Showing 18001 words to 21000 words out of 223329 words

Chapter 7 - Makauniyar Kaddara Hausa Novel Complete

21 Nov 2024

1161

kashe kanta ta ayyana yi amma wani ɓangare na zuciyarta ya ƙwaɓe akan wannan ba mafita bace.
      Tunda mashinansu suka shigo garin idanu caa a kansu. A take ƙananun magana suka fara tashi akan wai ankai Zinneerah kusada ne an zubar da ciki. Su dai basu san sunayi bama. Wani matsanancin tsoro ne ya shiga zuciyar Zinneerah ganin sun iso gida. da ga ita sai Gwaggo Laritu suka iya shiga gidan. Su kawu juyawa nasu gidajen sukai abinsu dan basusan yanda zasu tunkari yayansu da wannan magana ba. Gashi likita yace abar Zinneerah ta huta na kwana biyu kamar yanda jikinta ke buƙata.
     Mata ne cike da gidan danƙam anata arerewa da guɗa. Dan masu kiɗan ƙwarya Inna ta kira suke wasa a gidan wai yau take nata yinin bikin. Da farko har suka shigo gidan sukama kusa kaiwa ɗakin kwanan su Zinneerah babu wanda ya kula da su. Suna gab da shigewarne Inna ta hango Zinneerah. A tsawace tace, “K! K! K! Dakata mani. Masu kiɗa ku saurara kaɗan ina zuwa”.
      Kamar wadda tai busa da sarewa a kunnuwan jama'a a take gidan yay tsit, hankalin kowa ya dawo kan Zinneerah da Yaya Gajeje yasata saurin nufosu itama. Kusan a tare suka iso gaban Zinneerah ɗin, inna ta kalla Gwaggo Laritu datai kamar batajiba tana neman shigewa ɗakin su Zinneerah ɗin.
         “Lallai ko ba'a faɗaba yanayin da kuka shigo mani gida kawai ya tabbatar da zancen ciki......”
      Da sauri Gajeje ta katseta da faɗin, “Haba Inna wacce irin maganace haka? Wannan ai zancene na cikin gida ko”.
     Harara Inna ta watsama Gajeje, ta kai hannu ta finciko hannun Zinneerah da kanta ke a ƙasa hawaye masu zafi na ziraro mata a saman kumatu. Hannu tasa ta yaye hijjab ɗin jikinta ta jefar. Ta kama rigarta zata cire Gwaggo Laritu ta riƙeta a fusace. “Wlhy! Wlhy wlhy kinji na rantse sau uku, inhar kika hiddama yarinyar nan riga yau saina nuna miki ni jinin gidan baduku ce Asabe. Wai kina tunanin ana tsoronkine ko me? Mi yarinyarnan ta tsare maki a gidan nan ne wai shin? Idan ma cikkinne da gaske a jikinta ai kece silarsa. Dan kece kika hana mata rayuwa zaman lahiya kamar yanda kika hana ubanta. Ya auro mahaifiyarta dan yaji sauƙi kika shiga kika hita sai da kikaga tabar gidan saboda son zuciyarki. Wama yasani yanzunma ko kece kika biya aka lalatama yarinya rayuwa, dan wlhy duk abinda akace kinyi Asabe nasan zaki iya mahiyinsa saboda son duniyarki”.
      Tofa babbar magana. Waɗan nan zantuka na Gwaggo Laritu a take ya hargitse gidan, kafin kace mi taron biki ya zama taron faɗa da bala'i. Tun anayi a cikin gida har aka koma ƙofar gida, abu kamar wasa sai ga ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai faɗa ya juye tsakanin dangin Baba dana Inna. Yayinda jama'ar gari suka rabu gida biyu, wasu na goyon bayan Inna wasu na goyen bayan dangin Baba da Zinneerah. Abu yay tsamari har magriba babu alamar zasu sarara, daga ƙarshe dai sai da zance ya kaisu ga gidan mai-gari daya aiko aka tattaresu zuwa can.
         Sosai zancen ciki a jikin Zinneerah ya tayarma mai-gari hankali. dan har ransa yakejin ƙaunar yarinyar da tausayinta. Tun a randa sukazo shari'arnan shi kaɗai yasan abinda ke ransa game da Zinneerah. Dan ya ɗaukama kansa alƙawarin zai tsaya mata tai karatu, kuma ɗansa dake karatu yanzu haka a Katsina shi yake burin zama mijinta. Sai kuma gashi yau wannan magana maiban tashin hankali ta ɓullo rana tsaka.
     A yau ma tambayar duniya anma Zinneerah akan wanene mai ciki tace ita bata taɓa aikata iskanciba, dan haka batasan ina ta samo ciki ba. Lallai wannan al'amari ya kai a kirasa MAKAUNIYAR ƘADDARA, ita da ciki ke jikinta batasan yanda samuwarsa ta wanzuba, su kuma dake tuhumarta ina zasu kama?.
      Ganin dare yana neman rufawa mai-gari yace suje gida gobe idan ALLAH ya kaimu zai nemesu, dan wannan magana babbar maganace dolene sai sunje ga hakimin kusada ko a samo bakin zaren a can. Wannan magana ta tadama Inna da Zinneerah hankali matuƙa. Ita Inna tsoronta ALLAH tsoronta a gano gaskiyar da sa hannunta Zinneerah ta tafi Katsina. Saukinta ma Hajji Lanti bata dawo garinba ai tun tafiyar da tai dasu Zinneerah ɗin. To amma tasan akaje gaban hakimi ai ca za'ai sai wajen ƴan doka (Police) da ga haka kuma sai wajen alƙali. Lallai tsugunne bata ƙare ba kenan, ba burinta kenanba, babban burinta kawai Zinneerah tabar mata garin baki ɗaya dan bata ƙaunar ganinta a cikinsu kamar yanda ta tsani mahaifiyarta sanda tana tare da su.
       Sanin halin inna yasa Gwaggo Laritu tafiya da Zinneerah gidanta, bayan ta saka Sa'a ta tattaro mata duk kayan Zinneerah dake a can gidansu dan dolene ta dawo zama a gidajen ɗaya daga cikinsu har ALLAH ya sauketa lafiya.

