karta sakama ranta fargabar tsotso dan yaron nan daga gani ba wasa zaiyi da cikinsaba. Ita dai Zinneerah zamewa ma tai ta kwanta a hankali tana matse baki dan inda aka yankata na mata ciwo sosai har yanzun.
Sun daɗe a asibitin yaran na cigaba da jagwalgwala yaron da aka samu yay shiru, yayinda Zinneerah ke kwance shiru bata sake kula kowa ba. Idonta a lumshe suke tana zirar da hawaye ta gefensu, yayinda hancinta ke shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren dake manne da jikin showal ɗin yaron da batan a ina ya kwasoshi ba.
Ƴar hayaniyar yarance ta saka Doctor shigowa ɗakin yace suyi haƙuri a barta ta huta hakanan, ya kuma bada damar a bata abu mara nauyi tasha, kamar shayi ko kunu haka. Godiya sukai masa ya fice. Alhaji kuma ya tattara iyalansa shima sukai musu sai da safe suka tafi. Aka barta daga ita sai Maman Halina dake haɗa mata kunun da akace zata iya sha ɗin.
_____________★
Haka Zinneerah ta cigaba da jiyya a asibiti. yayinda abokan arziƙin Maman Sadiq na anguwa da dangi ɗai-ɗai dake anan suke ɗan shigowa dubata. Kulawa da take samu na abinci ya saka komai yake tafiya kan tsari Alhmdllh. Dan jikinta yayi ƙyau sosai a kwanki shidan data ɗauka a asibitin. Idanma ba'a faɗa makaba bazaka taɓa ɗauka cs akai mataba. Sai dai sam babu mai ganin walwalarta, sannan ko kallo yaron bai ishetaba sai Maman Halima ta mata jan ido.
Matsalar da suke fuskanta da yaron kawai shine idan yasha nono cikinsa sai ya kumbura yayta kuka. Da farko basu fahimci hakanba sai suke ɗauka cibiyarsa ne ke ciwon. Sai daga baya Doctor ya gane inda matsalar take. Dan haka ya dakatar da Zinneerah daga bama yaron nonon gudun kar a cutar da yaron kuma. Sai dai sun ɗorata akan magani zuwa wani lokaci sai ta cigaba da shayar da shi. shi kuma yaron suka bada shawarar a ringa bashi madara.
Hakan yama Zinneerah daɗi, dan a shirementa ayyanawa take a ranta ta huta da ciyar da ɗan aljanu, dan har cikin ranta ta yarda aljanune sukai mata ajiyar yaron kawai a cikinta.
Babu wanda yasan da wannan shirmen nata, sai dai ranar tsabar jin daɗi har ɗan sakin jikinta tai sukai hira da Maman halima da ada take danganta rashin walwalar Zinneerah ɗin da rashin ƙarfin jiki.
Washe gari Alhaji ya sayi raguna biyu aka raɗama yaro suna Abdul-Mutallaf a masallaci, wato dai takwaran AK Shira kenan kamar yanda akai masa huɗuba. Ba ayi wani shagaliba kasancewar mai jego na asibiti, sai dai maman Sadiq tayi abinci ta bada sadaka ko zata samu sassauci a ranta da nutsuwar rugumar wannan ƙaddara a garesu.
Da yamma da sukazo dubasu a asibiti Alhaji yake sanarma Maman Halima cewar yaro yaci suna Abdul-Mutallaf.
Cike da murnarta da farinciki taita jera addu'a ga jariri tana tsokanarsa. Zinneerah kam ko motsi bataiba balle ta nuna taji sunan da yaron yaci. Sai dai tausayinsu da takeyi akan sunatama ɗan aljanu hidima batare da sun saniba. Ta tabbata wataran sai aljanin daya ajiye mata ɗan yazo ya ɗauke ɗansa batarema dasun saniba zasu gane wahalar banza sukayi. Babu wanda ya damu da rashin tankawar tata. Garama maman halima taɗan mata faɗa kamar yanda ta saba idan taga tana share yaron. Shiru dai tai batace komaiba kamar kullum, sai hawayen data share a ɓoye duk da ita Maman Sadiq na lure da ita.