          Tunda suka shigo gidan sam hankalin Zinneerah baya a jikinta. A hankali wani irin tsanar garin Danya da komai nasa ke shiga jikinta. Koda Sa'a ta kawo mata kayanta tana zaune can rakuɓe kanta cikin ƙafafu, ba kuka takeba ba kuma tunani ba. baƙon al'amarin dake shiga cikin jikinta ne kawai ke ratsata. Ta ɗago ta kalli Sa'a data dafa ta, ganin yanda Sa'a ke hawaye ya sata sakin wani murmushi maiban mamaki, batare da tace komaiba ta maida kanta yanda yake.
        Hankalin Sa'a ne ya ƙara tashi, dan a duk sanda taga irin wannan murmushin a fuskar Zinneerah to takai ƙololuwa a shiga tashin hankalin rayuwa kenan. Dan duk lokacin da takurawa da matsawar Inna yaymata yawa bata kuka. Ko nuna tausayinta sukai kuma sai dai tai musu wannan murmushin bazata taɓa ta tanka ba.
          Zuciyar Gwaggo Laritu a kusa take ainun da baƙin cikin halin da suke ganin Zinneerahn ta jefa kanta. Da kuma haushin Inna dana Baba da ya koma tamkar mara amfani agaresu, yanzu haka a kaf ruguntsumin nan da akeyi yaƙi cewa ƙala. Wanan takaicin da sukai mata yawane ya sata shigewa ɗaki tabar Zinneerah waje zaune batare da tace taje ta kwanta ba. Sauƙinta ma itama su kaɗaine a gidan sai matan ƴaƴanta biyu, suma kuma an katangema kowa sashensa babu mai ganin wani.
       Abinka da ƙauye ahankali garin ya fara ɗaukar shiru. Har takai Zinneerah dake zaune a ƙofar ɗakin Gwaggo Laritu barci ɓarawo ya saceta har takai ga zamewa ƙasa ta kwanta akan sumintin wajen tai filo da jikkar kayanta da Sa'a ta kawo da yake ba wata babba bace, dan kayan nata basu wuce a ƙirga ba.
        Barci ne sosai mai nauyi yay gaba da ita, yayinda itama acan Gwaggo Laritu datai tunanin idan Zinneerah ta gaji da zaman wajen zata shigo ɗaki ta kwanta barcin yay gaba da ita dan gajiya.

         Tamkar wadda akace ta tashi Zinneerah ta miƙe zumbur, babu wani tunani ta ɗauki jikkar kayanta ta nufi hanyar ƙofar gidan nasu Gwaggo Laritu. A hankali ta zare sakatar murfin gidan ta fice kamar tana tsoron wani ya jita koya ganta. Kallon gabas da yamma kudu da arewa tayi, garin tsit babu alamar akwai wani rai mai numfashi, ga wata yayi nisa babu wani hasken kirki, ga sanyi kasancewar lokacinsane sai dai farko-farko dan baiyi ƙarfi ba. Ta sauke wani nannauyar ajiyar zuciya ta fara tafiya babu alamar tsoro ko fargabar jin garin shiru tattare da ita sam.
           A cikin daren nan Zinneerah ta nausa kanta cikin daji batare da alamun akwai hankali a jikintaba, dan yanda take matsoraciya ko fitsari ya kamata da dare sai ta tada Yaya Sa'a ta rakata. Amma yau sai gata a hanyar daji cikin tsakkiyar dare babu ko gezau.............✍


Hasbinallahu wani'imal wakil. Ya rabbu ka iya mana da abinda yafi ƙarfinmu, harma da wanda mukafi ƙarfinsa.😭🙏🏻



       *_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*

Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.

*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_

*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_

*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_

*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_

*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_

Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.

Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  0903 234 5899

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
https://youtu.be/NgqdCTVKOF8

Channel name Abdul-rahmaan.

He's a very young boy who's passionate about becoming one among the huffaz, he loves reciting the Holy Qur'an even at his younger age. He has memorized so many surahs within juz ammah.

please help him grow his channel fisabilillah and also pray for him to be come a Hafiz in future in sha Allah. Jazakumullah khair

________________________

*_TYPING📲_*


*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*


*Page 7*

...........Tafiya take batare da tasan ina take dosaba. Gashi babu alamar gajiyawa tattare da ita, duk da mai kallo a kallo ɗaya zai iya fahimtar lallai tana tare da gajiyar, amma ita kasancewar bata cikin hayyacinta bata saniba. Babban burinta kawai tai nesa da garin Danya baki ɗayansa. Bata damu da yunwa da ƙishirwar dake damunta ba, balle ta tuna bayan ita akwai wata halitta a jikinta dake buƙata idan ita bata buƙata.
            Kusan dai-dai ketowar alfijir ta iso bakin titin da batasan kona wane gari bane. Batai kuma tunanin son ta sani ɗinba ta zube a ƙofar wani shago ta kwanta cike da gushewar hankali dana tunani. Wani irin nannauyan barcine ya ƙwasheta kuwa, kafin wani dogon lokaci ta fara sauke numfashi......