Ganin komai normal ta samu lafiya Alhmdllh washe gari aka basu sallama. tare da basu ranakun da zasu dawo domin duba lafiyarta. Daɗi sosai Zinneerah taji da wannan sallama. dama ba ƙaramin gundura tayi da zaman asibitinba.
Koda suka dawo gida sun sami ƙyaƙyƙyawar tarba daga yaran gidan, dan harda ƴaƴan Maman Halima na ma'auri duk sunzo gidan tarbarsu, dama duk sai da sukaje asibiti anan nema Zinneerah ta fara saninsu. Amma yanda suka karɓeta saika ɗauka a cikinsu ta tashi itama.
Yau ɗinma tararwa sukai sun haɗa wata ƴar ƙwarya-ƙwaryar liyafa iya su kawai ƴan cikin gidan, sai ƴaƴan Naziru da matarsa da maƙwafta na kusa da ake gaiswar mutunci. Kowa yayi mamaki dan babu wanda yasan da wannan shirin nasu. Maman Sadiq zata hana Alhaji ya hanata akan kartace komai, dan sudai basusan komaiba akan wannan haihuwa ba. Sannan kosu ɗin da suka sani ai Zinneerah batasan sun saniba. Su daure su ƙarfafa farincikinta har lokacin da za'aje gaɓar da tuhumarta zatai musu amfani, kuma dalilin hanyar samuwar ɗan bazaisa su toshe hanyoyin karɓar ƙaddarar da yazo a cikintaba, da har zasu ƙi farinciki ko nuna godiyarsu ga ALLAH.
Badan tasoba ta haƙura ta zuba idanu itama.
Ita dai Zinneerah bata nuna wani alamun damuwa da hakanba, dan tunda suka shigo gidan Maman Halima tai mata gashi na musamman a jikinta sai ta samu nutsuwa sosai, aka kawo mata abinci kuma taci ta ƙoshi tasha magani sai barci. Sai gashi har suka gama walinarsu ita bama tasan wace waina suke toyawaba, sai bayan ta tashine su Aunty Halima suka shigo sukai mata sallama zasy wuce gida dan lokacin anyi sallar isha'i.
Yanda suke nuna mata so da ƙauna su da mahaifiyarsu yasa itama take sakin jiki dasu sosai, kuma tanajinsu tamkar yayunta, dansun maye mata gurbin su Yaya Gajejen ta.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 13*
________________________
*_Hummmmm!!. Wai wai wai, wani aiki sai: GIDAN ƘAMSHI💃🏻💃🏻💃🏻🥺_*
*_INA MATA ƳAN ƘWALISA MA'ABOTA SON ƘAMSHIN GIDA DANA JIKI?_*
*_INA MATAN DAKAN SO DUK INDA SUKA DOSA KO SUKA BARI SAI SUN BAR MUSU TARIHIN ƘAMSHINSU_*
*_TO MATAN ƘWARAI KUZO GA WANI SIRRI DAZAN BAKU DAGA FITACCEN GIDAN ƘAMSHIN NAN DA BAIDA NA BIYU A KANON DABO😁_*
_Ina magana ne akan GIDAN ƘAMSHI da ke a Jihar KANON DABO MAIDUGURI ROAD MARIRI_.
*MUNA SIYAR DA TURARURRUKAN WUTA SET NA AMARE, MUNA KUMA BADA SARI.*
*AKWAI KUMA SABULUN GYARAN JIKI MAIDA TSOHUWA YARINYA, BUDURWA TAURARUWA, MATAN ƘWARAI ANNURIN HASKAKA GIDA. SHIMA DAI AKAN SARI, DOZIN KO KATON*
*AKWAI KUMA ZUMAR ƘARA ƘIBA GA MATAN DA KESON SU GANSU DUMURMUR SUNA JUYAMA OGA KAYAN...😉🙈💃🏻 kundai gane*.