★★★★

         Tsabar gajiyar da suka kwasone a yinin yau ya saka Gwaggo Laritu barci mai nauyi sosai, har takai da sai da babban ɗanta ya leƙo sashen domin tada ita da asuba. Dan da kullum itace mai tashinsu, amma sai gashi yau sun rigata su. Rashin jin motsinta kuma ya tabbatar masa da makara tayi kenan.
       Tashi tai da ƙyar tana mamakin barcin da tai haka mai nauyi. ga ƙofartata buɗe alamar Zinneerah bata rufe musu ba. Kallon saman gado tayi inda ta bar mata ta kwanta dan ita dama bata iya kwanciya a gado sai ƙasa. Ganin babu kowa a gadon tai tunanin ko Zinneerah bayi ta shiga ita ta tashi ne.
     Bata damuba ta fito gabatar da alwala. Saboda tunanin Zinneerah na bayin ya sata zuwa can wajen dabbobinsu tayo fitsari tazo tai alwala kar makarar tai yawa. Hankalin Gwaggo Laritu bai sake tashi ba sai da taga harta idar da salla gari yay ɗan shaaaa babu motsin Zinneerah. Ajiye carbin da take ja tayi ta fito tsakar gidan. Ganin babu alamarta ya sata nufar ƙofar bayi tai gyaran murya. Shiru. ta sakeyi, nanma shiru. Sai kawai ta danna kai. Gabanta ya faɗi ganin babu alamar anyi amfani da bayin ma. A rikice ta fito, hakan yay dai-dai da dawowar Awwal babban ɗanta daga masallaci, shi Safiyanu yana Lagos neman kuɗi.
      “Mama lafiya kuwa? Mi kike nema?.”
       A rikice tace, “Zinneerah wannan yaron (bata faɗar sunansa saboda ɗan fari). Ban gantaba”.
      Da mamaki shima yace, “Dama anan ta kwana? Ko zuwa tai yanzu da sahe?”.
        “Anan ta kwana mana. tare da ita muka taho nan saboda gidan nasu kasan akwai mutane bazai yuwu zama gareta ba ai ko?”.
      “Hakane Mama”. Ya faɗa yana cigaba da lalleƙa ko'ina na sashen nata. Har takaisa ga fita nasu sasssan. Har sashen ƙaninsa Safiyanu ya tambayi matar tace bataga Zinneerah ba itakam. Bama tasan anan ta kwanaba, dan sanda su Gwaggo Laritu suka dawo gidan tayi barci kasancewar tanada tsohon ciki dama.
     Wani tunani ne yazoma Awwal a rai, dan idan bai mantaba dazai fita salla a buɗe yaba ƙofar zaure. Ya dawo sashen Gwaggo yana faɗin, “Lallai Mama akwai matsala. ALLAH yasa yarinyar-nan ba guduwa tai ba, dan wlhy a buɗe naga ƙofar soro yau, kuma na tabbatar bazaki kwanta baki rihe ba”.
        “Hazbunallah! Wlhy na rihe wannan yaron, ni kuma takaici da damuwar da suka haɗu sukaimin yawa ya sani shigewa na barta anan zaune akan idan ta gaji da zaman zata shigo ɗaki ta kwanta. Aiko zama bai ganniba bara muga ko tana gidan nasu”.
       “A'a mama yi zamanki ni bara inje”.
      “Kai dai barsa naje. Ai ba fasa zancen za'aiba cikin hikina za'a dubata. Dan dama dole naje gidan saboda aiki tunda yau ne ɗaurin auren Karima ”.
      Badan hakan ya masaba ya haƙura. Dan har ransa yana son Zinneerah da tausayinta matsayinsa na ɗan-uwanta.

       Koda Inna taje gidan bata shigaba. Dan dama batazo danta shiga ɗinba. Tayi alƙawarin har agama wannan bikin bazata leƙa gidanba. Sunbar Inna da ƴaƴanta kamar yanda tafi buƙata. Yaro ta samu ta aika ya kira mata Sa'a anan maƙauftansu da yace sun kwana ita da su Karima.. Babu jimawa kuwa sai gata ta fito tana mutstsukar ido alamar yanzu ta tashi. Ko gaisuwarta Gwaggo Laritu bata tsaya amsawaba tace, “Sa'a shiga gidan nan naku cikin hikima ki dubamin Zinneerah ”.
        “Gwaggo Zinni kuma? Ba'a gidanki ta kwanaba dama?”.
      “Nidai ba surutu na tambayeki ba, jeki fara dubawa”.
      Kai Sa'a ta kaɗa tana nufar cikin gidan da ƴar hayaniyar waɗanda suka tashi ta fara kaurewa. Babu wanda ta tambaya ta shiga neman Zinneerah a gidan. Sai dai babu mai ko alamarta. A rikice ta dawo ta sanarma Gwaggo Laritu. Itama sai ta sake ruɗewa......

★★★★

         A ɓangaren Zinneerah kuwa barci tasha sosai a ƙofar wannan shago har fitowar rana. Sai da mai shagon ya fitone ya tadata domin buɗewa. Tashi tai kawai ta matsa gefe batare data tanka masa ba. Shima ɗin bai tanka ba dan kallon mahaukaciya kawai yake mata duk da babu alamar datti a jikinta. Saɓanin kwanciyar yanzu kam zama tai tana kallon motsin mutane dana wucewar motoci. Babu abinda take fahimta dan ƙwalwarta ba aiki take irin na mutane ba. Ga yunwa mai tsanani na cinta. Dan haka ta ƙurama mutane dake a runfar mai-shayi dake acan tsallaken titi idanu sunasha suna kwasar hira da dariya da gaddamar siyasa. A hirar tasunema takejin sunan garin da take a yanzu mai suna Tsanyawa.
       Mai shagon ne ya lura hankalinta na ga masu shan shayi, haka kawai yaji tausayinta, dan haka ya fito zuwa tsallaken ya siyo mata shayin da biredi harda indomie.
       Wajenta ya dawo yana murmushi, “Baiwar ALLAH kina son kici ko?”. Ya faɗa yana kallonta. Batace komaiba tai ƙasa da kanta kawai tana wasa da yatsun hannunta. Murmushi ya sakeyi shima ya ajiye mata filet ɗin indomie ɗin da kofin shayin da aka ɗora biredi a sama. “Gashi to kici”. Kanta ta rausaya masa kawai taja filet ɗin nanma batai magana ba. Batai ko tunani wanke hannu ba balle yin sallar asuba. Tasa hannu ta hau cin abincin a nutse kamar yanda nutsuwa ta kasance jinin jikinta dama can. Citai ta ƙoshi tai gyatsa. Batare da wanke hannunba ma a yanzu ta zame ta sake kwanciya sai barci.
       Sosai tausayinta ya sake cika zuciyar mai-shagon nan. Yazo ya kwashe kayan data gama cin abincin batare da yayi magana ba.

       Yanzu ma barci sosai Zinneerah tasha a wajen, dan bata farkaba sai gabanin la'asar. Zama tai tana kallon mutanen garin daketa faman kaiwa da komawa, dan wajen ya sake cika fiye da ɗazu da safe. Ga titin motoci nata kai kawo suma. Mai-shagon nan ne dai ya fito salar la'asar ya ganta zaune ta tashi. Cike da tausayinta yace, “Baiwar ALLAH kin tashi ashe?”.
     Bata tanka masaba yanzu ma. Tadai ɗago kai tai masa kallo guda ta maida kanta ƙasa. Yanzuma kamar ɗazun murmushi yayi, ya nufi inda masu abinci suke ya siya mata yazo ya bata. Kamar ɗazu bata tankaba bakuma ta wanke hannu ba tahau ci, tare da ɗaukar ledan ruwan ta fasa tasha ta ƙoshi tana lumshe idanu. Tamkar ɗazun sai ta sake zamewa a wajen ta kwanta sai barci.
     Mai shagon ya dawo sallar la'asar ya ganta ta koma barci, mamaki ya kamashi sosai ganin barci bai mata wahala. Yama fahimci yunwarce ke tadata kenan. Barcin kuma shine salon nata lalurar.
     Har lokacin tashinsa yayi kusan ƙarfe takwas na dare bata tashiba. Ya sai abinci ya ajiye mata bayan ya rufe shagon ya wuce gida.
         Zinneerah bata farka ba sai kusan sha biyun dare. Yanda ta tashi tana riƙe ciki da matse fuska zai baka tabbacin yunwace. Idonta na sauka akan roba rufe da leda tai saurin jawowa kuwa. Ganin abinci jikinta har rawa yake ta hau ci. Sai da ta cinye tas tasha ruwa sannan ta miƙe tamkar an tsikareta. Jakkar kayanta ta ɗauka ta fara tafiya tamkar daren jiya dan jitai gaba ɗaya nanma ta tsanesa. Burinta kawai ta ƙara gaba tai nesa da garin na Tsanyawa.
        Tafiya take cikin gushewar hankali da tunani tamkar daren jiya. Gashi abin tashin hankalin yau a kan titi ne. Sauƙinma darene babu yawan mitoci sai jefi-jefi. Haka dai ta cigaba da nausa kanta cikin kariyar UBANGIJI a wannan dare ma.....

★★★

           Hankalin kowa ya tashi na rashin ganin Zinneerah ɗin, dan Gwaggo Laritu kasa haƙurin ɓoye rashin ganin nata tai sai da ta fasa. A take aka shiga nemanta lungu da saƙo na garin, sai dai ganin har wani daren ya sake rufawa kowa ya fahimci dai da gaske Zinneerah ta sake guduwa kamar yanda Inna ke faɗi cike da gadarar tabbatarwa tana dariya kuma.
        Kuma duk da tashin hankalin rashin ganin Zinneerah ɗin a haka aka ɗaura auren Babawo da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login