*_Mata ku garzaya GIDAN ƘAMSHI domin ƙamsasa kanku kuma kar aci kasuwar sama babu ku😁_*
*ZAKU IYA SAMUN MU TA WANNAN LAMBAR WAYAR: 07033778564 DOMIN JIN ƘARIN BAYANI*.
*KO A KANO MAIDUGIRI ROAD MARIRI*.💃🏻💃🏻👍🏻
_______________________
*Page 13*
............A zahiri dai Zinneerah ce ta haifi Abdul-Mutallaf. Amma dukkanin abinda ya shafi yaron ƙiri da muzu ta sakarma Maman Sadiq. Musamman daya kasance ba abincinsa yake sha ba yanzu sai madara. Idan ka gansa a hannunta ko tana masa wata hidima to Mama Sadiq na wajen Abba ne ko tana aiki, yaran kuma basa gida.
Wanda bai saniba ma idan yazo gidan saiya ɗauka Maman Sadiq ɗince ta haifi yaron. Tsabar ƙwarewa a shahara wani lokacin idan tace Zinneerah tai masa wani abu tata kumbura baki kenan. Ita maman Sadiq ma abin har dariya yake bata.
Itako Zinneerah ba komai ke ɗawainiya da itaba sai tsabar shirme da ƙuruciya, sannan har cikin ranta ta rigada ta saka cewar yaron ɗan aljanune suka ajiye mata. Bawai bata sonsa bane, sosai take son abinta kasancewarta mai son yara dama can, dan a hankanma wani lokacin haka zata zauna taita satar kallonsa, idan kuma Mama ta fita a ɗakin takan ɗaukesa kota zauna tana kallonsa tana murmushi da shafar kansa, kai har kiss idan ALLAH ya cidashi yimasa akeyi ko rawa.
A yau kusan shine ma ya tadasu da asubahi da kukansa, dan a daren jiya tsautsayi ya saka Maman Sadiq tsare Zinneerah ta shayar dashi akan ko za'a dace yanzun tunda tana shan maganin. Sai gashi a cikin rashin dacewar cikin yaron ya kumbura kamar yanda ya ringayi a asibiti. Abba daya dawo daga masallaci ya shigo yana faɗin, “Yaya dai wai nikam?. Mi akaima abokina ne yau a gidan nan?”.
Maman Sadiq dake bashi maganin da aka dinga bashi sanda suna asibiti idan hakan ta faru ta ɗago tana dubansa. “Wlhy Yaya tsautsayi yasa na sakata ta shayar da shi jiya da daddare dan tausayi yake bani, ace jinjiri kamar wannan babu abincinsa sai madarar banzar nan. Tofa shine kaga cikin dai ya kumbura kamar yanda yakeyi”.
Amsarsa yayi a hannunta bayan ta goge masa maganin daya ɗan ɗisa masa a wuya. Ya sakashi a kafaɗa yana hura masa kunne da shafar bayansa. sassauta kukan ya farayi kaɗan-kaɗan, kafin ya koma ajiyar zuciya. Kusan mintuna biyar suna a haka yaron ya saki gyatsa mai ƙarfi. Su dukansu sai da suka sauke numfashi. Su Sadiq dake zaune duk cikin damuwa Abdul yace, “Abba Little yaji sauƙi (dan haka suke kiransa saboda Abdul ɗin).
Fuskar Abba da murmushi yace, “Insha ALLAH yaji sauƙi gashi yayi gyatsa. Da alama kuma barci ma zaiyi, sai a goyashi”. Ya ƙare maganar da kallon Maman Sadiq.
Miƙewa tai tana faɗin, “Tazo ta goyashi ɗakinka zanje na gyara, dan sakarci duk wannan ihun da yaron nan keyi tana ciki tana jinmu amma ko leƙe, tun a ɗakinma luf tayi ita a dole barci take bata jimuba”.
Dariya kawai Abba yayi batare da yace komaiba. Maman Sadiq kuma ta shiga kwalama Zinneerah da duk tana jiyosu daga ɗakin kira. Fitowa tai sum-sum-sum kamar wata munafuka. Abba yace, “Koma ki ɗakko zani kizo ki goyashi akwai sanyin safiya”.
Cike da kunya ta juya ta koma. babu jimawa ta dawo da zanin goyon a hannu. Maman Sadiq ce ta amshesa ta saka mata a baya dan har yanzu ba wani iya goyon tayi da ƙyauba. Kusanma wannan shine karo na uku kacal da zata goyashi. Dan mafi yawancin lokuta su ƴan biyune ke goyashi ko Maman Halima ko ita Maman Sadiq ɗin. Har Sadiq da Abdull goyamusu akeyi, ƴaƴan maman sakina ma sukan faki ido suzo su ɗaukesa saboda kusan shine ɗan ƙaramin yaro yanzu a gidan, sai yazan abin sha'awa ga kowa banda maman sakina da ko sau ɗaya bata taɓa ɗaukarsaba ma ita.
Da ƙyar Maman Sadiq ta samu goyon yayi dai-dai tanata ma Zinneerah ɗin faɗa. Ita dai batace komaiba sai dariya takema a ranta wai mama ta dage da masifa akan ɗan aljanu, sai randa sukazo suka ɗauke abinsu taga yanda kowa zaiyi a gidan ai.
Bayan fitar Abba da Maman Sadiq Zinneerah ta hau gyaran ɓangaren nasu kamar yanda ta saba, Sadiq kuma suka shige suna shirin makaranta dan an koma hutu.
★★★★
Haka rainon Little Abdull ya cigaba da gudana kusan kaso biyu a hannun Maman Sadiq da maman Halima ne. Kaso ɗaya kuwa Zinneerah na rabawa dasu Sadiq. A haka sukai arba'in yaron yay ɓulɓul masha ALLAH, ga ƙyawunsa na sake fitowa. Yaro gaba ɗaya bai ɗakko kamannin Zinneerah ba ta fuska sai halittar yatsunsa na ƙafa da hannu da abinda ba'a rasaba. Amma daga basuba kamanninsa daban da nata. Takan zauna ta dinga kallonsa da shiga dogon nazarin ko zata iya gano da wanda yake kamar. Amma sam bata iya hasaso komai ga kamannin nasa.
Sosai jikinta ya warke, idanma baka saniba bazaka taɓa ɗauka cs akai mataba. Musamman da yazam bayan dawowarsu gida maman Sadiq da Maman Halima kulawa da gyara na musamman suke mata wanda ita bawani gane inda suka dosa take ba. Abinda kawai ta sani tanajin daɗin jikinta sosai balle yanzu barci take sosai tamkar kasa. Ga lafiyayyen abinci da take samu kuma ga kwanciyar hankali. Sam bata wani tunawa da Inna. Garama Babanta da Yaya Sa'a da Yaya Gajeje. Takanyi kuka a duk sanda sukazo mata ranta koda a boyene. Sai ko Khalipha da har yanzu yake maƙale a zuciyarta. Gashi yanzu Naziru ko gidan yazo baya mata maganarsa ma. Itako kunya ta hanata sake tambayarsa ko yanzu yana samunsa.
Bayan tayi arba'in da kusan wata ɗaya Maman Sadiq taga zaman nata baida wani amfani. sai dai taci ta ɗanyi aikin gida ta kwanta barci. Samun Abba tai da shawara akan Zinneerah ɗin ta shiga wata islamiyya dake anan kusa da su ta ƴanmata, inda su Sakina ke zuwa da yamma. To sunayi da safe kuma zuwa ƙarfe ɗaya ga yaran da basa zuwa boko.
“Eh shawaranki mai ƙyau ce Hauwa'u, nima kuma maganar fara karatunta dama yana raina. Na bartane kawai Abdul-Mutallaf ɗin ya ƙara ƙwari sannan. To amma tunda dai naga bama itace ke rainonsa ba gara ta fara islamiyyar kawai itama bokon sai a nema mata inda zai dace da ita dan nasan da wuya ace acan tayi karatunma”.
Cikin gamsuwa da bayaninsa Maman Sadiq tace, “ALLAH ya saka da alkairi yaya, sai dai duk da bamu taɓa maganar karatu da itaba sai naga kamar taɗanyi acan, dan naga wasu lokutan idan su Abdull na Assignment haka takan saka musu baki harma tayi gyara a wani wajen”.
“A'a ikon ALLAH, to kinga kiramin ita dai muji ta bakinta, kinga ai sai mu sami madafar kamawa ko”.
Miƙewa tai tana amasa masa da to. Babu jimawa kuwa sai gasu sun dawo tare da Zinneerah. Bayan ta gaida Abba sai yake tambayarta ajinta nawa a makaranta?.
Duk da a bazata tambayar tazo mata sai gashi ta saki murmushin da ya basu mamaki. Kanta tsaye cike da zumuɗi tace, “Abba nayi jsce ma ai”.
“Ikon ALLAH, to to Alhmdllh. Ashe ɗiyar tawama ƴar boko ce bamu da labari. Amma gaskiya naji daɗin hakan sosai, kuma na yaba ƙoƙarin babanki anan....”
Cikin suɓutar baki tace, “Lah Abba ai bama shine ya sakaniba. Inagama Baba fa baisan ina zuwa makarantaba, dan shifa babu ruwansa dani a gidan. Ni saima nayi kwana hudu biyar ban gansaba wani lokacin”.
Duk idanu suka zuba mata, a ransu kuma cike suke da zumudi da jin daɗin yanda ta fara sakin jiki da faɗa musu abinda ke ranta.
Maman Sadiq ce tace, “To wani guri yake zuwa da har kike kwanaki baki gansaba?”.
“A'a mama, yana nan a gidan, kawai dai bansan miyasaba shi bayason ganina ne wani lokacin, wani lokacin kuma daga sallar asuba idan ya fita bai dawowa sai munyi barci”.
Babu wanda ya iya magana tsakanin Maman Sadiq da Alhaji. Maman Sadiq dai rayawa take a ranta yaushe al'amarin baban ya taɓarɓare haka kuma?. Dan tasanshi a da mutumne tsayayye akan iyalansa da gidansa. Dan ko talla wannan bai yarda yaronsa ya fita ba. Duk inda akai sallar isha'i kuwa yana gidansa, bazai sake fitaba sai asuba. Da an idar da salla zai dawo gida ya karya sai rana ta haska zai fita kasuwa wajen sana'ar sai da dankalinsa ɗanye da makani.......
Tambayar da Alhaji ya jefama zinneerah ce ta katse tunanin Maman Sadiq ɗin ta maida hankalinta garesu.
“Karki damu yarinyata, haka rayuwa take kullum cikin tsere-tsere da jarabawa. To amma wanene ya kaiki makarantar?”.
Kunyar wanda zata ambata ɗin ya sakata jan lokaci kafin ta bashi amsa. “Abba Babawo ne ya kaini kafin ya koma yace Yaya Karima yake so”.
Duk da a dunƙule tai maganar kasancewarsu manya masu hangen nesa sai duk suka gano inda ta dosa kai tsaye.
“ALLAH ya saka masa da alkairi”.
Abba ya faɗa dajin daɗi. Amin sukace ita da maman Sadiq. Daga haka Abba ya sallameta suka cigaba da tattaunawa shi da matarsa.
“Hauwa'u kinga fa'idar shiru da mukai mata akan son sanin bayanta ko? Ina mai tabbatar miki inhar zamu cigaba da binta a haka harma abinda bamuyi zatoba sai munji daga gareta wataran. Kinsan shi yaro tamkar dabba yake, mai kula dashi da mai sake masa shi yake sakewa da shi shima. Dan haka ki sake nutsuwa wajen fahimtarta a hankaki komai da muke buƙata zai fito. Domin a fahimtar danai mata rashin samun sake a inda ta baro ya sakata kasancewa shiru-shiru kamar mara wayo. Amma ras take kuma tanada kwaramniya, sai a hankali zakiga ta hau